Ba zai yiwu mu bar Khamenei a raye ba — Isra’ila
Published: 19th, June 2025 GMT
Ministan Tsaron Isra’ila, Israel Katz ya ce ba zai yiwu su bar jagoran addinin Iran, Ayatollah Ali Khamenei a raye ba.
Israel Katz ya yi barazana ga Ayatollah yana mai cewa ya zama tilas ya ɗauki alhakin hare-hare da makamai masu linzami da Iran ta yi a kan wata cibiyar lafiya da ke kusa da Tel Aviv.
Kafin harin an yi ƙoƙari kwashe marasa lafiya da dama, saboda a ceto rayukansu.
Tuni dai Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya ziyarci Cibiyar Lafiya ta Soroka da ke Beersheba da harin makami mai linzami na Iran ya faɗawa.
Sai dai ita kuma Iran din ta ce ta kai harin ne kan sansanin sojoji da ke kusa da asibitin.
Kalaman Mista Katz na nuna cewa sojojin Isra’ila a yanzu za su yi ƙoƙarin ganin sun kashe Ayatollah — bayan kashe kwamandojinsa na soji da dama.
A makon da ya gabata ne Isra’ila ta ƙaddamar da hare-hare ta sama kan babbar abokiyar gabarta a yankin Gabas ta Tsakiya Iran, lamarin da ya yi sanadiyar mutuwar manyan kwamandojin sojin ƙasar, tare da lalata wasu cibiyoyin nukiliyata da kuma kashe fararen hula da dama.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ayatollah Ali Khamenei Iran
এছাড়াও পড়ুন:
Jamus ta soma jefa kayan agaji a Zirin Gaza
Rundunar sojin Jamus ta fara gudanar da aikin jefa kayayyakin gaji da suka hada da abinci da magunguna ta sama a Zirin Gaza.
Ma’aikatar Tsaron Jamus da ke Berlin, fadar gwamnatin kasar, ce ta tabbatar da hakan, inda ta ce jiragen rundunar sojin sama sun ajiye kunshin tallafi 34 dauki da tan 14 na abinci da kuma magunguna.
Ambaliya: Mutum 165 sun mutu a Nijeriya a bana — NEMA Dadiyata: Buhari ya gaza nemo shi, Tinubu yana da lokaci — AmnestySai dai a cewar Ministan Tsaron Jamus, Moris Pistorius kai tallafi ta sama ba zai yi wani babban tasiri ba.
A cewar Majalisar Dinkin Duniya, Zirin na bukatar tallafin tan dubu 62 na abinci a duk wata domin mutane su rayu.
Tun a ranar Lahadin makon jiya Isra’ila ta aminci da shigar da agaji ta kasa da sama, inda kasashe irinsu Jordan da kuma Hadaddiyar Daular Larabawa suka yi ta jefa kayan agaji ta sama.
Ana ci gaba danka kayayyakin tallafin a hannun kungiyoyin agaji na kasa da kasa da suke ci gaba da ayyukan rarraba su.
Ahmad Nadir, na kungiyar lafiya ta duniya WHO, ya ce tsame hannun Isra’ila daga batun karba da rabon kayan agaji ne kadai zai bai wa kwarraru kan ayyukan agaji damar gudanar da ayyukan da za a samu nasara.
A bayan nan ne Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya WFP ta ce kashi uku na al’ummar Gaza ba su ci abinci na kwanaki ba, kuma mutane 470,000 suna cikin yanayi na juriyar tsananin yunwa wanda tuni ya kai ga mutuwar wasu.
Isra’ila dai na ci gaba da fuskantar suka daga kasashen duniya, kan amfani da yunwa a matsayin makamin yaki kan al’ummar Falasdinu, lamarin da gwamnatin kasar ta ki amincewa da shi.
A makon jiyan ne aka fara shigar da kayyakin agaji zuwa Zirin Gaza wadanda galibi ta sararin samaniya aka rika jefawa da jirage daga kasashen Jordan da Hadaddiyar Daular Larabawa.
Arshiyan Kohen, kakakin ma’aikatar tsaron Isra’ila ya ce, za a dakatar da farmakin soji na tsawon sa’o’i 10 a kowace rana a wasu sassan Gaza tare da ba da damar samun sabbin hanyoyin ba da agaji.
Sakataren Majalisar Dinkin Duniya, Antonio Gutteress ya siffanta wannan matakin da mai sanyaya zuciya bayan damuwa da bala’in da mazauna Gaza suka tsinci kansu a ciki, yana mai fatar gaggauta shigar da kayayyakin agajin da kuma dorewarsa.
Babban jami’in bayar da agajin gaggawa na Majalisar Dinkin Duniya, Tom Fletcher ya yi maraba da matakin, yana mai cewa yanzu haka yana tuntubar kungiyoyi wadanda za su yi duk mai yiwuwa don isa ga mutane da dama da ke fama da yunwa a wannan lokaci.