Nijeriya za ta fara fitar ta tataccen mai zuwa Asia — Matatar Dangote
Published: 18th, June 2025 GMT
A karon farko Nijeriya za ta fara fitar da tataccen man fetur zuwa nahiyyar Asia kamar yadda wata majiya daga Matatar Dangote ta sanar.
Majiyar ta ce wani jirgin ruwan dako mai ɗauke da tan 90,000 na man fetur zai yi jigilar daga Matatar Dangote da ke Nijeriya zuwa nahiyar Asia.
HOTUNA: Yadda Tinubu ya ziyarci waɗanda suka jikkata a harin Benuwe Hare-haren Benuwe: Tinubu ya ziyarci waɗanda suka jikkata a asibitiKamfanin Dillancin Labarai na Reuters ya ambato majiyar wadda ta buƙaci a sakaya sunanta tana cewa “yanzu jirgin ruwan Mercuria zai tafi Asia a ranar 22 ga Yuni.
“Muna sayar da kayanmu ne ga waɗanda suka yarda su ba mu farashi mafi yawa. Mai saye na da haƙƙin kai wa duk inda yake so,” in ji kakakin matatar mai ta Dangote.
Darektan a kamfanin Horizon Engage, Clementine Wallop, ya alaƙanta fitar da man da matatar za ta yi a matsayin wani gagarumin tasiri na zama abar dogaro wajen samar da mai a faɗin duniya.
Tun bayan da matatar mai karfin tace ganga 650,000 na ɗanyen mai a kowacce rana ta fara fitar da fetur a bara, jiragen ruwan da ke ɗaukar man zuwa Yammacin Afirka ne.
Matatar man ta dala biliyan 20 da mai kuɗin Afirka Aliko Dangote ya samar a birnin Legas, ta fara aiki a watan Janairun shekarar da ta gabata.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Matatar Dangote Nahiyar Asiya
এছাড়াও পড়ুন:
Hauhawar Farashi Ya Sauka Zuwa Kashi 22.9 A Watan Mayun 2025
Wannan ya nuna ragin hauhawar farashi a faɗin ƙasar nan.
Masana na ganin wannan ragi a matsayin alamar ci gaba ga tattalin arziƙi, sai dai har yanzu ‘yan Nijeriya da dama na fama da tsadar rayuwa, musamman wajen samun kayan abinci da wasu muhimman abubuwan buƙara na yau da kullum.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp