Aminiya:
2025-09-19@04:06:31 GMT

Kotun Amurka ta daure ’yan Najeriya 5 shekaru 159 kan aikata damfara

Published: 19th, June 2025 GMT

Wata kotu a kasar Amurka ta yanke wa wasu ’yan Najeriya su biyar hukuncin daurin shekaru 159 bisa samun su da da laifin damfarar Amurkawa sama da 100.

Kotun dai ta sami mutanen ne da laifin damfarar kamfanoni da hukumomin gwamnatin kasar kudin da yawansu ya kai Dala miliyan 17, kwatwankwacin Naira biliyan 27 da miliyan 200.

Hakan dai na kunshe ne a cikin wata sanarwa da sashen shari’a na kasar ya wallafa a shafinsa na intanet ranar Laraba, mai dauke da sa hannun mai rikon mukamin Babban Lauyan gwamnati na gundumar gabashin Texas, Ray Combs.

’Yan bindiga sun kashe manoma 24 a Katsina Yadda manoma suka yi addu’ar roƙon ruwa a Zamfara

Sanarwar ta ce mutanen da aka yanke wa hukuncin sun hada da Damilola Kumapayi, Sandra Iribhogbe, Edgal Iribhogbe, Chidindu Okeke and Chiagoziem Okeke, kuma mambobi ne a wani gungun ’yan damfara na kasa da kasa.

Lauyan ya ce ’yan damfarar sun fara harkallar ne tun a shekara ta 2017, inda suke hakon tsofaffi da kuma masu rangwamen gata ta hanyar kirkiro dabaru daban-daban na karbar kudi daga wajensu, wasu lokutan ma ilahirin abin da suka tara a rayuwarsu.

“Da zarar sun karbi kudade daga mutane ta hanyar damfarar, sai su tuttura su ta hanyar asusun ajiya a bankuna da dama da kuma abokan harkallarsu da ’yan kasuwa da ke kasashe a nahiyoyin Afirka da Asiya,” in ji lauyan na gwamnatin Amurka.

Sanarwar ta ce bayan kama su, an gurfaran da su a gaban kotu kan laifukan da suka hada da hadin baki, zambar kudade da kuma damfara, wadanda dukkansu suka amsa aikatawa.

A cewar sanarwar, hakan ce ta sa alkalin kotun, Mai Shari’a Amos Mazzant, ya yanke musu hukuncin daurin shekaru daban-daban a kurkuku.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan Najeriya Damfara

এছাড়াও পড়ুন:

Shugabar Ma’aikata Ta Jihar Kaduna Ta Yi Kiran Amfani Da Fasahar AI.

 

Shugabar ma’aikata ta jihar Kaduna, Madam Jummai Bako ta yi kira ga ma’aikatan gwamnati da su yi amfani da fasahar Artificial Intelligence, A.I yadda ya kamata domin bunkasa ayyukan yi da gudanar da ayyukan.

 

Misis Bako ta yi wannan kiran ne a wani taron bita na yini guda da ofishin shugaban ma’aikata tare da hadin gwiwar cibiyar samar da ayyukan yi ta kasa tsakanin rukunin ma’aikata dake matakin goma zuwa goma sha uku da kuma wasu daraktoci a jihar.

 

Da take bude taron, shugabar ma’aikatar, Madam Jummai Bako ta bayyana cewa, Artificial Intelligence, A.I na iya taimaka wa gwamnati wajen yanke shawara mai kyau, magance matsalolin da suka dade suna tabarbarewar gwamnati da kuma cin hanci da rashawa, don haka akwai bukatar dukkan ma’aikatan gwamnati a jihar Kaduna su shiga cikinsa.

 

Ta bayyana cewa, muhimmancin AI a fannin hidimar jama’a ba zai iya misaltuwa ba, domin zai yi tafiya yadda ya kamata, da inganta gaskiya da kuma kara gamsar da ma’aikata ta hanyar sarrafa ayyuka, da inganta rabon albarkatun kasa da kuma samar da bayanan da suka dace.

 

Ta bayyana cewa gwamnatin jihar Kaduna a karkashin jagorancin Malam Uba Sani na taka muhimmiyar rawa wajen samar da manufofin da za su tallafa wa ma’aikatan gwamnati wajen bunkasa karfinsu na haduwa su yi koyi da su don gabatar da gaskiyar kimiyyar fasahar Sadarwa.

 

“Makullin samun bunƙasa a cikin wannan makomar AI na gaba shine daidaitawa. Muna buƙatar haɓaka al’adun rayuwa na dogon lokaci, inda ma’aikata ke ci gaba da sabunta basirarsu don kasancewa masu dacewa,” in ji ta.

 

A jawabin da ya gabatar, mai gudanarwa a shirin kuma shugaban cibiyar samar da ayyukan yi ta kasa, Malgwi Gideon ya jaddada bukatar ma’aikatan gwamnati su mai da hankali wajen bunkasa kansu domin bayar da gudunmawa a wuraren ayyukansu.

 

A nasa bangaren, Farfesa Ayuba Peter dake sashin kimiyyar lissafi na Jami’ar Jihar Kaduna wanda ya yi magana a kan batun: inganta fasahar kere-kere don inganta ayyukan jama’a a Jihar Kaduna ya bayyana cewa zai taimaka gaya wajen ganin ayyukansu sun gudana cikin sauki.

 

Farfesa Ayuba ya ba da shawarar cewa a kafa wata kungiya mai aiki da za ta tsara bayanin manufofin da za su jagoranci amfani da AI a cikin ma’aikata don kauce wa yin amfani da shi ba daidai ba.

 

A wata hira da wasu daga cikin mahalarta taron, Mista Alexander Garba dake ofishin shugabar ma’aikata da Misis Victoria Williams dake hukumar KASACA da Mista Nuhu Yakusa dake hukumar Kastlea, sun ce horon ya taimaka wajen wayar da kan su yadda za su yi aikinsu cikin sauki.

 

Sun ce samar da sabis da aiki shine mabuɗin kuma sun yi alkawarin yin amfani da ilimin da suka samu yadda ya kamata

 

Taken taron bitar shine dabaru da amfani da fasahar AI don inganta aiki da aiki.

 

COV. Naomi Anzaku

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita
  • An yanke wa Soja hukuncin kisa ta hanyar rataya
  • An kama sojan bogi da ɓarayin mota 2 a Jigawa
  • Shugabar Ma’aikata Ta Jihar Kaduna Ta Yi Kiran Amfani Da Fasahar AI.
  • NAJERIYA A YAU: Wadanne Kalubale Gwamna Fubara Zai Fuskanta Bayan Dawowa Mulkin Ribas?
  • Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 
  • Saudiyya ta saki ’yan Najeriya 3 da ta kama kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi
  • NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba
  • Ministan Tsaron Kasar venezuela Ya Gargadi Amurka Dangane Da Kokarin Juyin Mulki A Kasar
  • Pezeshkian: Ya kamata kasashen musulmi su yanke alaka da gwamnatin sahyoniya tare da kiyaye hadin kai