Kashe jagoran addini na Iran zai kawo ƙarshen yaƙi — Netanyahu
Published: 17th, June 2025 GMT
Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri na kashe jagoran addini na Iran Ayatollah Ali Khamenei ba zai rura wutar rikicin da ake yi yanzu ba, hasali zai ma kawo ƙarshen rikicin ne.
A wata hira ta tsawon minti 20 da tashar talabijin ta ABC ta Amurka ta yi da shi, Netanyahu ya kare matakin farmakin da ƙasarsa ta kai wa Iran, inda ya kwatanta jagoran addini Khamenei a matsayin wani sabon Hitler na wannan zamani.
A yayin hirar, duk wata tambaya da aka yi masa game da ko Shugaban Amurka Donald Trump ya sahale wa Isra’ila kan shirin kashe babban jagoran addinin, Netanyahu ya ki kawar da yuwuwar hakan.
Da aka matsa shi a kan ko za su hari jagoran, sai ya ce : “Muna yin abin da muke da bukatar yi.”
“Mun hari manyan masana nukiliyarsu, sannan har yanzu muna da sauran aikin da za mu yi a daya bangaren.”
Netanyahu ya nuna cewa sun kai wa Iran hari ne domin kare al’umma, domin kare duk wata barazanar nukiliya daga Iran.
Firaministan a hirarrakin da ya yi da kafofin yada labaran Amurka a kwanakin nan, ya bayyana rikicin Isra’ila da Iran a matsayin “yakin wayewa da dabbanci.”
Ya ce akwai bukatar Amurkawa su damu matuka game da kokarin da Tehran ke yi na mallakar makamin nukiliya da karfinta na makami mai linzami.
“Idan yau birnin Tel Aviv ne, gobe kuma New York ne,” kamar yadda Netanyahu ya shaida wa wakilin ABC, Jon Karl.
AFP
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ayatollah Ali Khamenei Benjamin Netanyahu Netanyahu ya
এছাড়াও পড়ুন:
Isra’ila Ta Kashe Mutane 4 Tare Da Jikkata Wasu Guda 3 A Kudancin Labanon
A ci gaba da keta yarjejeniyar dakatar da bude wuta da HKI ke yi a kasar labanon a jiya ma ta kai hari a kudancin kasar kuma ta yi sanadiyar mutuwar mauta 4 tare da jikkata wasu guda 3,
Isra’ila ta kai hari da jirgin sama mara matuki kan wata mota a kauyen kafr rumman , kana kuma ta sake kai wani harin a garin kafr sir kamar yadda rahotanni suka bayyana, kuma wadannan hare haren suna zuwa ne kwanaki 3 bayan da sojojin israila suka kai samame ta kasa a kudancin labanon a yankin Nabatiya inda suka kai hari a jiya,
A ranar jumaa da ta gabata ne shugaban kasar ta labanon joseph Aun ya nuna damuwarsa game da ci gaba da keta yarjejeniyar dakatar da bude wuta da Isra’ila ke yi, inda yayi tir da tel aviv game da irin mataken da take dauka na karya yarjejeniyar.
A yan kwanankin nan sakatare janar din kungiyar hizbullah na kasar labanon shaikh Naim Qassem ya jaddada cewa tsayin daka ne karfin labanon, don haka Amurka na matsin lamba ne don ganin an danneta an tauye mata yanci da raunata ta don biyan muradun gwamnati.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran Ta Gargadi Isra’ila Kuma Tasha Alwashin Kare Shirinta Na Nukiliya November 2, 2025 Shugaban AmurkaTrump ya yi barazanar daukar matakin soji kan Najeriya November 2, 2025 Kamaru: Jagroan ‘Yan Hamayya Ya Yi Kira Da A Tsayar Da Harkoki A Fadin kasar November 1, 2025 MDD Tana Sa Ido Akan Kashe-kashen Da Ake Yi A Zaben Kasar Tanzania November 1, 2025 Gaza: Daga Tsagaita Wuta Zuwa Yanzu Fiye Da Mutane 200 Ne Su Ka Yi Shahada November 1, 2025 Shugaban Najeriya Ya Mayar Da Martani Ga Takwaransa Na Amurka Akan Rikicin Addini November 1, 2025 Iran ta damu da halin da ake ciki a yankin El Fasher na Sudan November 1, 2025 Kwamitin Tsaron MDD ya goyi bayan shirin Morocco game da yankin Yammacin Sahara November 1, 2025 Samia Suluhu Hassan ta lashe zaben shugaban kasa a Tanzaniya November 1, 2025 Najeriya ta musanta ikirarin Trump, na cewa Kristoci na fuskantar babbar barazana a kasar November 1, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci