Sojoji sun raunata shugaban ISWAP na Najeriya, Albarnawi
Published: 18th, June 2025 GMT
A ci gaba da yakin da suke yi da ’yan ta’adda, sojojin Najeriya sun samu nasarar jikkata jagoran kungiyar ISWAP, Abu Moussab Albarnawi a dajin Sambisa.
Bayanai sun nuna sojoji sun sami nasarar ce bayan wani gagarumin harin da suka kai ta sama a wani sabon sansani na ’yan ta’addan da ke dajin Baikee a yankin Sambisa a Jihar Borno.
Dakarun rundunar da ke karkashin Operation KALACHEN WUTA, wanda bangare ne na rundunar sojojin saman Najeriya da ke karkashin rundunar Operation Hadin Kai (OPHK) ne suka kai harin.
Litar fetur za ta iya komawa N1,000 a Najeriya saboda yakin Isra’ila-Iran – Masana Majalisa ta aike wa Tinubu kudurorin dokar haraji domin ya rattaba musu hannuMajiyoyin sojojin Najeriya da ke rundunar OPHK wanda Manjo Janar Abdulsalam Abubakar ke jagorantar ta ce an aiwatar da wannan aiki ne a dajin inda ’yan ta’addan suke ci gaba da taruwa a sabon sansanin da suka kafa tare da shirya kai hare-hare kan fararen hula da ke kusa, musamman garin Izge.
Majiyar ta ce wannan aikin da Manjo Janar Abdulsalam Abubakar, Kwamandan Rundunar hadin gwiwa ta Arewa maso Gabas a Operation Hadin ke jagoranta, da kuma kwamandan rundunar sojin sama, kwamanda UU Idris, suka shirya a ranar 13 ga watan Yuni 2025 a jere, yadda aka kai hare-hare da dama kan wuraren taruwar ’yan ta’addan, tare da lalata wasu manyan kadarori da kuma kashe manyan kwamandodi na kungiyar ta ISWAP
Kididdigar barnar da majiyoyi suka tabbatar an yi a harin ta tabbatar da cewa kungiyar ta yi mummunar asara.
Wasu majiyoyin leken asiri sun kara tabbatar da cewa fitaccen shugaban kungiyar ISWAP, Abu Moussab Albarnawi, ya samu munanan raunuka a fuskarsa yayin harin ta sama, duk da cewar har yanzu ba a tabbatar da matsayin raunin da ya ji ba.
Nasarar kawar da ’yan ta’addan da kuma wargaza yunkurinsu na sake haduwa ya rage musu karfin fada sannan ya jefa su cikin rudani.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Boko Haram ISWAP yan ta addan
এছাড়াও পড়ুন:
PDP ta mutu murus a Kano — Shugaban NNPP
Shugaban jam’iyyar NNPP na Jihar Kano, Hashim Sulaiman Dungurawa, ya ce farin jinin jam’iyyar adawa ta PDP ya dusashe a jihar.
Ya bayyana hakan ne a lokacin da yake mayar da martanin da wasu jam’iyyun adawa suka yi, wajen zargin gwamnatin jihar da rashin bayyana yadda ta ke kashe kuɗaɗen da aka ware wa ilimi, lafiya, da gine-gine.
Haɗarin tirela ya yi sanadin asarar awaki sama da 100 a Zariya Martani: Har yanzu muna ci gaba da yajin aiki — Ma’aikatan jinyaDungurawa, ya ce waɗannan zarge-zargen siyasa ce kawai, ba su da tushe ko makama.
Ya ce waɗanda ke sukar gwamnati su ne suka gaza lokacin da suka yi mulki a Kano.
“Da farko, muna gode musu da suka amince muna aiki. Amma muna tunatar da su cewa sun yi shekara takwas suna mulki amma ba su bar wani abin a-zo-a-gani ba,” in ji Dungurawa.
Ya zargi gwamnatocin baya da yin ayyukan da ba su da tasiri, ba tare da duba buƙatun al’umma ba.
“Misali duba gadar ƙasa da suka yi a Dangi. Ba ta da wani amfani. Babu cunkoso a wajen da zai sa a gina irin wannan. Kawai sun zuba kankare ne ba tare da wata manufa ba,” in ji shi.
Dungurawa, ya ce a ƙarƙashin Gwamna Abba Kabir Yusuf, gwamnatin NNPP ta mayar da hankali kan muhimman ayyuka kamar gyaran tituna da gina gadoji don sauƙaƙa zirga-zirga a jihar.
“Yanzu haka, ramuka ƙadan za ka ga ni a titunan Kano. Titunanmu sabbi ne, alamomin titi a bayyane suke, fitilun titi suna aiki.
“Wannan yana nuna cewa masu kishin jihar sun karɓi ragamar mulki,” in ji shi.
Ya kuma kare yadda gwamnati ke biyan fansho, inda ya bayyana cewa an riga an biya Naira biliyan 27 daga cikin Naira biliyan 48 da gwamnatin jihar ta gada a matsayin bashi.
“A cikin shekara biyu kacal, mun biya Naira biliyan 27 sannan an biya biliyan 22, kuma za a biya wata biliyan biyar a watan Disamba.
“Wannan ya nuna irin yadda muke tafiyar da gwamnati da gaskiya,” in ji shi.
Game da maganar da wasu ‘yan adawa ke yi cewa jam’iyyunsu na ƙara ƙarfi, Dungurawa ya yi watsi da hakan.
“Wasu daga cikinsu ko a gidajensu ba za a goyi bayansu ba. PDP ba ta da wani ƙarfi. A zahirin gaskiya, mutuwa ta ke ƙara yi. Shugabanninta ba su da haɗin kai kuma son kansa yake yi,” in ji Dungurawa.
Bayan taɓo batun haɗakar ADC, Dungurawa ya ce hakan na nuna rikicin da ke cikin PDP.
“Idan har ɗan takarar shugaban ƙasa na PDP yana shirin komawa wata jam’iyya, me hakan ke nunawa?
“Yana nuna cewa jam’iyyar ba ta da tsari ko jagoranci. ‘Yan siyasa masu kishin ƙasa sun riga sun bar jam’iyyar tuntuni,” in ji shi.