Buni ya bai wa manoma 1,000 tallafin aikin gona
Published: 18th, June 2025 GMT
Gwamnan jihar Yobe, Mai Mala Buni, ya raba kayayyakin noma ga magidanta 1,000 da suka hada da ‘yan gudun hijira daga Mandunari da ke karamar hukumar Gujba da sauran al’ummomin da suke zaune a yankin.
Da yake jawabi a gidan gwamnati da ke Damaturu, Buni ya bayyana cewa, duk da cewa al’ummomin Mandunari ya kasance su ne yankin al’umma guda daya tilo a jihar Yobe da har yanzu ba a sake tsugunar da su ba, al’ummarta sun nuna jajircewarsu na komawa gidajen kakanninsu.
Ya kuma jaddada kudirin gwamnatin jihar na tabbatar da dawowar duk ‘yan gudun hijira lafiya, tare da tallafa musu ta hanyar saka hannun jari a ayyukan more rayuwa, tsaro, gidaje, kiwon lafiya, da ilimi.
Kayayyakin da aka bada tallafi ga manoman sun hada da ingantattun kayayyakin yin noma da irin masara, kubewa, gyada, gero, da irin shinkafa, taki, maganin kashe kwari da na ciyawa da makamantansu.
“A lokacin rani, manoma za su sami famfunan ruwa da ingantattun irin albasa, tumatir, kabeji, latas, da barkono.
“Gwamnatin jihar Yobe ta riga ta zuba jarin sama da dala biliyan 4 a ayyukan noma a fadin al’ummomi 178 na mazabun Jihar, inda ta samar da taraktoci, takin zamani, da sauran kayan masarufi don bunkasa samar da abinci,” inji gwamnan.
Ya ce gwamnati tare da hadin gwiwar hukumar raya kasa da hadin gwiwar kasar Switzerland za ta tallafa wa karin magidanta 2,000 da kayan noma da kiwo a Gaidam, Tarmuwa, da Damaturu.
Buni ya kara da cewa, kananan manoma za su kuma samu horo kan noma da kiwo da sauyin yanayi, yayin da a karkashin shirin samar da mafita mai dorewa manoma 1,000 da ma’aikatar kula da kiwon lafiya ta horas da su za su samu kananan tallafi don ci gaba da rayuwarsu.
“Muna ci gaba da jajircewa wajen ganin ba a bar wata al’umma a baya ba, duk wanda ya rasa matsugunai ya cancanci a ba shi dama mai kyau don sake gina rayuwarsu cikin aminci da mutunci,” in ji gwamnan.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jihar Yobe
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu ya bayar umarnin binciken hare-haren Benuwe
Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya umarci jami’an tsaro da su yi bincike tare da gano waɗanda suka kai hari a Jihar Benuwe, inda aka kashe sama da mutum 100.
Harin ya faru ne a ƙauyen Yelwata da ke Ƙaramar Hukumar Guma a jihar.
Iran ta rataye mutumin da ta kama yana yi wa Isra’ila leƙen asiri KADSEMA da IOM sun fara tantance ɓarnar da ambaliya ta yi a KadunaBayan harin, matasa sun rufe hanyar Lafiya zuwa. Makurdi domin nuna ɓacin ransu.
Zanga-zangar ta ci gaba da gudana har zuwa safiyar ranar Lahadi a birnin Makurdi, babban birnin jihar.
Rundunar ‘yan sandan jihar ta yi amfani da barkonon tsohuwa domin tarwatsa masu zanga-zangar.
A daren ranar Lahadi, Shugaba Tinubu ya wallafa saƙo a a shafin sa na X, inda ya ce dole a kawo ƙarshen wannan kashe-kashe, kuma ya umarci jami’an tsaro su ɗauki mataki don kama duk masu hannu a rikicin.
Tinubu ya kuma buƙaci Gwamnan Jihar Benuwe, Hyacinth Alia, da ya jagoranci tattaunawa da yin sulhu tsakanin manoma da makiyaya domin wanzar da zaman lafiya.
Ya gargaɗi shugabannin siyasa da na al’umma da su guji furucin da ka iya haifar da tarzoma.
Ya ce lokaci ya yi da za a haɗa kai domin warware matsaloli da hanyar gaskiya, adalci da fahimta, domin a samu zaman lafiya a Jihar Benuwe.