Aminiya:
2025-09-18@00:57:09 GMT

An ɗaure mutum 7 kan yi wa ɗan sanda rauni a Kano

Published: 19th, June 2025 GMT

Wata kotun shari’ar Musulunci da ke Kofar Kudu a Jihar Kano, ta yanke wa wasu mutum bakwai hukuncin ɗauri, bayan da suka ji wa wani ɗan sanda rauni yayin da ake ƙoƙarin cafke su.

Al’ummar unguwannin Tudun Maliki da Sheka ne suka kai rahoton mutanen, inda suka zarge su da sayar da miyagun ƙwayoyi.

’Yan bindiga sun kashe manoma 24 a Katsina Yadda manoma suka yi addu’ar roƙon ruwa a Zamfara

A kotun, an gurfanar da su kan laifukan haɗa baki domin tayar da hankali, jikkata mutum, hana ‘yan sanda yin aikinsu yadda ya dace, da kuma ɓoye wanda ake zargi.

Lauyan gwamnati, Barrista Aliya Ibrahim Aminu ce, ta karanta musu tuhumar a gaban kotu.

Ɗaya daga cikinsu ya musanta laifin, yayin da Idris Ado da wasu mutum biyar suka amsa wasu daga cikin tuhumar amma suka ƙi amincewa da sauran.

Alƙalin kotun, Khadi Shamsuddeen Ado Abdullahi Unguwar Gini, ya yanke musu hukuncin ɗaurin wata uku bisa laifin farko, da wata uku a laifi na biyu.

Haka kuma ya ƙara yanke musu hukuncin ɗaurin wata uku tare da tarar Naira 15,000.

Za a yi wa kowannensu bulala 20.

Baya ga haka kuma, kotun ta umarce su da su yi wata shida a ƙarƙashin kulawa, inda za su riƙa share magudanan ruwa a unguwanninsu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ɗan Sanda ɗauri

এছাড়াও পড়ুন:

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

 

Shugabannin biyu sun yi nazari kan muhimman fannonin hadin gwiwa tsakanin Nijeriya da Faransa, inda suka amince da zurfafa hadin gwiwa don samun ci gaban juna da kwanciyar hankali a duniya.

 

LEADERSHIP ta ruwaito cewa ba a bayar da wani dalili na sauya wannan hutun ba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati ta fara duba yara marasa galihu kyauta a asibitin Aminu Kano
  • ‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja
  • Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala
  • ’Yan sanda sun kama mutum 6 kan satar zinarin N109m a Kebbi
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
  • Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 40 a masallaci a Zamfara
  • ’Yan sanda sun sasanta rikicin asibitin AKTH da KEDCO
  • Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada Sakamakon Kisan Kiyashin ‘Yan Sahayoniyya A Gaza Ya Kusaci 65,000
  • Rabin Sojojin Isra’ila da suka ji rauni a yakin Gaza na fama da ciwon damuwa