Iran ta rataye mutumin da ta kama yana yi wa Isra’ila leƙen asiri
Published: 16th, June 2025 GMT
Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ta hanyar rataya ga mutumin da aka kama yana yi wa Isra’ila leƙen asiri.
Mahukunta a bangaren shari’ar sun ce an kama Esmail Fekri a shekarar 2023 yana ƙoƙarin miƙa wa Isra’ila bayanan sirri ne don samun kuɗi.
KADSEMA da IOM sun fara tantance ɓarnar da ambaliya ta yi a Kaduna Sabon harin Iran ya hallaka mana mutum 8 – Isra’ilaWannan ne karo na uku a baya-baya nan da Iran ke aiwatar da hukuncin kisa saboda zargin leƙen asiri ga Isra’ila.
A ranar Lahadi, Isra’ila ta ce ta kama wasu ’yan ƙasa biyu da ake zargin suna aiki da hukumar leƙen asirin Iran.
Babban alƙalin Iran, Gholamhossein Mohseni Ejei, ya bayyana a ranar Litinin cewa, la’akari da yanayin “yaƙi” da suke ciki, dole ne a gudanar da shari’o’i ga waɗanda ake zargin suna aiki da Isra’ila cikin hanzari.
Bayan shafe gomman shekaru ana sa-in-sa tare da nuna wa juna yatsa, a ranar Juma’ar da ta gabata Israila ta kaddamar da wani farmaki na ba-zata wanda ta ce tana kai hari kan makaman nukiliyarta.
Kawo yanzu dai rayukan mutane 224 sun salwanta a kasar ciki har da manyan dakarun sojoji, kwararrun manazarta kimiyyar makaman nukiliya da kuma fararen hula.
Sai dai tuni ita ma Iran din ta mayar da martani tana mai luguden wuta ba dare ba rana a kan Isra’ila da zuwa alkaluman da ofishin firaiministan kasar ya fitar sun ce rayukan mutane akalla 24 sun salwanta.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Ranar Foliyo Ta Duniya: Muna Fatan Ganin Karshen Cutar Foliyo A Jihar Katsina -Zulaihat Dikko Radda
A cewar ta a cikin shekarar 2024 jihar Katsina kawai ta samu masu wannan cuta mutum 17 tare da guda biyu a karamar hukumar Danmusa a cikin wannan shekara
Haka kuma Hajiya Zulaihat Radda ya bada tabbacin cewa kowane yaro an tabbatar da ya amshi allurar Riga-kafin shan Inna
Ana jawabin wakilin asusun tallafawa yara na UNICEF na ofishin Kano, Rahama Mohammed Farah ta yabawa kokarin jihar Katsina na dawo da sabon yunkurin kawar cutar shan Inna a Nijeriya baki daya
Ya kuma bayyana cewa asusun kula da kananan yara na UNICEF Yana hadin gwiwa da gwamnatoci da hukumomi da masu ruwa da tsaki a kananan hukumomi domin ganin wajen fadakar da al’umma akan allurar Riga-kafin shan Inna a jihar Katsina.
Shima da yake jawabi shugaban hukumar lafiya a matakin farko ta Jihar Katsina Dakta Shansudeen Yahaya ya yi alkawarin cigaba da wayar da kan al’umma akan wannan cuta ta shan Inna da sauran cututtuka masu kashe yara a kananan hukumomi 34 na jihar Katsina
Wadanda suka shaida wannan bikin ranar ‘Polio’ ta duniya sun hada da hukumar lafiya ta WHO da kuma masu lalurar cutar shan Inna da wakilan asusun UNICEF da matan shugabannin kananan hukumomi 34 na jihar Katsina
ShareTweetSendShare MASU ALAKA