Leadership News Hausa:
2025-09-18@00:54:54 GMT

‘Yan Bindiga Sun Kashe Jami’an Tsaro 4 Da Manoma A Katsina

Published: 17th, June 2025 GMT

‘Yan Bindiga Sun Kashe Jami’an Tsaro 4 Da Manoma A Katsina

Jaridar LEADERSHIP ta ruwaito cewa gwamnatin Jihar Katsina na ƙoƙarin sasantawa da wasu ƙungiyoyin ‘yan bindiga a wasu yankunan jihar.

Wasu daga cikin ‘yan bindigar da ke Jibia, Batsari da DanMusa sun amince da zaman lafiya tare da miƙa makamansu.

Sai dai wannan hari na baya-bayan nan ya sa al’umma sun fara shakkar ko zaman lafiyar zai ɗore.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Hari Yan bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara

A ƙalla fasinjoji 17 ne suka rasa rayukansu bayan wata motar haya ta faɗa cikin wata gada da ta ruguje a kan titin Gwalli da ke ƙaramar hukumar Gummi, jihar Zamfara.

A cewar hukumar kiyaye haɗura ta ƙasa (FRSC) reshen Zamfara, hatsarin ya faru ne a daren Lahadi lokacin da motar ɗauke da kaya da fasinjoji ta faɗa cikin gadar da ta ruguje. Jami’in hulɗa da jama’a na hukumar, SRC Isah Aliyu, ya tabbatar da lamarin a wata sanarwa da ya fitar.

Kwamandan FRSC na jihar, CC Aliyu Magaji, wanda ya ziyarci wurin hatsarin, ya bayyana matuƙar baƙin cikinsa da asarar rayukan, inda mafi yawansu mata ne. Ya ce hatsarin ya biyo bayan nauyin da aka ɗora wa motar fiye da ƙima da kuma tafiya da daddare.

Hukumar ta gode wa mazauna yankin da suka gaggauta taimakawa wajen ceto wasu daga cikin waɗanda hatsarin ya rutsa da su. Kwamanda Aliyu ya yi ta’aziyya ga gwamnatin Zamfara da al’ummar Gummi, tare da yin kira ga direbobi su rika bin ƙa’idojin hanya da kuma guje wa tuƙa mota da dare domin kare rayuka.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 
  • Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa
  • Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba
  • NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
  • Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo
  • ‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara
  • ’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu
  • Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato
  • Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara