Hukumar Zaɓen Neja ta sanar da ranar zaɓen ƙananan hukumomoni
Published: 6th, March 2025 GMT
Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta Jihar Neja ta sanya ranar 1 ga watan Nuwamba, 2025 domin gudanar da zaɓen ƙananan hukumomi.
Shugaban Hukumar Zaɓen, Mohammed Jibrin Iman ne ya bayyana haka a lokacin da yake ƙaddamar da jadawalin ayyukan gudanar da zaɓen ƙananan hukumomi na shekarar 2025 a hedikwatar hukumar da ke Minna, babban birnin jihar.
Imam ya ce an fara shirye-shiryen zaɓen ne daga ranar 6 ga watan Maris, 2025, yana mai cewa za a gudanar da zaɓen fidda gwani na jam’iyyu ne tsakanin ranakun 15 zuwa 24 ga Maris, 2025, yayin da za a tattara fom da kuma jerin sunayen ’yan takara za su gudana daga ranar 25 ga Maris zuwa 2 ga Afrilu, 2025.
Shugaban ya ce, za a maido da jerin sunayen ’yan takarar da aka tura musu daga ranar 3 zuwa 10 ga Afrilu yayin da za a wallafa bayanan ’yan takarar daga ranar 11 zuwa 18 ga Afrilu, 2025.
Ya ƙara da cewa an shirya tattara fom ɗin tsayawa takara a ranar 19 zuwa 26 ga Afrilu yayin da jam’iyyun siyasa za su gabatar da fom ɗin takara daga ranar 27 ga Afrilu zuwa 3 ga Mayu, 2025.
Ya ce, za a fara gangamin yaƙin neman zaɓen daga ranar 27 ga watan Mayu har zuwa ranar 31 ga Oktoba, 2025.
Imam ya tabbatar wa jam’iyyun siyasa matakin da za a yi na gudanar da zaɓuka cikin ’yanci, gaskiya da adalci bisa wasu dokoki da jagororin gudanar da zaɓukan kansiloli.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Siriya Da HKI Zasu Gudanar Da Taro A Baku
Ministocin harkokin wajen kasar Siriya da kuma na HKI zasu gudanar da taro a birnin Baku na kasar Azarbaijan a ranar Alhamis mai zuwa don tattauna maganar tsaro a kasar Siriya kamar yadda suka fada.
Shafin yanar gizo na labarai ArabNews na kasar Saudiya ya bayyana cewa Asaad Al-Shaibani ministan harkokin wajen kasar Siriya da kuma ministan ayyuka na musamman na HKI Ron Dermer sun gudanar da taro a birnin Paris na kasar faransa a cikinn yan kwanakin da suka gabata, a halin yanzu kuma zasu gudanar da taron a birnin Baku na kasar Azrbaijan a ranar Alhamis mai zuwa.
Labarin ya kara da cewa kafin haka dai Al-Shaibani ya ziyarci Moscow kamar yadda wata majiya wacce bata son a bayyana sunanta fadawa Arabnews.
Kafin haka dai muna iya cewa HKI tana yaki da kasar Siriya tun shekara 1948 wato a lokacinda turawan Ingila suka kafata., har zuwa watan decemban shekara ta 2024 a lokacinda kasashen yankin suka taimakawa kungiyar yan ta’adda ta HTS ta han kan kujerar shugaban kasar.
Sai dai masana da dama suna ganin da wuya a ce taron kasashen biyu bai shafi kasar Iran ba. Don idan batun kasar Siriya ce me ya hada siriya da Baku.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Girgizar Kasa Mai Karfi Ta Kada Yankin Kamtashatka Na Kasar Rasha July 30, 2025 Yahudawa ‘Yan Share Wuri Zauna Sun Kutsa Cikin Masallacin Kudus July 30, 2025 Kasashen Yankin Caribbean Suna Son Bunkasa Alakarsu Ta Kasuwanci Da Nahiyar Afirka July 30, 2025 Shugaban Kasar Ivory Coast Ya Bayyana Shirinsa Na Sake Tsayawa Takarar Shugabanci Karo Na Hudu July 30, 2025 Kasashen Iran Da Rasha Sun Tattauna Batun Hadin Gwiwar Kafofin Watsa Labarai A Tsakaninsu July 30, 2025 MDD Zata Aiwatar Da Hanyar Warware Rikicin Falasdinawa Da Yahudawan Sahayoniyya July 30, 2025 Birtaniya Ta Yi Barazanar Amincewa Da Kasar Falasdinu A Watan Satumba Idan Yanayin Gaza Bai Canza Ba July 30, 2025 Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Saman Lod Da Ke Jaffa Da Makami Mai Linzami July 30, 2025 Faransa Ta Bayyana Wuce Gona Da Irin ‘Yan Sahayoniyya Kan Falasdinawa Da Ayyukan Ta’addanci July 30, 2025 Jagora: Iran Ta Bayyana Karfinta Da Jajircewarta A Yakin Kwanaki 12 Ga Duniya July 29, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci