Aminiya:
2025-06-19@10:39:18 GMT

’Yan bindiga sun kashe manoma 24 a Katsina

Published: 19th, June 2025 GMT

’Yan bindiga sun kashe akalla manoma 20 da wasu mutum uku da kuma wani dan sinitiri a jihar Katsina.

An kashe mutanen ne a wasu hare-hare daban-daban da aka kai karamar hukumar Kankara, daya daga cikin yankunan da suka fi fama da kalubalen tsaro a jihar.

A cewar wani mazaunin yankin da bai amince a bayyana sunansa ba, “Kimanin kwanaki shida da suka gabata ’yan bindiga suka kai hari kauyukan Yargoje, Kwakware, Danmarke, Gidan Dawa da kuma Burdugau.

Yadda manoma suka yi addu’ar roƙon ruwa a Zamfara NAJERIYA A YAU: Yadda Cutar Amosanin Jini Ta Hana Ni Cimma Buri Na

“Sun kashe kusan manoma 20, sun sace wasu sannan suka sace shanun da manoman ke amfani da su wajen huda a gonakin nasu,” in ji shi.

Kazalika, wata majiyar ta shaida wa wakilinmu cewa a ranar Litinin ’yan bindiga sun kai hari kauyen Marmara, shi ma da yake karamar hukumar ta Kankara, inda suka fafata da wasu masu aikin sintiri a yankin da ake kira da C’Watch da wasu ’yan sa-kai, inda suka kashe dan sintirin daya sannan suka jikkata masu aikin sa-kai biyu a kusa da kauyen.

“Sannan sun sami nasarar shiga kauyen Marmara, inda suka kashe mutum uku,” in ji majiyar.

Wakilinmu ya kuma gano cewa a dai daren Litinin din, maharan sun farmaki wasu kauyuka da ke kusa da Kwakware, inda suka sace mutanen da ba a san adadinsu ba.

Wani mazaunin yankin da shi ma bai amince a bayyana sunansa ba ya ce karuwar hare-hare a karamar hukumar a ’yan kwanakin nan ba zai rasa nasaba da yadda wasu kananan hukumomin da ke da makwabtaka da ita suka cimma yarjejeniyar zaman lafiya ba.

“Saboda matukar za a samu yarjejeniyar zaman lafiya a wasu wuraren ba a ko ina ba, akwai yiwuwar su farmaki wuraren da ba su da yarjejeniyar zaman lafiyar,” in ji shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga yan bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

Dan shekara 10 ya kashe mahaifinsa ɗan sanda da bindiga

Wani yaro mai kimanin shekaru goma a duniya ya harbe mahaifinsa wanda jami’in ɗan sanda ne mai mukamin sufeto a Jihar Anambra da ke kudu maso gabashin Nijeriya.

Haka kuma, wakilinmu ya ruwaito cewa yaron ya harbi wani yayansa da bindigar mahaifin nasa ta aiki kirar AK-47.

Kashe jagoran addini na Iran zai kawo ƙarshen yaƙi — Netanyahu Mun bankaɗo sabuwar dabarar ’yan siyasa ta satar kuɗi — EFCC

Wannan dai na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar ’yan sandan Anambra, Tochukwu Ikenga ya raba wa manema labarai a ranar Litinin.

Kakakin ya ce an gaggauta kai jamin asibiti domin a ceto rayuwarsa amma likitoci suka tabbatar da cewa rai ya riga ya yi halinsa.

Sanarwar ta ce “a ranar Lahadi 15 ga watan Yuni, dan gidan wani jami’in dan sanda mai kimanin shekara goma da haihuwa ya harbe mahaifinsa har lahira ya kuma jiwa yayan sa mummunan rauni.

“Abin bakin ciki muna sanar da ku mutuwar jami’inmu mai mukamin sufeto, Okolie Amechi, bisa harbe shi da dansa ya yi a gidansa.

“Wannan ba karamin abin takaici ba ne da kaddara,” in ji sanarwar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda manoma suka yi addu’ar roƙon ruwa a Zamfara
  • An Kashe Wasu ‘Yan Bindiga 12, An Kwato Makamai A Katsina
  • Wasu ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Gidan Sanata Natasha A Kogi
  • Hare-haren Benuwe: Tinubu ya ziyarci waɗanda suka jikkata a asibiti 
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Ƙauyen Kebbi, Sun Kashe Mutane Da Dama
  • Amurka na iya kashe jagoran addini na Iran don mun san inda yake — Trump
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Jami’an Tsaro 4 Da Manoma A Katsina
  • Sabon Shirin Gwamnatin Katsina: Za A Fara Sauya Tunanin Tubabbun ‘Yan Bindiga
  • Dan shekara 10 ya kashe mahaifinsa ɗan sanda da bindiga