Yau Alhamis, an bude bikin baje kolin kayayyakin kasar Sin da kasashen kudancin Asiya wato CSAE karo na 9, tare da taron cinikayyar kayayyakin shige da fice na Kunming na Sin karo na 29, wanda za a gudanar tsawon kwanaki 6, a cibiyar baje kolin kasa da kasa na tabkin Dianchi na birnin Kunming a lardin Yunnan dake kudu maso yammacin kasar Sin.

Baje kolin CSAE na bana ya kunshi mahalarta daga kasashe da yankuna da kungiyoyin kasa da kasa guda 73, da fiye da kamfanoni 2500 da ke baje kolinsu, kana da halartar dukkan kasashen kudancin Asiya da kudu maso gabashin Asiya.

Baje kolin na wannan karo na ci gaba da amfani da taken “Yin hadin gwiwa da samun ci gaba tare”. Sannan rumfunan nune-nunen guda 16 sun nuna fasahohin masana’antun samar da kayayyaki na zamani, da makamashi mai tsafta, da aikin gona na zamani da dai sauran fannoni wadanda suke samun damar yin hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen kudancin Asiya da na kudu maso gabashin Asiya.

An yi nasarar gudanar da baje kolin CSAE sau 8 a baya, inda sama da kamfanoni 20,000 na gida da na waje suka halarci baje kolin, kuma jimillar kudin kwangilolin da aka daddale ta zarce dalar Amurka biliyan 110.(Safiyah Ma)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Tarayya Da Jamus Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Yuro Miliyan 20 A Ɓangaren Makamashi

“Za a sauƙaƙe hakan ne ta hanyar Bankin Raya kasa na KfW da Asusun Kalubalan Kasuwancin Afirka.”

 

An gudanar da bikin sanya hannun ne a ofishin ministan kasafin kudi da tsare-tsaren tattalin arziki, Abubakar Bagudu, wanda ya wakilci Nijeriya.

 

Sakatare na farko kuma shugaban hadin gwiwar raya kasa a ofishin jakadancin Jamus a Nijeriya, Dr Karin Jansen, da wakilin bankin raya kasa na KfW, Gerald Keuhnemund, duk sun halarci rattaba hannun.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Tarayya Da Jamus Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Yuro Miliyan 20 A Ɓangaren Makamashi
  • Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya
  • Sin Za Ta Samar Da Cibiyar Kasa Da Kasa Ta Gudanar Da Hada-hadar Kudin RMB Na Dijital
  • “Ruhin Sin Da Tsakiyar Asiya” Ya Jagoranci Bude Wani Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Yanki
  • Majalisa ta aike wa Tinubu kudurorin dokar haraji domin ya rattaba musu hannu
  • Sin Ta Fara Aiwatar Da Matakin Soke Haraji Kan Kayayyakin Kasashen Afirka 53
  • Xi Ya Gabatar Da Muhimmin Jawabi A Taron Koli Na Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu
  • Tankokin Isra’ila sun kashe mutum 51 a wurin karbar abinci a Gaza
  • Dalilin Mara Wa Tinubu Baya Ba Tare da Ambaton Shettima Ba – Shugaban APC Na Arewa Maso Gabas