An Nemi A Kafa Dokar Ta-ɓaci Kan Masu Ƙwacen Waya
Published: 20th, June 2025 GMT
Hukumar kididdiga ta kasa (NBS) ce ta bayyana hakan a rahoton ayyukan ta’addanci na watanni 12. Rahoton ya bayyana ayyukan ta’addanci miliyan 51.89 da suka shafi iyalai, satar waya ce mafi yawa a ciki da kaso 13.8 da rahoton satar waya miliyan 25.
Rahoton ya nuna akwai layukan waya da ke aiki a wayoyin hannu miliyan 216.
A yayin da duniya ke kara komawa a duniyar fasaha, wayoyin hannu na yi wa al’umma amfani fiye da sadarwa domin suna amfani a matsayin wajen neman ilimi, kasuwanci, karamin banki da biyan bukatun yau da kullum, kuma hanyar rayuwar al’umma da dama wanda hakan ya sa kwacen waya ya zama abin damuwa.
Nazarin ya nuna, a lokacin NBS ta bayar da rahoton mutane miliyan 17.97 ne suka fada tarkon masu kwacen waya. Daga ciki akwai Dorcas Oluwaseyi wadda aka sace wayar ta a cikin mota. “Sun kwace jaka ta, suka dauki karamar jaka ta, suka dauke waya, da katukan ATM di na.”
A yau bata gari suna farautar wayoyin hannu a al’ummar da kunci da tsadar rayuwa ta yi wa katutu, a yayin da raunanan hukumomin tsaro suka bar ta’addancin na ci gaba da faruwa a kullum.
Hukumomin tsaro a lokuta daban-daban kan bayyana kokarin da suke yi wajen kawar da ta’addancin kwacen waya sai dai al’umma na kukan kokarin jami’an ba wani abin rubutawa ba ne a bisa ga yadda matsalar karuwa take yi maimakon raguwa.
Jihar Kano ce kan gaba a Arewacin Nijeriya inda kwacen waya ya yanke cibi ta yadda barayin ba sani ba sabo suka mayar da ‘ya’ya da yawa marayu, suka mayar da mata zawarawa suka raba dimbin al’umma da mahaifan su, duka a dalilin kwace wayoyin wadanda ba su ji ba ba su gani ba.
Kisan gillar da wani mai kwacen waya ya yi wa matashin jami’in sojin ruwan Nijeriya a Kaduna a kan ya ki aminta ya bashi wayarsa ya kara daga hankalin al’umma a kan girman matsalar wadda har za a iya cakawa soja wuka har lahira.
Sojan Laftanar Kwamanda M. Buba ya tsaya ne a bakin gadar Kawo, Kaduna domin ya yi facin tayar motarsa a inda barawon ya samu sa’a ya caka masa wuka lamarin da duk da jama’a sun kawo dauki sun yi wa barawon kisan gilla, tuni hukumar kwalejin horas da hafsoshin soji da ke Jaji in da sojan ke karbar horo suka kama mutane 27 a maboyar su.
A Gombe matashin magidanci, Ahmad Kasiran ne masu kwacen waya suka raba da duniya a kan wayarsa lamarin ya daga hankalin jama’a tare da girgiza su.
A yayin hada wannan rahoton wakilin mu ya samu rahoton yadda masu kwacen waya suka cakawa wani malamin jami’a wuka a Kano suka bar shi a cikin jini.
Gagarumar matsalar kwacen waya ta ta’azzara ne a dalilin rashin madafa a halin tsadar rayuwa. Rashin aikin yi ya mamaye ko’ina ta yadda jama’a ba su samun ayyukan yi. Hauhawar farashin kaya da karyewar darajar naira ya kara girman wannan matsalar wadda ta jefa miliyoyin ‘yan Nijeriya a cikin fatara da bude kofar ta’addanci da rashin tsaro.
A bisa ga wannan a yau jama’a da dama sun zabi kwacen waya a matsayin hanya mafi sauki ta samun kudi a bisa ga bukatar da ake da ita ta wayoyin da ba sababbi ba.
A haka wasu na ganin mafita ita ce dokar agajin gaggawa, gyaran dokoki, karfafa hanyoyin fasahar bin diddigin gano waya, zartas da hukunci mai tsauri da aiwatar da shiraruwan rage matsalar rashin ayyukan yi.
