Aminiya:
2025-08-02@00:03:57 GMT

Amurka na iya kashe jagoran addini na Iran don mun san inda yake — Trump

Published: 17th, June 2025 GMT

Shugaban Amurka Donald Trump ya bayyana cewa ya san inda jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei yake “boye”, kuma ya yi gargadi cewa Washington na iya halaka shi, amma za su dakata a halin yanzu.

Wannan na zuwa ne yayin da Trump din ya gargadi Iran kan da kada ta kai harin makamai masu linzami kan fararen hula ko kuma sojojin Amurka, yana mai cewa hakurinsu na karewa.

Iran ta kai hari hedikwatar hukumar leƙen asirin Isra’ila Rikicin ƙabilanci ya yi ajalin mutum 20 a Chadi

A wani sakon da ya wallafa a shafinsa na Truth mintuna kadan bayan wannan sako, Trump ya rubuta cewar Iran din ta mika wuya ba tare da wani sharadi ba kawai.

Rahotanni a bayan nan sun ce Trump ya ƙi amincewa da shirin Isra’ila na kashe jagoran Iran, Ayatollah Ali Khamenei, kamar yadda majiyoyi uku suka shaida wa kafar yaɗa labarai ta CBS News.

Bayanan sun ce Shugaba Trump ya shaida wa Firaiministan Isra’ila Benjamin Netanyahu cewa kashe Khamenie “ba shawara ce mai kyau ba.”

Tattaunawar ta faru ne bayan harin da Isra’ila ta ƙaddamar kan Iran a ranar Juma’a.

A lokacin wata tattaunawa da kafar yaɗa labarai ta Fox News, Netanyahu bai fayyace kai-tsaye ko Trump ya ƙi amincewa da shawarar kashe Ayatollah ba, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ruwaito.

“Akwai rahotannin da dama kan tattaunawar da ake cewa an yi amma kuma ba gaskiya ba ne, ba zan shiga cikin irin wannan maganar ba,” in ji Firaiminstan Isra’ila.

Tun tsawon kwanaki biyar, Isra’ila ke kai hare-hare a cikin Iran, da suka shafi wuraren nukiliya da manyan kwamandojin soji da masana kimiyya da cibiyoyin tsaro da birane da ma cibiyoyin mai da iskar gas.

Iran dai ta mayar da martani da makamai masu linzami gami da jirage masu sarrafa kansu a kan Isra’ila, lamarin da ke kara fargabar cewa Amurka za ta iya shiga cikin rikicin kai tsaye, wanda kuma zai iya haifar da sabon babi mai hadari a rikicin.

A gefe guda kuma, babban hafsan tsaron Iran ya yi gargadi ga mazauna Isra’ila “musamman ma na biranen Tel Aviv da Haifa da su gaggauta barin wurarensu don tsira da rayukansu.

Janar Abdolrahim Mousavi, ya ce ayyukan da aka gudanar zuwa yanzu sun kasance gargadi ne kan abin da ke tafe, kuma za a gudanar da wani aiki na ladabtarwa nan ba da jimawa ba daga Iran.

Koda yake hare-haren Iran sun kashe akalla Isra’ilawa 24 tun a ranar Juma’a, galibin makaman Iran din dai Isra’ila ta dakatar da su ta hanyar tsarin kariyarta ta sama.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ayatollah Ali Khamenei Benjamin Netanyahu Iran Isra ila

এছাড়াও পড়ুন:

Kasar Iran Ta Bayyana Gushewar Hasashen Raunin Karfin Sojinta Kuma Ba Zai Dawo Ba

Kakakin dakarun kare juyin juya halin Musulunci na Iran “IRGC” ya bayyana cewa: Hasashen Raunin Iran ya gushe, kuma ba zai sake dawowa ba

Kakakin dakarun kare juyin juya halin Musulunci na Iran Birgediya Janar Ali Mohammad Na’eini ya jaddada cewa: Ra’ayin cewa Iran mai rauni ce ya raguje kwata-kwata, yana mai jaddada cewa; Yakin kwanaki 12 na baya-bayan nan ya fallasa gazawar makiya wajen karya manufofin Jamhuriyar Musulunci ta Iran, sannan kuma ya nuna cewa duk wani sabon harin wuce gona da iri zai fuskanci martani mai tsanani da gauni da zai wurga makiya cikin mummunar nadama.

