Aminiya:
2025-06-15@19:22:20 GMT

An kama ’yan Pakistan biyu da laifin yin garkuwa a Legas

Published: 6th, March 2025 GMT

Jami’an hukumar ’yan sandan Jihar Legas sun kama wasu ’yan ƙasar Pakistan guda biyu, Roman Gull mai shekara 19 da kuma Aftab Ahmad mai shekara 28 bisa zargin jagorantar wata ƙungiyar masu garkuwa da mutane a jihar.

Jaridar PUNCH ta ruwaito cewa waɗanda ake zargin tare da wasu mutum biyar ne, sun kama wani ɗan ƙasar Pakistan mai shekara 48 ɗan asalin Jihar Kano da tayin aikin bogi a matsayin mai dafa abinci kafin su yi awon gaba da shi tare da neman kuɗin fansa miliyan 50 daga ma’aikacin nasa.

Hukumar Zaɓen Neja ta sanar da ranar zaɓen ƙananan hukumomoni Sheikh Sa’idu Hassan Jingir ya rasu

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sandan jihar, Benjamin Hundeyin ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a ranar Alhamis, inda ya ce jami’an sashin Ikeja sun kai ɗaukin gaggawa inda suka yi nasarar ceto wanda abin ya shafa.

Sai dai wasu ’yan ƙungiyar sun yi nasarar tserewa.

“An samu kiran gaggawa a cibiyar ofishin Ikeja na rundunar ’yan sandan Jihar Legas a ranar Laraba, 5 ga Maris, 2025, game da sace wani ɗan Pakistan mai shekara 48 a Ikeja.

Hundeyin ya ce, “An tura tawagar da ke yaƙi da masu aikata laifuka cikin gaggawa, lamarin da ya kai ga ceto wanda aka kashe tare da kama biyu daga cikin waɗanda suka yi garkuwa da shi, Roman Gull da Aftab Ahmad, ‘yan ƙasar Pakistan, yayin da wasu biyar suka tsere.”

Binciken farko ya nuna cewa waɗanda aka kama tare da abokan aikinsu sun yaudari wanda aka azabtar zuwa Legas ta hanyar yi masa alƙawarin aiki a matsayin ma’aikaci mai dafa abinci.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda garkuwa da mutane mai shekara

এছাড়াও পড়ুন:

Wakilin Sin: Matakin Amurka Game Da Harajin Kwastam Bai Yi La’akari Da Rarar Cinikayyar Hidimomi Ba

Kungiyar cinikayya ta duniya wato WTO, ta gudanar da taron shekara-shekara na biyu, na hukumar zartaswar cinikayyar hidimomi a birnin Geneva dake kasar Switzerland a jiya Juma’a, inda bangaren Sin ya yi nuni da cewa, matakin Amurka game da harajin kwastam na tattare da rashin fahimta da rashin gaskiya a wasu fannoni, don haka ya bukaci bangaren Amurka da ta bi ka’idojin kungiyar WTO, da daidaita matsaloli ta hanyar yin hadin gwiwa a tsakanin bangarori daban daban, da dakatar da daukar matakai daga bangare daya, don tabbatar da tsarin ciniki na duniya tare da bangarori daban daban. (Zainab Zhang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An samu gobara a wasu matatun mai guda biyu na Iran bayan harin da Isra’ila ta kai
  • Wutar lantarki ta kashe mutum 5, ta jikkata 13 a Gombe
  • Sojoji Sun kama ɗan China da wasu 4 kan zargin safarar makamai a Borno da Yobe
  • Wakilin Sin: Matakin Amurka Game Da Harajin Kwastam Bai Yi La’akari Da Rarar Cinikayyar Hidimomi Ba
  •   Iran  Kakkabo Wani Jirgin Yakin HKI Samfurin F-35  Karo Na 3 Tare Da Kama Matukinsa
  • Dimokuradiyya A Shekara 26: Ba Yabo Ba Fallasa
  • Dakarun Juyin Juya Halin Musulunci Na Iran Sun Kakkabo Jiragen Yakin Isra’ila Biyu Kirar F-35
  • An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasu
  • An kama ’yar Najeriya da laifin safarar ɗalibai 15 a Australia
  • Ƴansanda Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 2, Sun Ceto Mutane 11 A Delta Da Katsina