Ambaliyar Mokwa – Har yanzu muna neman mutum 700 – Gwamnatin Neja
Published: 18th, June 2025 GMT
Gwamnatin jihar Neja ta ce har yanzu akwai sama da mutum 700 da suka bace ba gan su ba tun bayan mummunar ambaliyar ruwan da aka yi a karamar hukumar Mokwa da ke jihar.
Gwamnan jihar, Mohammed Umar Bago ne ya bayyana hakan lokacin da ya karbi babban dogarin tsohon Shugaban Kasa marigayi Janar Sani Abacha, Manjo Hamza Al-Mustapha yayin ziyarar jaje kan ambaliyar a Minna ranar Talata.
Gwamnan, wanda mataimakinsa, Yakubu Garba ya wakilta ya kuma ce akalla mutum 207 ne aka tabbatar da mutuwarsu sannan gidaje sama da 3,000 ne suka rushe.
DAGA LARABA: Ko Kare Kai Daga Harin ‘Yan Ta’adda Zai Kawo Karshen Matsalar Tsaro? Jirgin alhazai ya yi saukar gaggawa kan barazanar harin bom“Sama da mutum 700 ne suka bace kuma ba a san inda suke ba. Wannan ambaliyar ta jawo mana babbar asara,” in ji shi.
Ya kuma yaba wa hukumomi da kamfanoni da ma daidaikun jama’a da suka ba da tallafi, inda ya ce iftila’in annoba ce ta kasa baki daya.
Gwamnan ya kuma ce yanzu haka gwamnatin na dakon sakamakon binciken hukumomi kan musabbabin ambaliyar da hanyoyin kauce mata a nan gaba.
Tun da farko, Al-Mustapha ya ce ya je jihar ne domin jajanta mata kan mummunar ambaliyar ta Mokwa
“Za mu gana da masu rike da sarautun gargajiya da musamman Ciyaman din karamar hukumar ta Mokwa domin mu yi musu addu’ar kare faruwar hakan a nan gaba,” in ji shi.
Ya kuma ce tawagar jajen tasu ta kunshi muhimman mutane daga sassa daban-daban na kasar nan domin jajantawa da bayar da tallafi ga gwamnati da yankunan da ta shafa.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Sabon harin Iran ya hallaka mana mutum 8 – Isra’ila
Isra’ila ta ce mutum takwas sun mutu a daren ranar Litinin sakamakon sabon harin da Iran ta kai a biranen Tel Aviv da Haifa da wasu sassa na ƙasar.
Wannan na zuwa ne a matsayin ci gaba daga jerin hare-hare da Iran ke kai wa tun bayan da Isra’ila ta fara kai mata hari makonnin da suka wuce.
NAJERIYA A YAU: Dalilan Durƙushewar Sababbin Sana’o’i Tun Ba A Je Ko’ina Ba Iran ta kai sabbin hare-hare birnin Tel Aviv da HaifaYanzu haka, adadin mutanen da hare-haren Iran suka kashe a Isra’ila ya kai 24, yayin da mutane sa.a da 300 ke kwance a asibitoci saboda raunuka.
Isra’ila ta ce a martaninta, jiragen yaƙin ƙasar sun kai hari a birnin Tehran, babban birnin Iran, inda suka lalata wata hedikwatar dakarun juyin juya hali.
Haka kuma sun kai farmaki a wasu cibiyoyi da Iran ke adana makamai a tsakiyar ƙasar.
An fara wannan rikici ne bayan da Isra’ila ta kai hari da asubahin ranar Juma’a a Iran.
Iran ta ce a wannan harin, mutane sama da 200 ne suka mutu.
Wannan hari ya fusata gwamnatin Iran, inda ta fara mayar da martani da hare-hare a Isra’ila.
A baya ma, ana zargin Isra’ila da kai hare-hare da dama a Iran, musamman kan dakarun da ta ke zargi da taimaka wa ƙungiyoyin da ke barazana gare ta, kamar Hezbollah da Hamas.
Rikicin ya ci gaba da tsananta, yayin da kowane ɓangare ke kai farmaki ga ɗaya, al’ummar ƙasashen biyu na ci gaba da jikkata da mutuwa.