Aminiya:
2025-06-17@18:10:46 GMT

An garzaya da ’yan Isra’ila 154 asibiti bayan harin Iran

Published: 17th, June 2025 GMT

Isra’ila ta tabbatar cewa an garzaya da ’yan ƙasarta aƙalla 154 asibiti bayan sabbin hare-haren ramuwar gayya da Iran ta kawo mata.

Ma’aikatar lafiyar Isra’ila ta ce aƙalla mutum huɗu daga cikin waɗanda aka kai asibitin suna cikin halin rai-kwakwai-mutu-kwakwai, wasu biyar kuma na samun kulawa ta musamman saboda tsananin tashin hankali.

Alkaluman da ma’aikatar ta fitar sun nuna cewa mutum 130 daga cikin majinyatan sun samu raunuka marasa tsanani a sakamakon hare-haren.

Wannnan na zuwa ne a yayin da Iran ta ci gaba luguden rokoki a matsayin ramuwar gayya a sassan Isra’ila a a ranar Talata.

Isra’ila ta ce Iran ta lashe mata mutane akalla 24.

A ɗaya ɓangaren kuma Iran cewa harin tsokana da Isra’ila ta kai mata ya yi ajalin kimanin mutum 224.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: hare hare Iran Isra ila Ramuwar Gayya Isra ila ta

এছাড়াও পড়ুন:

Tankokin Isra’ila sun kashe mutum 51 a wurin karbar abinci a Gaza

Tankokin yaƙin Isra’ila sun i kashe kimanin mutun 51 a yankin Khan Younis da ke Zirin Gaza, a yayin da mutanen suke tsaka da karbar abincin tallafi.

Jami’ain lafiya sun sun ce mutum 51 sun mutu, wasu 200 sun samu raunuka — 20 daga cikinsu suna cikin halin rai-kwakwai-mutu-kwakwai — bayan harin.

Sun bayyana harin a matsayin daya daga cikin mafiya muni da sojojin Isra’ila suka kai a baya-bayan nan a yayain da Falasdinawa ke kokarin samun abinci domin su rayu.

Bidiyon lamarin da suka karade kafofin sada zumunta sun nuna wasu gomman gawarwaki da ake zargin tankokin yakin Isra’ila sun mutsuttsuke a kan titi a Khan Younis.

Shaidu sun bayyana cewa sai da sojojin Isra’ilan suka sa mutanen suka taro a wuri guda sa’annan tankokin suka bude musu wuta.

Tankokin sun bude wuta ne a daidai lokacin da suke kokarin karbar tallafin abinci daga wata babbar motar kungiyar agaji.

Rundunar sojin Isra’ila ta tabbatar da aukuwar harin na ranar Litinin, wanda ta ce tana gudanar da bincike a kai.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran ta kai hari hedikwatar hukumar leƙen asirin Isra’ila
  • Tankokin Isra’ila sun kashe mutum 51 a wurin karbar abinci a Gaza
  • Matatar man Isra’ila ta daina aiki bayan sabon harin Iran
  • Sabon harin Iran ya hallaka mana mutum 8 – Isra’ila
  • Kungiyar Abokan Yarjejeniyar M.D.D Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ke Kai Wa Kan Iran
  • Dalilin da muka soke tattaunawar nukiliya da Amurka — Iran
  • Martanin sojojin Iran ga Isra’ila zai zama mafi muni idan aka ci gaba da kai hari (Pezeshkian)
  • An samu gobara a wasu matatun mai guda biyu na Iran bayan harin da Isra’ila ta kai
  • Gwamnatin Najeriya Ta Yi Allawadai Da Harin Da “Isra’ila” Ta Kawo Wa Iran