Aminiya:
2025-09-18@22:30:58 GMT

Rikicin Filato: An sake kashe mutum 17 a Mangu da Bokkos

Published: 20th, June 2025 GMT

Mahara sun sake kai hari tare da kashe akalla mutum 17 a kananan hukumomin Mangu da Bokkos na jihar Filato.

Rahotanni sun nuna an kai harin ne ranar Alhamis a kauyen Manja da ke masarautar Chakfem a Mangu da kuma kauyen Tangur da ke Bokkos.

Bayanai sun nuna maharan sun farmaki yankunan ne a lokuta daban-daban.

2027: ‘Sai bayan babban taron APC Tinubu zai bayyana wanda za su yi takara tare’ Za mu iya galaba kan Iran ko babu Amurka — Isra’ila

Yayin da aka kai harin Tangur wajen misalin karfe 9:00 na dare, shi kuma na Manja an kai shi ne tun da gefen almuru.

Majiyoyi daga yankunan sun ce maharan sun bude wuta suka karkashe mutanen kafin daga bisani su cika wandunansu da iska.

A cewar majiyoyin, an kashe mutum bakwai a Mangu, a Bokkos kuma mutum 10.

Sun kuma ce maharan, wadanda ke dauke da bindiga sun rika harbin kan mai uwa da wabi sannan suka rika haura gidajen mutane suna karkashe su.

Daraktan Al’adu na kungiyar Ci Gaban Mwaghavul, Shohotden Mathias Ibrahim, da kuma Daraktan da ke kula da sansanin ’yan gudun hijira na Mangu ne suka tabbatar da alkaluman mutuwar, inda suka ce yanzu haka ana zaman dardar a yankin.

Sai dai ya zuwa yanzu, shugabannin al’umma da kuma mazauna yankin ba su amsa sakon da wakiliyarmu ta tura musu na neman karinn bayani ba.

Kazalika, rundunar ’yan sandan jihar Filato ba ta magantu a kan hare-haren ba, sakamakon Kakakin runduna, Alfred Alabo, bai amsa kiran waya da sakon kar-ta-kwana da na Whatsapp din da wakiliyarmu ta tura masa ba, ya zuwa lokacin hada wannan rahoton.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: hari

এছাড়াও পড়ুন:

Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

Duk da cewar an yi yarjejeniya tsakanin ɓangarorin biyu, rikici ya sake ɓarkewa bayan NUPENG ta ce Dangote bai cika alƙawari ba.

Amma matatar ta musanta zargin, inda ta bayyana cewa ma’aikatanta na da damar shiga ƙungiya idan sun so, amma ba dole ba ne.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato
  • ’Yan sanda sun kama mutum 9 kan yin garkuwa da kansu
  • An kashe ’yan ta’addan IPOB da yawa a Imo — ’Yan Sanda
  • Gobara ta kashe manyan jami’an hukumar FIRS 4 a Legas
  • ‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja
  • Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno
  • Kungiyar Kare Hakkokin Bil’Adama Ta Siriya Ta Bankado Karin Fararen Hula Da Aka Kashe A Rikicin Suweida
  • Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?
  • ’Yan sanda sun kama mutum 6 kan satar zinarin N109m a Kebbi
  • ’Yan ‘Mafiya’ na ƙoƙarin kashe matatar man fetur da na gina —Ɗangote