Aminiya:
2025-06-20@00:16:14 GMT

Hisbah ta lalata katan 243 na barasa da wasu kayan maye a Yobe

Published: 19th, June 2025 GMT

A ci gaba da ƙoƙarinta na tabbatar da kyawawan halaye da kuma samar da zaman lafiya a tsakanin al’umma, Hukumar Hisbah ta Jihar Yobe ta lalata katan 243 na barasa da galan 100 na barasa da aka haɗa a gida, da aka fi sani da sukudaye.

A wata sanarwa da jami’in yaɗa labarai na Hukumar, Adamu Muhammad ya sanya wa hannu, ta ce an lalata barasa a Damaturu, a wani mataki na aiwatar da dokar hana sha da kayan rarraba barasa a jihar.

Guguwar ruwan sama ta yi ɓarna a Kwalejin Kimiyya da Fasaha a Kogi Tinubu na ƙaddamar da wasu ayyuka a Jihar Kaduna

Shugaban Hukumar Hisbah na jihar, Dokta Yahuza Hamza Abubakar ne ya bayyana cewa aikin ya yi dai-dai da aikin hukumar na aiwatar da dokokin da ke inganta nagarta da kare martabar al’umma.

“Shaye-shaye na haifar da barazana ga lafiyar jama’a da zamantakewar jama’a wadda akan hakan ne aka haramta sha da rarraba ta a cikin jihar a ƙarƙashin dokokin da ake da su,” in ji shi.

Dokta Yahuza ya nanata ƙudurin hukumar na samar da zaman lafiya, adalci da gyara al’umma, inda ya ce Hisbah ta kuma sasanta tare da warware wasu matsaloli a ayyukan da suka yi a baya-bayan nan.

Ya buƙaci mazauna jihar da su ci gaba da marawa ƙoƙarin hukumar baya wajen tabbatar da kyawawan ɗabi’u da mutuncin jama’a.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu Ya Kai Ziyara Benuwe Sakamakon Kisan Kiyashi Da Aka Yi Wa Jama’a

Don girmama ziyarar shugaban ƙasa, gwamnatin jihar ta ayyana ranar Laraba a matsayin hutu domin bai wa mazauna yankunan damar halarta taron da kuma bin diddigin abubuwan da suka shafi ziyarar.

Wannan ita ce ziyarar farko da Tinubu ya kai Jihar Benuwe tun bayan da rikicin ya ƙara tsananta.

Jama’a da dama na kallon wannan ziyara a matsayin gwada gwamnati kan yadda za ta shawo kan matsalolin tsaro, musamman a jihohin da ke fama da hare-haren ‘yan bindiga, rikicin makiyaya da na ƙabilanci.

Kisan da aka yi a Yelwata, wanda shi ne na baya-bayan nan cikin jerin hare-haren, ya janyo suka damuwa a faɗin ƙasar tare da ƙara matsin lamba ga shugaban ƙasa da ya ɗauki matakin gaggawa don tabbatar da adalci da tsaron rayukan jama’a.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu na ƙaddamar da wasu ayyuka a Jihar Kaduna
  • Za a dawo da dukkan Alhazai gida ranar 28 ga Yuni – NAHCON
  • EFCC Ta Kama Tsohon Kakakin Majalisar Filato Da Wasu ‘Yan Majalisa 14 Bisa Zargin Almundahana
  • Mun shirya yin sulhu da ’yan bindiga — Gwamnatin Sakkwato
  • Tinubu Ya Kai Ziyara Benuwe Sakamakon Kisan Kiyashi Da Aka Yi Wa Jama’a
  • Buni ya bai wa manoma 1,000 tallafin aikin gona
  • An Gudanar Da Bikin Mu’amalar Jama’a Da Al’adu A Tsakanin Sin Da Tsakiyar Asiya A Astana
  • Iran ta kai hari hedikwatar hukumar leƙen asirin Isra’ila
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Cin Ganyayyaki Ke Yi Wa ‘Yan Najeriya Wahala