Ambaliyar Mokwa – Har yanzu muna neman mutum 700 – Gwamnatin Neja
Published: 18th, June 2025 GMT
Gwamnatin jihar Neja ta ce har yanzu akwai sama da mutum 700 da suka bace ba gan su ba tun bayan mummunar ambaliyar ruwan da aka yi a karamar hukumar Mokwa da ke jihar.
Gwamnan jihar, Mohammed Umar Bago ne ya bayyana hakan lokacin da ya karbi babban dogarin tsohon Shugaban Kasa marigayi Janar Sani Abacha, Manjo Hamza Al-Mustapha yayin ziyarar jaje kan ambaliyar a Minna ranar Talata.
Gwamnan, wanda mataimakinsa, Yakubu Garba ya wakilta ya kuma ce akalla mutum 207 ne aka tabbatar da mutuwarsu sannan gidaje sama da 3,000 ne suka rushe.
DAGA LARABA: Ko Kare Kai Daga Harin ‘Yan Ta’adda Zai Kawo Karshen Matsalar Tsaro? Jirgin alhazai ya yi saukar gaggawa kan barazanar harin bom“Sama da mutum 700 ne suka bace kuma ba a san inda suke ba. Wannan ambaliyar ta jawo mana babbar asara,” in ji shi.
Ya kuma yaba wa hukumomi da kamfanoni da ma daidaikun jama’a da suka ba da tallafi, inda ya ce iftila’in annoba ce ta kasa baki daya.
Gwamnan ya kuma ce yanzu haka gwamnatin na dakon sakamakon binciken hukumomi kan musabbabin ambaliyar da hanyoyin kauce mata a nan gaba.
Tun da farko, Al-Mustapha ya ce ya je jihar ne domin jajanta mata kan mummunar ambaliyar ta Mokwa
“Za mu gana da masu rike da sarautun gargajiya da musamman Ciyaman din karamar hukumar ta Mokwa domin mu yi musu addu’ar kare faruwar hakan a nan gaba,” in ji shi.
Ya kuma ce tawagar jajen tasu ta kunshi muhimman mutane daga sassa daban-daban na kasar nan domin jajantawa da bayar da tallafi ga gwamnati da yankunan da ta shafa.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Kwara Ta Kwashe Mabarata Daga Titunan Jihar Su 94
Gwamnatin jihar Kwara ta kori mabarata 94 daga titunan Ilorin, domin tantancewa, gurfanar da su da kuma mayar da su gida.
Da take magana da ‘yan jarida yayin aikin, kwamishiniyar jin dadin jama’a da ci gaban jihar Dr Mariam Nnafatima Imam ta ce wadanda aka kama domin dawo da su sun hada da mata 43 da maza 51.
Ta ce ma’aikatar ta yi aikin dawo da mabaratan domin an haramta barace-barace a jihar Kwara.
Imam ya godewa gwamnan jihar bisa kokarin da yake yi na ganin jihar ta kawar da barace-barace a kan tituna da sauran matsalolin zamantakewa .
Kwamishinan ta ce a ko da yaushe gwamnatin jihar tana tuntubar gwamnatocin jihohin masu bara a tituna kafin a mayar da su jihohinsu.
A nasa jawabin, mataimaki na musamman ga gwamnan jihar Kwara kan sha da fataucin miyagun kwayoyi, Haliru Mikail ya ce galibin mutanen da ke bayyana kansu a matsayin mabarata suna safarar kwayoyi.
Ya ce aikin dakile barace-barace a kan tituna zai ci gaba da kasancewa domin tabbatar da zaman lafiya a tsakanin al’umma.
A nasa bangaren, shugaban sashin da ba na kariya ba, rundunar ‘yan sandan Najeriya reshen jihar Kwara Mista Adebayo Okunola ya bayyana cewa, an gudanar da aikin ne domin tsaftace jihar daga matsalolin zamantakewa yayin da wadanda aka kama tare da gurfanar da su a gaban kotun da ta dace za a hukunta su daidai da dokar jihar ta 2019.
Ya yi nuni da cewa hukumar da ke aikin za ta tabbatar da hukunta wadanda aka kama.
An gudanar da aikin ne a wasu yankuna da aka zaba a cikin birnin Ilorin da suka hada da Geri Alimi, Junction Tanke, Garage Offa, Garage Tipper da Zango, da dai sauransu.
COV/ALI MUHAMMAD RABIU