Aminiya:
2025-06-17@01:37:13 GMT

Kashe jagoran addini na Iran zai kawo ƙarshen yaƙi — Netanyahu

Published: 17th, June 2025 GMT

Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri na kashe jagoran addini na Iran Ayatollah Ali Khamenei ba zai rura wutar rikicin da ake yi yanzu ba, hasali zai ma kawo ƙarshen rikicin ne.

A wata hira ta tsawon minti 20 da tashar talabijin ta ABC ta Amurka ta yi da shi, Netanyahu ya kare matakin farmakin da ƙasarsa ta kai wa Iran, inda ya kwatanta jagoran addini Khamenei a matsayin wani sabon Hitler na wannan zamani.

Mun bankaɗo sabuwar dabarar ’yan sisaya ta satar kuɗi — EFCC Tinubu zai je jaje bayan kisan fiye da mutum 100 a Benuwe

A yayin hirar, duk wata tambaya da aka yi masa game da ko Shugaban Amurka Donald Trump ya sahale wa Isra’ila kan shirin kashe babban jagoran addinin, Netanyahu ya ki kawar da yuwuwar hakan.

Da aka matsa shi a kan ko za su hari jagoran, sai ya ce : “Muna yin abin da muke da bukatar yi.”

“Mun hari manyan masana nukiliyarsu, sannan har yanzu muna da sauran aikin da za mu yi a daya bangaren.”

Netanyahu ya nuna cewa sun kai wa Iran hari ne domin kare al’umma, domin kare duk wata barazanar nukiliya daga Iran.

Firaministan a hirarrakin da ya yi da kafofin yada labaran Amurka a kwanakin nan, ya bayyana rikicin Isra’ila da Iran a matsayin “yakin wayewa da dabbanci.”

Ya ce akwai bukatar Amurkawa su damu matuka game da kokarin da Tehran ke yi na mallakar makamin nukiliya da karfinta na makami mai linzami.

“Idan yau birnin Tel Aviv ne, gobe kuma New York ne,” kamar yadda Netanyahu ya shaida wa wakilin ABC, Jon Karl.

AFP

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ayatollah Ali Khamenei Benjamin Netanyahu Netanyahu ya

এছাড়াও পড়ুন:

Isra’ila da Iran su daidaita rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin Tarayya

Gwamnatin Tarayya ta roƙi ƙasashen Isra’ila da Iran da su daina rikici, su zauna lafiya su sasanta tsakaninsu. 

A wata sanarwa da Ma’aikatar Harkokin Waje ta fitar, ta bayyana damuwa kan yadda rikicin ke ƙara ta’azzara, inda ta nemi ɓangarorin biyu da su kai zuciya nesa don samar da zaman lafiya a duniya baki ɗaya.

Mahara sun kashe mutum 26 a sabon hari a Binuwai Mulkin Tinubu ya fi kowane muni tun bayan dawowar mulkin farar hula — Dalung

Sanarwar ta ce faɗa da ramuwar gayya na jefa rayukan fararen hula cikin hatsari, kuma yana iya haddasa rikici mai muni a yankin Gabas ta Tsakiya, wanda hakan zai iya barazana ga tsaron duniya da kuma ci gaban tattalin arziƙi dunuya.

“Mu a matsayimmu na ƙasa mai son zaman lafiya, muna roƙon ƙasashen da ke rikici da su zauna su tattauna maimakon su ci gaba da faɗa.”

Gwamnatin Tarayya ta kuma yi kira ga ƙasashen duniya, musamman Kwamitin Tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya, da su ɗauki matakai don hana yaɗuwar rikicin da kuma samo hanyar warware matsalar.

Sanarwar ta ƙara da cewa amfani da ƙarfin soji ba shi da amfani matuƙa, domin faɗa ba zai kawo sauƙi ba.

Najeriya ta ce a shirye ta ke ta bayar da taimako domin hana yaɗuwar rikicin da kuma tabbatar da zaman lafiya a yankin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ya Ce: Sojojin Isra’ila Sun Kashe Kananan Yara Masu Yawa A Iran
  • Sabon harin Iran ya hallaka mana mutum 8 – Isra’ila
  • Martanin sojojin Iran ga Isra’ila zai zama mafi muni idan aka ci gaba da kai hari (Pezeshkian)
  • Isra’ila da Iran su daidaita rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin Tarayya
  • Gwamnatin Najeriya Ta Yi Allawadai Da Harin Da “Isra’ila” Ta Kawo Wa Iran
  • Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin Tarayya
  • Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu
  • Mahara sun kashe mutum 26 a sabon hari a Binuwai
  • Jagora: Sojojin Iran ba zasu sararawa Isra’ila ba