Rikicin Filato: An sake kashe mutum 17 a Mangu da Bokkos
Published: 20th, June 2025 GMT
Mahara sun sake kai hari tare da kashe akalla mutum 17 a kananan hukumomin Mangu da Bokkos na jihar Filato.
Rahotanni sun nuna an kai harin ne ranar Alhamis a kauyen Manja da ke masarautar Chakfem a Mangu da kuma kauyen Tangur da ke Bokkos.
Bayanai sun nuna maharan sun farmaki yankunan ne a lokuta daban-daban.
Yayin da aka kai harin Tangur wajen misalin karfe 9:00 na dare, shi kuma na Manja an kai shi ne tun da gefen almuru.
Majiyoyi daga yankunan sun ce maharan sun bude wuta suka karkashe mutanen kafin daga bisani su cika wandunansu da iska.
A cewar majiyoyin, an kashe mutum bakwai a Mangu, a Bokkos kuma mutum 10.
Sun kuma ce maharan, wadanda ke dauke da bindiga sun rika harbin kan mai uwa da wabi sannan suka rika haura gidajen mutane suna karkashe su.
Daraktan Al’adu na kungiyar Ci Gaban Mwaghavul, Shohotden Mathias Ibrahim, da kuma Daraktan da ke kula da sansanin ’yan gudun hijira na Mangu ne suka tabbatar da alkaluman mutuwar, inda suka ce yanzu haka ana zaman dardar a yankin.
Sai dai ya zuwa yanzu, shugabannin al’umma da kuma mazauna yankin ba su amsa sakon da wakiliyarmu ta tura musu na neman karinn bayani ba.
Kazalika, rundunar ’yan sandan jihar Filato ba ta magantu a kan hare-haren ba, sakamakon Kakakin runduna, Alfred Alabo, bai amsa kiran waya da sakon kar-ta-kwana da na Whatsapp din da wakiliyarmu ta tura masa ba, ya zuwa lokacin hada wannan rahoton.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: hari
এছাড়াও পড়ুন:
Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare
Gwamnatin jihar Borno na shirin sake tsugunar da ‘yan gudun hijira kusan 5,000 daga al’ummomin Bama su biyar kafin damina ta kare. Gwamna Babagana Umara Zulum ya bayyana haka a wata ziyarar ban girma da ya kai wa Shehun Bama, Dakta Umar Kyari Umar El-Kanemi a ranar Juma’a. Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM Gwamnatin Tarayya Za Ta Aiwatar da Shirin Daƙile Sulalewar Kuɗaɗen Haraji Al’ummomin da aka kudiri niyyar sake tsugunar da su sun hada da Goniri, Bula Kuriye, Mayanti, Abbaram da Darajamal. Zulum ya ce ana kafa matsugunan tanti na wucin gadi guda 1,000 a kowace al’umma, inda tuni aka kammala wacce ke Darajamal. “Mun himmatu wajen mayar da ‘yan gudun hijira zuwa gidajensu na asali, a yanzu haka, ana ci gaba da gudanar da ayyukan a Mayanti, Goniri, Bula Kuriye da kuma Abbaram. “An kammala Darajamal. Ana haka gololo a kewayen wadannan al’ummomi don inganta tsaro,” in ji Zulum.Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp