Aminiya:
2025-06-17@01:18:20 GMT

Mun bankaɗo sabuwar dabarar ’yan siyasa ta satar kuɗi — EFCC

Published: 17th, June 2025 GMT

Hukumar EFCC mai yaƙi da masu yi wa tattalin arzikin Nijeriya ta’annati ta ce ta gano wata sabuwar dabarar satar kudi da wasu ’yan siyasa ke amfani da ita a yanzu ta hanyar amfani da ’yan damfara wadanda aka fi sani da ’yan yahoo a fadin kasar.

Shugaban EFCC, Ola Olukoyede na wannan furuci ne yayin ganawa da manema labarai a hedikwatar hukumar da ke Abuja a ranar Litinin.

Tinubu zai je jaje bayan kisan fiye da mutum 100 a Benuwe Gwamnati ta kasa ɗaukar matakin da ya dace a kan kashe-kashen Benuwe — Atiku

Olukoyede wanda ya ce wadannan matasa ’yan yahoo da suke zubar da kimar Nijeriya a idon duniya sun kuma faɗa dumu-dumu ta’adar  nan ta garkuwar da mutane domin neman kuɗin fansa.

Ya bayyana cewa kaurin suna da ’yan yahoo suka yi a matsayin miyagu sun shafa wa kowane ɗan Nijeriya bakin fenti da duk inda suka shiga ake ɗari-ɗari da su a matsayin masu laifi.

Shugaban na EFCC ya ce a yanzu da zarar miyagun ’yan siyasa sun samu damar yin ruf da ciki a kan dukiyar kasa, sukan haɗa kai da waɗannan matasa ’yan yahoo-yahoo su boye kuɗaɗen a cikin wani asusun yanar gizo da ake kira wallet.

“Sau tari irin waɗannan ’yan siyasa sukan jibge ’yan yahoo a otel-otel su rika buɗe musu asusun ajiya na kirifto su boye biliyoyin kuɗaɗen da suka sata.”

Olukoyede ya buga misali da wani matashi mai shekaru 22 da hukumar ta kama yana yi wa ’yan siyasa irin wannan aika-aikar wanda aka gano ya samu tukwicin Naira biliyan biyar a tsawon watanni 18 kacal.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Yahoo Satar kudi

এছাড়াও পড়ুন:

Matatar Dangote Za Ta Fara Dakon Man Fetur Da Dizal Kyauta A Fadin Nijeriya

Matatar mai ta Dangote ta sanar da fara dakon man fetur da dizal a fadin kasar daga ranar 15 ga Agusta, 2025. A cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Lahadi, matatar ta bayyana cewa shirin zai hada da ‘yan kasuwa, masu gidajen mai, masana’antun, kamfanonin sadarwa, kamfanonin jiragen sama, da sauran manyan masu amfani da man a fadin kasar nan. A wani bangare na dabarun kasuwanci, matatar Dangote za ta yi dakon man kyauta, domin kawar da tsadar sufuri da kuma inganta harkar kasuwancin matatar a duk fadin kasar. Domin saukaka aikin, matatar ta sayo sabbin tankunan dakon man mai amfani da iskar Gas (CNG) 4,000, wadanda za su zama kashin bayan dakon kayan zuwa inda ake bukata.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mun bankaɗo sabuwar dabarar ’yan sisaya ta satar kuɗi — EFCC
  • Gwamnati ta kasa ɗaukar matakin da ya dace a kan kashe-kashen Benuwe — Atiku
  • Matatar Dangote Za Ta Fara Dakon Man Fetur Da Dizal Kyauta A Fadin Nijeriya
  • Rundunar Sojin Ruwa Ta Nijeriya Ta Lalata Haramtattun Matatun Mai 5 A Ribas
  • Matatar Dangote Zata Fara Rarraba Man Fetur Da Dizal A Nijeriya
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 100 a Benuwe
  • Rawar Da ‘Yan Wasan Afirka Suka Taka A Gasar Premier Ta Ingila
  • Mahara sun kashe mutum 26 a sabon hari a Binuwai
  • Dimokuradiyya A Shekara 26: Ba Yabo Ba Fallasa