Aminiya:
2025-06-20@14:20:43 GMT

Rikicin Filato: An sake kashe mutum 17 a Mangu da Bokkos

Published: 20th, June 2025 GMT

Mahara sun sake kai hari tare da kashe akalla mutum 17 a kananan hukumomin Mangu da Bokkos na jihar Filato.

Rahotanni sun nuna an kai harin ne ranar Alhamis a kauyen Manja da ke masarautar Chakfem a Mangu da kuma kauyen Tangur da ke Bokkos.

Bayanai sun nuna maharan sun farmaki yankunan ne a lokuta daban-daban.

2027: ‘Sai bayan babban taron APC Tinubu zai bayyana wanda za su yi takara tare’ Za mu iya galaba kan Iran ko babu Amurka — Isra’ila

Yayin da aka kai harin Tangur wajen misalin karfe 9:00 na dare, shi kuma na Manja an kai shi ne tun da gefen almuru.

Majiyoyi daga yankunan sun ce maharan sun bude wuta suka karkashe mutanen kafin daga bisani su cika wandunansu da iska.

A cewar majiyoyin, an kashe mutum bakwai a Mangu, a Bokkos kuma mutum 10.

Sun kuma ce maharan, wadanda ke dauke da bindiga sun rika harbin kan mai uwa da wabi sannan suka rika haura gidajen mutane suna karkashe su.

Daraktan Al’adu na kungiyar Ci Gaban Mwaghavul, Shohotden Mathias Ibrahim, da kuma Daraktan da ke kula da sansanin ’yan gudun hijira na Mangu ne suka tabbatar da alkaluman mutuwar, inda suka ce yanzu haka ana zaman dardar a yankin.

Sai dai ya zuwa yanzu, shugabannin al’umma da kuma mazauna yankin ba su amsa sakon da wakiliyarmu ta tura musu na neman karinn bayani ba.

Kazalika, rundunar ’yan sandan jihar Filato ba ta magantu a kan hare-haren ba, sakamakon Kakakin runduna, Alfred Alabo, bai amsa kiran waya da sakon kar-ta-kwana da na Whatsapp din da wakiliyarmu ta tura masa ba, ya zuwa lokacin hada wannan rahoton.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: hari

এছাড়াও পড়ুন:

EFCC Ta Kama Tsohon Kakakin Majalisar Filato Da Wasu ‘Yan Majalisa 14 Bisa Zargin Almundahana

Sauran sun hada da: Danjuma Azi, Fwangje Bala Ndat, Salome Tanimu Wanglet, Namba Rimuyat, Nimchak Rims, Ishaku Maren da Paul Datugun.

 

Kakakin hukumar ta EFCC, Dele Oyewale, wanda ya tabbatar da kamun, ya ce bincike ya nuna cewa tsaffin ‘yan majalisar sun shafe watanni shida ne kawai a kan karagar mulki, sannan gwamnatin jihar ta siya musu motocin alfarma.

 

 

Bincike ya kuma nuna cewa, motocin da aka ce kudinsu ya kai Naira biliyan 2.5. Bayan sun sauka akan mukaminsu, sun tafi da motocin kuma duk kokarin da aka yi na su dawo da su, lamarin ya ci tura.

 

Sai da gwamnatin jihar ta sake sayo wa ‘yan majalisar na yanzu motocin da kudinsu ya kai kimanin naira biliyan biyu.

 

Oyewale ya tabbatar da cewa nan ba da jimawa ba za a gurfanar da tsohon shugaban majalisar da sauran mambobin a kotu.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Filato, Mutane 15 Sun Mutu A Bokkos Da Mangu
  • An ɗaure mutum 7 kan yi wa ɗan sanda rauni a Kano
  • ’Yan bindiga sun kashe manoma 24 a Katsina
  • An Kashe Wasu ‘Yan Bindiga 12, An Kwato Makamai A Katsina
  • Wasu ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Gidan Sanata Natasha A Kogi
  • EFCC Ta Kama Tsohon Kakakin Majalisar Filato Da Wasu ‘Yan Majalisa 14 Bisa Zargin Almundahana
  • An Ɗaure Wani Mutum Wata 6 Kan Satar Takalma A Masallaci A Kaduna
  • Ambaliyar Mokwa – Har yanzu muna neman mutum 700 – Gwamnatin Neja
  • Rikicin ƙabilanci ya yi ajalin mutum 20 a Chadi