Aminiya:
2025-08-02@03:43:51 GMT

Buni ya bai wa manoma 1,000 tallafin aikin gona

Published: 18th, June 2025 GMT

Gwamnan jihar Yobe, Mai Mala Buni, ya raba kayayyakin noma ga magidanta 1,000 da suka hada da ‘yan gudun hijira daga Mandunari da ke karamar hukumar Gujba da sauran al’ummomin da suke zaune a yankin.

Da yake jawabi a gidan gwamnati da ke Damaturu, Buni ya bayyana cewa, duk da cewa al’ummomin Mandunari ya kasance su ne yankin al’umma guda daya tilo a jihar Yobe da har yanzu ba a sake tsugunar da su ba, al’ummarta sun nuna jajircewarsu na komawa gidajen kakanninsu.

Amurka na iya kashe jagoran addini na Iran don mun san inda yake — Trump Iran ta kai hari hedikwatar hukumar leƙen asirin Isra’ila

Ya kuma jaddada kudirin gwamnatin jihar na tabbatar da dawowar duk ‘yan gudun hijira lafiya, tare da tallafa musu  ta hanyar saka hannun jari a ayyukan more rayuwa, tsaro, gidaje, kiwon lafiya, da ilimi.

Kayayyakin da aka bada tallafi ga manoman sun hada da ingantattun kayayyakin yin noma da irin masara, kubewa, gyada, gero, da irin shinkafa, taki, maganin kashe kwari da na ciyawa da makamantansu.

“A lokacin rani, manoma za su sami famfunan ruwa da ingantattun irin albasa, tumatir, kabeji, latas, da barkono.

“Gwamnatin jihar Yobe ta riga ta zuba jarin sama da dala biliyan 4 a ayyukan noma a fadin al’ummomi 178 na mazabun Jihar, inda ta samar da taraktoci, takin zamani, da sauran kayan masarufi don bunkasa samar da abinci,” inji gwamnan.

Ya ce gwamnati tare da hadin gwiwar hukumar raya kasa da hadin gwiwar kasar Switzerland za ta tallafa wa karin magidanta 2,000 da kayan noma da kiwo a Gaidam, Tarmuwa, da Damaturu.

Buni ya kara da cewa, kananan manoma za su kuma samu horo kan noma da kiwo da sauyin yanayi, yayin da a karkashin shirin samar da mafita mai dorewa manoma 1,000 da ma’aikatar kula da kiwon lafiya ta horas da su za su samu kananan tallafi don ci gaba da rayuwarsu.

“Muna ci gaba da jajircewa wajen ganin ba a bar wata al’umma a baya ba, duk wanda ya rasa matsugunai ya cancanci a ba shi dama mai kyau don sake gina rayuwarsu cikin aminci da mutunci,” in ji gwamnan.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Yobe

এছাড়াও পড়ুন:

Manyan makarantu 2 ne kacal ke da rajista a Katsina — Gwamnati

Kwamitin da Gwamnan Jihar Katsina, Dikko Umari Radda, ya kafa domin binciken ayyukan makarantun gaba da sakanadare masu zaman kansu na jihar, ya tabbatar da cewa, 37 cikin 39 ba su da rajista da gwamnati.

Shugaban kwamitin, Farfesa Ahmed Muhammad Bakori, ne ya bayyana hakan a wani taron masu ruwa da tsaki da aka gudanar a ƙaramar hukumar Bakori da ke jihar.

Mamakon ruwan sama ya haddasa ambaliya a Maiduguri  Sojoji sun daƙile hari, sun kashe mayaƙan Boko Haram 9 a Borno

Bakori, wanda shi ne Kwamishinan Harkokin Noma na jihar, ya ce binciken kwamitin ya gano cewa makarantu biyu masu zaman kansu ne kacal a faɗin jihar ke da cikakkiyar rajista da hukumomin da suka dace.

“Jihar Katsina na da makaruntun gaba da sakanadare na gwamnati huɗu da ke bayar da takardar shaidar difloma da koyarwa, sai kuma ƙarin 39 masu zaman kansu.

“Sai dai bincikenmu ya bankaɗo biyu ne kacal a cikin 39 suke da cikakkiyar rajista da hukumomi.”

Kwamishinan, ya kuma ce shida daga cikinsu na buƙatar gyare-gyare domin kammala rajistar, yayin da 22 ke aiki ba tare da rajistar ba.

“Ƙarƙashin sabon tsarin da muka ɗauka yanzu, ya zamo dole makarantun da ke bayar da takardar shaidar digiri su yi rajista da Hukumar Jami’o’i ta Ƙasa (NUC).

“Masu difloma kuma da Hukumar Kula da Ilimin Fasaha (NBTE), sai masu koyarwa da Hukumar Kula da Kwalejin Ilimi ta Ƙasa (NCCE).

Bakori, ya jaddada cewa, duk makarantar da ta saɓa wa wannan tsarin, a shirye gwamnatin take ta rufe ta.

Sai dai ya yi wa ɗaliban da ke makarantun albishir ɗin cewa gwamnatin za ta tabbatar ta sauya musu makaranta zuwa masu rajista daga waɗanda ba su da su, idan buƙatar rufe su ta taso.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda Yajin Aikin Ma’aikatan Jinya Ya Bar Baya Da Kura A Asibitocin Jihar Filato
  • Hukumar Kula da Da’ar Ma’aikata Za Ta Fara Daukar Bayanai Ta Yanar Gizo
  • Tallafin matar Tinubu na N1bn ga ’yan gudun hijirar Binuwai ya bar baya da kura
  • Gwamna Namadi Ya Kaddamar da Tallafin Miliyoyin Naira Ga Ƴan NURTW da Mahauta a Jigawa
  • Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin Tarayya
  • Manyan makarantu 2 ne kacal ke da rajista a Katsina — Gwamnati
  • Shugaban SUBEB Yayi Alkawarin Bayar Da Tallafin Ilimi A Jihar Nasarawa
  • Gwamnatin Jihar Kano Ta Kaddamar da Manufar Sauyin Yanayi
  • An shawarci Manoman Kwara Da Su Yi Taka-Tsan-Tsan Saboda Hasashen Ruwa Da Tsawa A Jihar
  • Faransa Ta Bayyana Wuce Gona Da Irin ‘Yan Sahayoniyya Kan Falasdinawa Da Ayyukan Ta’addanci