Yadda manoma suka yi addu’ar roƙon ruwa a Zamfara
Published: 19th, June 2025 GMT
Al’ummar garin Kaura Namoda da ke Jihar Zamfara, sun gudanar da sallar roƙon ruwa bayan da aka shafe kwanaki ba tare da an samu ruwan sama ba.
Mutane da dama sun fara nuna damuwa saboda har yanzu babu ruwa ba, duk da cewa an shiga lokacin damina tun da daɗewa.
NAJERIYA A YAU: Yadda Cutar Amosanin Jini Ta Hana Ni Cimma Buri Na Sojojin Nijeriya sun kashe gomman ’yan ta’adda a Tafkin ChadiWasu manoma da ke jiran ruwa domin su yi shuka sun ce har zuwa ranar Laraba sun fito domin roƙon Allah Ya saukar da ruwa.
Babban limamin garin Kaura, Malam Badamasi, ne ya jagoranci sallar.
Ya ce sun ga dacewar yin wannan addu’a ne domin tun mako biyu da suka wuce ba su samu ruwa ba a garin.
Sheikh Malam Muhammad ya yi wa jama’a wa’azi mai ratsa zuciya, inda ya tunatar da su muhimmancin komawa ga Allah da yawaita ibada a irin wannan lokaci na fari da rashin ruwa.
Daga cikin waɗanda suka halarci sallar akwai Abdul Hadi Ibrahim Mai Yadi da Kasimu Namadi.
Sun ce sun zo domin neman gafara daga Allah da fatan zai saukar da ruwa.
Sun bayyana damuwarsu da cewa mako biyu kenan ba a yi ruwa a yankinsu ba, kuma ruwan da ya zo a baya bai wadatar wajen yin shuka ba, sai kuma ya ɗauke gaba ɗaya.
Sun ce fari na ruwa babbar matsala ce ga kowa, ba wai manoma kaɗai ba.
“Wannan musiba ce da ya kamata kowa ya tashi tsaye ya roƙi Allah Ya kawo sauƙi,” in ji su.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Fari Kauran Namoda Roƙon Ruwa Zamfara
এছাড়াও পড়ুন:
Zargin Kisan Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini — Tinubu
Shugaba Bola Tinubu ya mayar wa da Shugaban Amurka, Donald Trump martani cewa Najeriya ba ta yadda da duk wani nau’in zarafin addini.
Tinubu, ya yi wannan bayani ne bayan Trump ya sake sanya Najeriya cikin jerin ƙasashen da ake kiran “Ƙasashen da ke da Babbar Matsala wajen ’Yancin Addini.”
PDP ta dakatar da Anyanwu da wasu ’yan tsagin Wike Sharrin son auren Mai Wushirya aka yi min — Mansura IsaTrump ya yi iƙirarin cewa Kiristoci a Najeriya na fuskantar barazana, amma ya sha alwashin cewa Amurka za ta kare su.
A cikin wani saƙo da ya wallafa a kafafen sada zumunta, Trump ya rubuta cewa: “Addinin Kirista yana fuskantar babbar barazana a Najeriya. Ana kashe dubban Kiristoci.”
A ranar Asabar, Tinubu ya mayar da martani ta kafar sada zumunta, inda ya ce Najeriya ƙasa ce mai dimokuraɗiyya wadda kundinta ya tabbatar da ’yancin yin addini.
“Najeriya tana da cikakken tanadi a kundinta da ya tabbatar da ’yancin yin addini,” in ji Tinubu.
“Tun daga shekarar 2023, gwamnatina na aiki tare da shugabannin Kiristoci da Musulmai don magance matsalolin tsaro da ke shafar jama’a daga kowane ɓangare da addini.”
Ya ƙara da cewa, kiran Najeriya ƙasa mai matsala wajen gudanar addini ba gaskiya ba ne.
“Za mu ci gaba da kare ’yancin kowane ɗan ƙasa na yin addininsa cikin walwala. Najeriya ba ta goyon bayan zaluncin addini ko kaɗan,” in ji Tinubu.
Ya kuma ce Najeriya za ta ci gaba da haɗa kai da Amurka da sauran ƙasashe domin inganta zaman lafiya da fahimtar juna tsakanin mabiya addinai daban-daban.