An garzaya da ’yan Isra’ila 154 asibiti bayan harin Iran
Published: 17th, June 2025 GMT
Isra’ila ta tabbatar cewa an garzaya da ’yan ƙasarta aƙalla 154 asibiti bayan sabbin hare-haren ramuwar gayya da Iran ta kawo mata.
Ma’aikatar lafiyar Isra’ila ta ce aƙalla mutum huɗu daga cikin waɗanda aka kai asibitin suna cikin halin rai-kwakwai-mutu-kwakwai, wasu biyar kuma na samun kulawa ta musamman saboda tsananin tashin hankali.
Alkaluman da ma’aikatar ta fitar sun nuna cewa mutum 130 daga cikin majinyatan sun samu raunuka marasa tsanani a sakamakon hare-haren.
Wannnan na zuwa ne a yayin da Iran ta ci gaba luguden rokoki a matsayin ramuwar gayya a sassan Isra’ila a a ranar Talata.
Isra’ila ta ce Iran ta lashe mata mutane akalla 24.
A ɗaya ɓangaren kuma Iran cewa harin tsokana da Isra’ila ta kai mata ya yi ajalin kimanin mutum 224.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: hare hare Iran Isra ila Ramuwar Gayya Isra ila ta
এছাড়াও পড়ুন:
Tankokin Isra’ila sun kashe mutum 51 a wurin karbar abinci a Gaza
Tankokin yaƙin Isra’ila sun i kashe kimanin mutun 51 a yankin Khan Younis da ke Zirin Gaza, a yayin da mutanen suke tsaka da karbar abincin tallafi.
Jami’ain lafiya sun sun ce mutum 51 sun mutu, wasu 200 sun samu raunuka — 20 daga cikinsu suna cikin halin rai-kwakwai-mutu-kwakwai — bayan harin.
Sun bayyana harin a matsayin daya daga cikin mafiya muni da sojojin Isra’ila suka kai a baya-bayan nan a yayain da Falasdinawa ke kokarin samun abinci domin su rayu.
Bidiyon lamarin da suka karade kafofin sada zumunta sun nuna wasu gomman gawarwaki da ake zargin tankokin yakin Isra’ila sun mutsuttsuke a kan titi a Khan Younis.
Shaidu sun bayyana cewa sai da sojojin Isra’ilan suka sa mutanen suka taro a wuri guda sa’annan tankokin suka bude musu wuta.
Tankokin sun bude wuta ne a daidai lokacin da suke kokarin karbar tallafin abinci daga wata babbar motar kungiyar agaji.
Rundunar sojin Isra’ila ta tabbatar da aukuwar harin na ranar Litinin, wanda ta ce tana gudanar da bincike a kai.