Yadda manoma suka yi addu’ar roƙon ruwa a Zamfara
Published: 19th, June 2025 GMT
Al’ummar garin Kaura Namoda da ke Jihar Zamfara, sun gudanar da sallar roƙon ruwa bayan da aka shafe kwanaki ba tare da an samu ruwan sama ba.
Mutane da dama sun fara nuna damuwa saboda har yanzu babu ruwa ba, duk da cewa an shiga lokacin damina tun da daɗewa.
NAJERIYA A YAU: Yadda Cutar Amosanin Jini Ta Hana Ni Cimma Buri Na Sojojin Nijeriya sun kashe gomman ’yan ta’adda a Tafkin ChadiWasu manoma da ke jiran ruwa domin su yi shuka sun ce har zuwa ranar Laraba sun fito domin roƙon Allah Ya saukar da ruwa.
Babban limamin garin Kaura, Malam Badamasi, ne ya jagoranci sallar.
Ya ce sun ga dacewar yin wannan addu’a ne domin tun mako biyu da suka wuce ba su samu ruwa ba a garin.
Sheikh Malam Muhammad ya yi wa jama’a wa’azi mai ratsa zuciya, inda ya tunatar da su muhimmancin komawa ga Allah da yawaita ibada a irin wannan lokaci na fari da rashin ruwa.
Daga cikin waɗanda suka halarci sallar akwai Abdul Hadi Ibrahim Mai Yadi da Kasimu Namadi.
Sun ce sun zo domin neman gafara daga Allah da fatan zai saukar da ruwa.
Sun bayyana damuwarsu da cewa mako biyu kenan ba a yi ruwa a yankinsu ba, kuma ruwan da ya zo a baya bai wadatar wajen yin shuka ba, sai kuma ya ɗauke gaba ɗaya.
Sun ce fari na ruwa babbar matsala ce ga kowa, ba wai manoma kaɗai ba.
“Wannan musiba ce da ya kamata kowa ya tashi tsaye ya roƙi Allah Ya kawo sauƙi,” in ji su.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Fari Kauran Namoda Roƙon Ruwa Zamfara
এছাড়াও পড়ুন:
Mutuwar majinyata: Asibitin Aminu Kano na roƙon KEDCO ya dawo da wutar lantarki
Asibitin Koyarwa na Aminu Kano (AKTH) ya roƙi Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na KEDCO ya gaggauta dawo masa da wuta bayan rasuwar wasu marasa lafiya da ke samun kulawa ta ceton rayuwada na’ura.
Wata sanarwa da kakakin asibitin, Hauwa Inuwa Dutse ta fitar ta nuna takaici bisa rasuwar marasa lafiyan, tana mai cewa mace-macen waɗanda za a iya kauce wa ne idan akwai tsayayyiyar wutar lantarki.
Ta bayyana cewa Asibitin yana AKTH yakan biya kuɗin wuta akai-akai daga kuɗaɗen shigansa, kuma yana kashe kuɗaɗe wajen sanya mai a janareto domin amfani idan aka ɗauke wuta daga KEDCO.
Don haka, “Hukumar gudanarwar Asibitin AKTH na roƙon Kamfanin KEDCO da ya taimaka wa ayyukan asibitin ta hanyar dawo da wutar a yayin da muke ƙoƙarin biyan ragowar kuɗin wutar,” in ji sanarwar.
Ambaliya: An gano gawar ’yar shekara 3 da ruwa ya tafi da ita a Zariya Gwamnati ta gargaɗi jihohi 11 kan yiwuwar afkuwar ambaliya a wannan makonTa bayyana cewa a yayin da take ƙoƙarin biyan bashin da kamfanin ke bin sa, yana da muhimmanci a fahimci cewa yanke wutar lantarki daga muhimmiyar cibiyar lafiya babbar barazana ce ga majinyata da danginsu.