Kashe jagoran addini na Iran zai kawo ƙarshen yaƙi — Netanyahu
Published: 17th, June 2025 GMT
Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri na kashe jagoran addini na Iran Ayatollah Ali Khamenei ba zai rura wutar rikicin da ake yi yanzu ba, hasali zai ma kawo ƙarshen rikicin ne.
A wata hira ta tsawon minti 20 da tashar talabijin ta ABC ta Amurka ta yi da shi, Netanyahu ya kare matakin farmakin da ƙasarsa ta kai wa Iran, inda ya kwatanta jagoran addini Khamenei a matsayin wani sabon Hitler na wannan zamani.
A yayin hirar, duk wata tambaya da aka yi masa game da ko Shugaban Amurka Donald Trump ya sahale wa Isra’ila kan shirin kashe babban jagoran addinin, Netanyahu ya ki kawar da yuwuwar hakan.
Da aka matsa shi a kan ko za su hari jagoran, sai ya ce : “Muna yin abin da muke da bukatar yi.”
“Mun hari manyan masana nukiliyarsu, sannan har yanzu muna da sauran aikin da za mu yi a daya bangaren.”
Netanyahu ya nuna cewa sun kai wa Iran hari ne domin kare al’umma, domin kare duk wata barazanar nukiliya daga Iran.
Firaministan a hirarrakin da ya yi da kafofin yada labaran Amurka a kwanakin nan, ya bayyana rikicin Isra’ila da Iran a matsayin “yakin wayewa da dabbanci.”
Ya ce akwai bukatar Amurkawa su damu matuka game da kokarin da Tehran ke yi na mallakar makamin nukiliya da karfinta na makami mai linzami.
“Idan yau birnin Tel Aviv ne, gobe kuma New York ne,” kamar yadda Netanyahu ya shaida wa wakilin ABC, Jon Karl.
AFP
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ayatollah Ali Khamenei Benjamin Netanyahu Netanyahu ya
এছাড়াও পড়ুন:
ALGON ta karrama Gwamna Buni da lambar yabo kan kawo ci gaba a Yobe
Ƙungiyar shugabannin ƙananan hukumomin Jihar Yobe (ALGON) ta karrama Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni, da lambar yabo ta karramawa bisa himmar ayyukan raya ƙasa da gwamnatinsa ke gudanarwa a faɗin jihar.
Karramawar, wacce aka bayyana a matsayin irinta ta farko a tarihin Jihar Yobe, shugabannin ƙananan hukumomi 17 na jihar suka ba da ita ga gwamna.
Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a BornoDa yake jawabi, shugaban ƙungiyar ALGON a Jihar Yobe, kuma shugaban ƙaramar hukumar Damaturu, Alhaji Bukar Adamu, ya yaba da yadda Gwamna Buni yake gudanar da harkokin mulki na bai ɗaya. Ya ce nasarorin da aka samu sun haɗa da fannoni na ilimi, noma, kiwon lafiya, kasuwanci, da samar da ababen more rayuwa.
“Babu wani sashe a jihar da aka bari a baya a cikin ayyukan ci gaban da Gwamna Mai Mala Buni ke aiwatarwa,” in ji Adamu.
A nasa martanin, Gwamna Buni, wanda mataimakinsa, Alhaji Idi Barde Gubana, ya wakilta, ya karɓi karramawar a matsayin “hanyar mayar da martani mai ƙarfi” da ke tabbatar da tasirin gwamnatinsa a matakin farko.
Ya kuma yi alƙawarin ci gaba da ƙoƙarin kai Yobe matsayin jiha da za ta iya gogayya da takwarorinta a fagen ci gaban ƙasa.
Wakilinmu ya ruwaito cewa taron ya samu halartar manyan jami’an gwamnati, ’yan siyasa daga ciki da wajen jihar, da kuma sarakunan gargajiya.