Ma’aikatan Kwalejin Ilimi ta jihar Kaduna za su tsunduma yajin aiki
Published: 18th, June 2025 GMT
Kungiyoyin ma’aikata na Kwalejin Ilimi ta jihar Kaduna da ke Gidan Waya, Kafanchan sun bayyana aniyarsu na fara yajin aikin gargadi na kwanaki uku.
Sun ce za su shiga yajin aikin ne daga ranar Alhamis, 19 ga watan Yuni, 2025.
Wannan matakin ya biyo bayan karewar wa’adin kwanaki 14 da suka yi bai wa gwamnatin jihar, wanda zai kare ranar Laraba, 18 ga watan Yuni.
Aminiya ta rawaito cewa kungiyoyin da suka hada da na Kungiyar Malaman Kwalejojin Ilimi (COEASU), SSUCOEN da Kungiyar Manyan Ma’aikatan Kwalejojin Ilimi ta Najeriya (SSUCOEN) da Kungiyar Ma’aikatan da ba na Koyarwa ba (NASU), na bukatar daukar matakin gaggawa kan batutuwan walwalar ma’aikata da suka ce gwamnati ta yi sakaci da su duk da alkawuran da ta riga ta daukar musu.
Sanarwar ta fito ne daga wani taron manema labarai da Shugaban Hadaddiyar Majalisar Ma’aikatan, Kwamared Alkali Marajos ya jagoranta.
Daga cikin manyan bukatun da kungiyoyin ke nema akwai aiwatar da tsarin albashi na CONPCASS da CONTISS da kuma gyara dokar ritaya ta shekaru 65 don ta shafi hatta ma’aikatan da ba masu koyarwa ba.
Kungiyoyin sun gargadi cewa rashin cika wadannan bukatu zai tilasta musu fara yajin aikin gargadi daga 19 zuwa 23 ga Yuni, 2025.
Sai dai sun sake jaddada aniyarsu ta ci gaba da tattaunawa tare da bukatar gwamnatin jihar da ta dauki matakin gaggawa domin kaucewa tsaiko ga harkokin karatu a makarantar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Kwalejin Ilimi Yajin aiki
এছাড়াও পড়ুন:
Rahoton Majalisar Dinkin Duniya Ya Yi Gargadi Kan Barazanar Kungiyoyin ‘Yan Ta’adda A Afirka
Majalisar Dinkin Duniya ta yi gargadi game da barazanar kungiyoyin ta’addanci na ISIS da Al-Qaeda a nahiyar Afirka
Wani sabon rahoto da kwararrun Majalisar Dinkin Duniya suka fitar ya yi gargadin karuwar barazanar da kungiyoyin ‘yan ta’adda ke da alaka da ISIS da Al-Qaeda suka yi kan kasashen nahiyar Afirka.
Rahoton ya yi nuni da cewa: Nahiyar Afirka na fuskantar karuwar barazanar ayyukan ta’addanci da ba a taba ganin irinsa ba, yayin da wata gungun jama’a da take karkashin kungiyar al-Qaida ke ci gaba da fadada ikonta a arewacin Mali da Burkina Faso tare da samun ‘yancin kai, gami da samun goyon bayan ayyukan ci gaba da suka hada da jiragen sama marasa matuka ciki da nau’o’in makamai na zamani.
A yankin sahara, kungiyar ISIS ta sake farfado da ayyukanta a kan iyakar Nijar da Najeriya, yayin da kungiyar da ake kira al-Shabaab da take goyon bayan kungiyar al-Qaeda) ke karfafa sojojinta a Somaliya a cikin hadaka mai hadari da wasu ‘yan bindigar kasar Yemen da suka hada da musayar makamai da horar da ‘yan tawaye.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Shugaba Pezeshkiyan Ya Yi Juyayin Shahadar Haniya Bayan Shekara Guda Da Shahada August 2, 2025 MDD: HKI Ta Kashe Falasdinawa 1 Fiye Da 100 A Cikin Kwanaki 2 A Lokacinda Suka Karban Abinci August 2, 2025 Mutanen Kasar Siriya Sun Fito Zanga-Zanga Yin Allawadai Da Kissan Alawiyya A Kasar August 2, 2025 Shugaban Ansarullah: Amurka Tana Da Hannu A Ta’asar Da HKI Take Aikatawa A Gaza August 2, 2025 Kungiyar Wasan Taekwondo Ta Guragu Ta Iran Ta Zama Zakara A Asiya Karo Na 10 A Jere August 2, 2025 Iran ta yi gargadi game da makircin Isra’ila na kawo cikas ga tsaron yankin August 2, 2025 Firayim Ministan Senegal Ya Bayyana Sabon Shirin Farfado Da Tattalin Arzikin Kasar August 2, 2025 Gaza: Witfkoff ya yi rangadi a wuraren da Amurka ta kafa domin tallafi August 2, 2025 ‘Yan Sudan dama na komawa gida bayan gudun hijira na tsawon shekaru a Masar August 2, 2025 Iran Ta Ce Batun Neman Dakatar Da Tace Uranium Zai Rusa Duk Wata Jarjejeniya Da Ake Son Cimmawa August 1, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci