’Yan bindiga sun kashe manoma 24 a Katsina
Published: 19th, June 2025 GMT
’Yan bindiga sun kashe akalla manoma 20 da wasu mutum uku da kuma wani dan sinitiri a jihar Katsina.
An kashe mutanen ne a wasu hare-hare daban-daban da aka kai karamar hukumar Kankara, daya daga cikin yankunan da suka fi fama da kalubalen tsaro a jihar.
A cewar wani mazaunin yankin da bai amince a bayyana sunansa ba, “Kimanin kwanaki shida da suka gabata ’yan bindiga suka kai hari kauyukan Yargoje, Kwakware, Danmarke, Gidan Dawa da kuma Burdugau.
“Sun kashe kusan manoma 20, sun sace wasu sannan suka sace shanun da manoman ke amfani da su wajen huda a gonakin nasu,” in ji shi.
Kazalika, wata majiyar ta shaida wa wakilinmu cewa a ranar Litinin ’yan bindiga sun kai hari kauyen Marmara, shi ma da yake karamar hukumar ta Kankara, inda suka fafata da wasu masu aikin sintiri a yankin da ake kira da C’Watch da wasu ’yan sa-kai, inda suka kashe dan sintirin daya sannan suka jikkata masu aikin sa-kai biyu a kusa da kauyen.
“Sannan sun sami nasarar shiga kauyen Marmara, inda suka kashe mutum uku,” in ji majiyar.
Wakilinmu ya kuma gano cewa a dai daren Litinin din, maharan sun farmaki wasu kauyuka da ke kusa da Kwakware, inda suka sace mutanen da ba a san adadinsu ba.
Wani mazaunin yankin da shi ma bai amince a bayyana sunansa ba ya ce karuwar hare-hare a karamar hukumar a ’yan kwanakin nan ba zai rasa nasaba da yadda wasu kananan hukumomin da ke da makwabtaka da ita suka cimma yarjejeniyar zaman lafiya ba.
“Saboda matukar za a samu yarjejeniyar zaman lafiya a wasu wuraren ba a ko ina ba, akwai yiwuwar su farmaki wuraren da ba su da yarjejeniyar zaman lafiyar,” in ji shi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga yan bindiga
এছাড়াও পড়ুন:
Dadiyata: Buhari ya gaza nemo shi, Tinubu yana da lokaci — Amnesty
Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan Adam ta Amnesty International, ta ce Gwamnatin Tarayya ta yi sakaci game da ɓacewar ɗan gwagwarmaya Abubakar Idris, wanda aka fi sani da Dadiyata.
A wata sanarwa da ta fitar, Amnesty, ta ce abin takaici ne ganin cewa shekara shida kenan da Dadiyata ya ɓace ba tare da wani sahihin bayani ba.
Mutum ɗaya ya rasu, an jikkata wasu yayin arangama da ’yan sanda a Abuja Rufe gidan rediyo ya haifar da cece-ku-ce a NejaDadiyata ya ɓace ne a ranar 2 ga watan Agustan 2019, bayan wasu mutane ɗauke da makamai sun shiga gidansa da ke unguwar Barnawa a Jihar Kaduna, suka tafi da shi.
Tun daga wannan lokacin, iyalansa da abokansa ke jiran jin wani abu game da ɓacewarsa, amma har yanzu babu bayani.
Shugaban Amnesty a Najeriya, Isa Sanusi, ya ce Dadiyata mutum ne mai kishin ƙasa kuma yana da kishi wajen faɗin gaskiya a kafafen sada zumunta.
Ya ce akwai yiwuwar ɓacewar Dadiyata na da alaƙa da irin sukar da yake yi wa gwamnati da wasu ‘yan siyasa.
Ko da yake gwamnati ta musanta cewa tana da hannu, Amnesty ta ce dole gwamnati ta ɗauki alhakin binciken abin da ya faru da bayyana gaskiya domin rage wa iyalan Dadiyata raɗaɗi.
Ƙungiyar ta kuma buƙaci hukumomin tsaro su yi bincike mai zurfi, su kuma bayyana sakamakon da suka samu.
Ta ce abin takaici ne a ce shekara shida kenan ba tare da wani bayani dangane da ɓacewarsa ba.
Hakazalika, Amnesty ta buƙaci Shugaba Bola Ahmed Tinubu, da ya sa baki cikin lamarin domin a san halin da ake ciki.
Ta ce lokaci na ƙurewa, iyalan Dadiyata suna buƙatar amsa guda ɗaya kan inda ya shiga.
Wanda suka halarci taron manema labaran sun haɗa da matarsa Khadija Lame da ƙaninsa Usman Idris.