Hakan ya zo ne a jawabin da Birgediya Janar Na’eini ya gabatar a jiya Laraba a wajen bikin tunawa da shahidi Ramadan Ali Jobadari da shahidan yakin baya-bayan nan. Ya kara da cewa: “Babban bangare na yakin kwanaki goma sha biyu ya kasance yakin kafar watsa labarai da na kwakwalwa da kuma fahimtar hakikanin juna,” ya kara da cewa, “Sun samu gagarumar nasara a fagen yada labarai a lokacin yakin da aka yi a baya-bayan nan. Da kafofin watsa labaru ba su da tasiri, da makiya ba su kai hari kan kafofin watsa labaru da ‘yan jarida ba.

Ya bayyana cewa, “a cikin wannan yakin, makiya sun kai hare-hare kan manyan cibiyoyin kasa da suka hada da cibiyoyin kimiyya da na masana, kwamandojin soji, hedkwatar gudanarwa, cibiyoyin leken asiri da tsaro, da kuma kafofin watsa labarai a matsayin cibiyar tsara labarin.”

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Sojan Amurka Ya Bada Ruwayar Yadda Sojojin Sahayoniyya Suka Kashe Wani Yaro Balasdine July 31, 2025 Sojojin Yemen Sun Kai Zafafan Hare-Hare Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila Guda Uku   July 31, 2025 Qolibaf: Barin HKI Ta Yi Abinda Taga Dama Ne Yana Karfafa Mata Giwa July 30, 2025 Yunwa Ta Kashe Karin Falasdinawa 7 A Gaza July 30, 2025 Malta Zata Amince da Samuwar Falasdinu a Cikin Watan Satumba Mai Zuwa July 30, 2025 Amurka Ta Ce HKI Ba Zata Fice Daga Kasar Lebanon Ba Sai An Kwance Damarar Hizbullah July 30, 2025 Siriya Da HKI Zasu Gudanar Da Taro A Baku July 30, 2025  Girgizar Kasa Mai Karfi Ta Kada Yankin Kamtashatka Na Kasar Rasha July 30, 2025  Yahudawa ‘Yan Share Wuri Zauna Sun Kutsa Cikin Masallacin Kudus July 30, 2025 Kasashen Yankin Caribbean Suna Son Bunkasa Alakarsu Ta Kasuwanci Da Nahiyar Afirka July 30, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu
  • Limamin Sallar Juma’a Ya Ce; Iran Zata Mayar Da Isra’ila Kufai Idan Ta Sake Kai Hari Kan Kasarta
  • Iran ta yi watsi da zargin gwamnatocin turai na yunkurin kashe wasu mutane a kasashensu
  • Haaretz: Sojojin Isra’ila 7 ne suka kashe kansu a watan Yuli
  • Shekara 2 Ta Gwamnatin Tinubu: Gwamnonin Arewa Sun ƙaryata Zargin ACF Na Watsi ɗa Yankin
  • Amurka: “Afirka Ba Ta Cikin Jerin Fannoni Da Muka Ba Da Fifiko A Kai”
  • Kassim: Duk Wanda Yake Neman Hizbullah Ta Ajiye Makamanta Yana Yi Wa Isra’ila Aiki
  • ZAMFARA: APC Ta Bukaci Gwamnatin Tarayya Ta Kawo Dauki Don Matsalar Tsaro Na Kara Tsananta
  • Tawagar Iran Ta Fice A Taron Majalisun Dokokin Kasashen Duniya A Lokacin Jawabin Wakilin Isra’ila
  • Kasar Iran Ta Bayyana Gushewar Hasashen Raunin Karfin Sojinta Kuma Ba Zai Dawo Ba