Aminiya:
2025-06-18@13:25:04 GMT

Ma’aikatan Kwalejin Ilimi ta jihar Kaduna za su tsunduma yajin aiki

Published: 18th, June 2025 GMT

Kungiyoyin ma’aikata na Kwalejin Ilimi ta jihar Kaduna da ke Gidan Waya, Kafanchan sun bayyana aniyarsu na fara yajin aikin gargadi na kwanaki uku.

Sun ce za su shiga yajin aikin ne daga ranar Alhamis, 19 ga watan Yuni, 2025.

Wannan matakin ya biyo bayan karewar wa’adin kwanaki 14 da suka yi bai wa gwamnatin jihar, wanda zai kare ranar Laraba, 18 ga watan Yuni.

Majalisa ta aike wa Tinubu kudurorin dokar haraji domin ya rattaba musu hannu Ambaliyar Mokwa: Har yanzu muna neman mutum 700 – Gwamnatin Neja

Aminiya ta rawaito cewa kungiyoyin da suka hada da na Kungiyar Malaman Kwalejojin Ilimi (COEASU), SSUCOEN da Kungiyar Manyan Ma’aikatan Kwalejojin Ilimi ta Najeriya (SSUCOEN) da Kungiyar Ma’aikatan da ba na Koyarwa ba (NASU), na bukatar daukar matakin gaggawa kan batutuwan walwalar ma’aikata da suka ce gwamnati ta yi sakaci da su duk da alkawuran da ta riga ta daukar musu.

Sanarwar ta fito ne daga wani taron manema labarai da Shugaban Hadaddiyar Majalisar Ma’aikatan, Kwamared Alkali Marajos ya jagoranta.

Daga cikin manyan bukatun da kungiyoyin ke nema akwai aiwatar da tsarin albashi na CONPCASS da CONTISS da kuma gyara dokar ritaya ta shekaru 65 don ta shafi hatta ma’aikatan da ba masu koyarwa ba.

Kungiyoyin sun gargadi cewa rashin cika wadannan bukatu zai tilasta musu fara yajin aikin gargadi daga 19 zuwa 23 ga Yuni, 2025.

Sai dai sun sake jaddada aniyarsu ta ci gaba da tattaunawa tare da bukatar gwamnatin jihar da ta dauki matakin gaggawa domin kaucewa tsaiko ga harkokin karatu a makarantar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Kwalejin Ilimi Yajin aiki

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Ta Cimma Sabuwar Nasarar Bincike Duniyar Wata

Kasar Sin ta cimma nasarar aikin gwajin tserewa lokacin da ake gamu da matsala a matakin farko na harbar kumbo mai dauke da mutane na “Mengzhou” a yau Talata, a cibiyar harbar taurori dan Adam dake birnin Jiuqiu, abin da ya alamanta cewa, Sin ta cimma sabuwar nasara a aikin binciken duniyar wata tare da kumbo mai daukar mutane.

Wannan ita ce nasara irinta ta biyu da Sin ta samu a wannan bangare, bayan shekaru 27 da suka gabata, da samun nasara ta farko a aikin gwajin da ta gudanar a shekarar 1998.

Aikin gwajin tserewar da aka gudanar ya kasance muhimmin mataki na ba da tabbaci ga rayukan ’yan saman jannati, wato idan an gamu da hadari ko matsala ba zato ba tsammani, za a iya samar da jagoranci ga sashen kumbo mai dawowa ya bar wuri ma hadari, tare da dawo da ’yan saman jannati doron duniyarmu lami lafiya.

Kumbo mai daukar mutane na “Mengzhou”, sabuwar na’ura ce da Sin ta kera bisa dogaro da karfin kashin kanta, da zummar gudanar da nazarin sararin samaniya a nan gaba lami lafiya, wanda ke iya tashi zuwa sararin samaniya da dawowa doron kasa, wannan kumbo mai iya daukar mutane 7 na kunshe da fasaha ta sahun gaba a duniya. (Amina Xu)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Ɗaure Wani Mutum Wata 6 Kan Satar Takalma A Masallaci A Kaduna
  • Sin Ta Cimma Sabuwar Nasarar Bincike Duniyar Wata
  • Dortmund ta yi canjaras da Fluminense a Club World Cup
  • Buni ya bai wa manoma 1,000 tallafin aikin gona
  • Amurka na iya kashe jagoran addini na Iran don mun san inda yake — Trump
  • FCCPC Ta Sammaci Air Peace Kan Rashin Maido Da Kuɗin Tikitin Jirgin Da Aka Soke Tafiyarsa
  • KADSEMA da IOM sun fara tantance ɓarnar da ambaliya ta yi a Kaduna
  • Atalanta Na Neman Yuro Miliyan 50 Daga Duk Kungiyar Da Ke Son Daukar Lookman
  • An tallafa wa mata 250 da abinci da kayan sana’a a Kaduna