Inganta dokokin hukumomin tsaro ya zama wajibi kuma hanya ta farko a fafutukar kawar da wannan matsalar. Hobbasar Rundunar ‘Yan Sanda ba mai yawa ba ce domin rahoton hukumar kididdiga ya nuna kashi 90% na wadanda aka yi wa kwacen waya sun kai rahoton faruwar lamarin, amma kashi 11.7% ne kawai aka gano.
A mabambantan ra’ayoyin jama’a da LEADERSHIP Hausa ta tattaro sun bayyana wajibcin gwamnati da musamman hukumomin tsaro da su kaddamar da dokar daukin gaggawa, tare da hukunci mai tsauri kan masu kwacen waya da ke addabar al’umma tun kafin lamarin ya kara tabarbarewar da zai fi karfin hukuma.
“Wajibi ne hukumomin tsaro su kara daura damarar yaki da barayin waya domin matsalar ta wuce duk yadda ake tunani haka ma gwamnatoci su ba da cikakken goyon baya musamman a kafa dokar ta baci domin duk matsalar da ake yi wa jama’a kisan gilla to gagaruma ce haka ma a yaki matsalar shaye- shaye wadda ita sila.” In ji Kallamu Abubakar.
Abba Fadi ya bayyana nasa ra’ayin yana cewar “Inna lillahi wa Inna ilaihi Raji’un. Wannan masifa ni wallahi har na gaji da jin labarin kashe- kashen all’umar Annabi da masu kwacen waya ke yi. A gakiya ya kamata gwamnati ta tashi tsaye a kan lamarin nan tun kafin barayin waya su ci mu da yaki a kasar nan. Idan an kama barayin waya a rika zartar musu da hukuncin kisa a bainar jama’a don ya zama izina ga masu aikatawa.”
A ra’ayin Abdulkadir Aminu ya na ganin domin magance wannan matsalar shine “A dauki matakin kafa dokar ta baci ta hanyar ba- sani ba- sabo a kan barayin waya a kuma tsaurara hukunci ga duk wanda aka kama da kwacen da kuma sayen wayoyin sata.”
Shi kuwa Umar Albashir cewa ya yi “Tabbatar da hukunci ga duk wadanda aka kama da satar waya shine zai magance matsalar da sauran matsalolin da ake fuskanta. Wani babban abin dubawa shine matsalar shaye- shaye ita ce ta haddasa matsalar daba wadda kuma ta haifar da ta’addanci wanda shi kuma ya haifar da sace- sace da kwace- kwace wanda matukar ba a kawar da hanyar shaye-shaye ba to ba a dauki hanyar magance matsalolin ba.”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Waya masu kwacen waya hukumomin tsaro
এছাড়াও পড়ুন:
Dan Wasan Gaban Chelsea, Murdyk Ka Iya Shafe Shekaru 4 Ba Tare Da Ya Buga Wasa Ba
Murdyk ya halarci wasan karshe na gasar cin kofin Uefa Conference League da Chelsea ta doke Real Betis a watan da ya gabata, amma kuma ba a cikin tawagar Chelsea ba, a cikin wata sanarwa da ta fitar ranar Laraba, FA ta ce “Za mu iya tabbatar da cewa an tuhumi Mykhailo Mudryk da laifin keta dokar hana kara kuzari, ta hanyar amfani da wani abu da aka haramta, wanda kuma ya sabawa doka ta 3 da 4 a kundin dokokin FA na hana kara kuzari.
Zuwa yanzu Chelsea ba ta ce komai ba dangane da tuhumar da akeyiwa Murdyk amma a watan Disamba ta ce, ta na fatan dan wasan nata yayi nasara duba da cewa “Mykhailo ya tabbatar da cewa bai taba yin amfani da haramtattun abubuwa da gangan ba” tace a cikin sanarwar, a karkashin dokokin FA, yan wasa sunada yancin bukatar ayi masu gwaji na biyu bayan an samu tabbacin amfani da kwayoyi masu kara kuzari a gwajin farko, amma idan gwajin na biyu ya zo daidai da na farko to za a yanke masu hukunci.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp