Yadda manoma suka yi addu’ar roƙon ruwa a Zamfara
Published: 19th, June 2025 GMT
Al’ummar garin Kaura Namoda da ke Jihar Zamfara, sun gudanar da sallar roƙon ruwa bayan da aka shafe kwanaki ba tare da an samu ruwan sama ba.
Mutane da dama sun fara nuna damuwa saboda har yanzu babu ruwa ba, duk da cewa an shiga lokacin damina tun da daɗewa.
NAJERIYA A YAU: Yadda Cutar Amosanin Jini Ta Hana Ni Cimma Buri Na Sojojin Nijeriya sun kashe gomman ’yan ta’adda a Tafkin ChadiWasu manoma da ke jiran ruwa domin su yi shuka sun ce har zuwa ranar Laraba sun fito domin roƙon Allah Ya saukar da ruwa.
Babban limamin garin Kaura, Malam Badamasi, ne ya jagoranci sallar.
Ya ce sun ga dacewar yin wannan addu’a ne domin tun mako biyu da suka wuce ba su samu ruwa ba a garin.
Sheikh Malam Muhammad ya yi wa jama’a wa’azi mai ratsa zuciya, inda ya tunatar da su muhimmancin komawa ga Allah da yawaita ibada a irin wannan lokaci na fari da rashin ruwa.
Daga cikin waɗanda suka halarci sallar akwai Abdul Hadi Ibrahim Mai Yadi da Kasimu Namadi.
Sun ce sun zo domin neman gafara daga Allah da fatan zai saukar da ruwa.
Sun bayyana damuwarsu da cewa mako biyu kenan ba a yi ruwa a yankinsu ba, kuma ruwan da ya zo a baya bai wadatar wajen yin shuka ba, sai kuma ya ɗauke gaba ɗaya.
Sun ce fari na ruwa babbar matsala ce ga kowa, ba wai manoma kaɗai ba.
“Wannan musiba ce da ya kamata kowa ya tashi tsaye ya roƙi Allah Ya kawo sauƙi,” in ji su.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Fari Kauran Namoda Roƙon Ruwa Zamfara
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu ya bayar umarnin binciken hare-haren Benuwe
Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya umarci jami’an tsaro da su yi bincike tare da gano waɗanda suka kai hari a Jihar Benuwe, inda aka kashe sama da mutum 100.
Harin ya faru ne a ƙauyen Yelwata da ke Ƙaramar Hukumar Guma a jihar.
Iran ta rataye mutumin da ta kama yana yi wa Isra’ila leƙen asiri KADSEMA da IOM sun fara tantance ɓarnar da ambaliya ta yi a KadunaBayan harin, matasa sun rufe hanyar Lafiya zuwa. Makurdi domin nuna ɓacin ransu.
Zanga-zangar ta ci gaba da gudana har zuwa safiyar ranar Lahadi a birnin Makurdi, babban birnin jihar.
Rundunar ‘yan sandan jihar ta yi amfani da barkonon tsohuwa domin tarwatsa masu zanga-zangar.
A daren ranar Lahadi, Shugaba Tinubu ya wallafa saƙo a a shafin sa na X, inda ya ce dole a kawo ƙarshen wannan kashe-kashe, kuma ya umarci jami’an tsaro su ɗauki mataki don kama duk masu hannu a rikicin.
Tinubu ya kuma buƙaci Gwamnan Jihar Benuwe, Hyacinth Alia, da ya jagoranci tattaunawa da yin sulhu tsakanin manoma da makiyaya domin wanzar da zaman lafiya.
Ya gargaɗi shugabannin siyasa da na al’umma da su guji furucin da ka iya haifar da tarzoma.
Ya ce lokaci ya yi da za a haɗa kai domin warware matsaloli da hanyar gaskiya, adalci da fahimta, domin a samu zaman lafiya a Jihar Benuwe.