Aminiya:
2025-11-02@21:12:47 GMT

Kotu ta aike da dan TikTok din da ke wanka a kan titi a Kano gidan yari

Published: 20th, June 2025 GMT

Wata kotun Majistare da ke zamanta a unguwar Nomansland a Kano ta tura wani matashin dan TikTok din nan da ya yi kaurin suna wajen tare titi yana wanka a Kano gidan kurkuku.

Kotun dai ta sami matashin mai suna Umar Hisham Fagge, wanda aka fi sani da Tsulange, zuwa gidan yari har zuwa ranar 3 ga watan Yulin 2025.

2027: ‘Sai bayan babban taron APC Tinubu zai bayyana wanda za su yi takara tare’ NAJERIYA A YAU: Yadda Tsarin Ilimi Ke Karya Gwiwar ’Yan Najeriya

Kotu, wacce ke karkashin Mai Shari’a Hadiza Muhammad Hassan, ta yanke hukuncin ne ranar Alhamis.

Hukumar Tace Fina-finai ta jihar Kano ce dai ta gurfanar da Tsulange a gaban kotun biyo bayan kama shi da laifin sanya rigar ciki ta mata da kuma tare titi yana yin wanka tare da bidiyon barkwanci, in ji mai magana da yawun hukumar, abdullahi Sani Sulaiman.

Hukumar ta ce hakan ya saɓa wa al’adar bahaushe da tarbiyyar addinin musulunci.

Tuni kotun ta tura matashin gidan gyaran hali, yayin da ake ci gaba da gudanar da bincike da kuma samun damar duba matakin ladabtarwa na gaba.

Hukumar ta kuma ce za ta ci gaba da dauka irin wannan mataki domin kawo karshen aikin rashin da’a a kafafen sada zumunta na zamani ga masu amfani da su a jihar.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Dalilin Da Ya Sa Hukumar NIWA Ta Fara Gyaran Hanyoyin Ruwa A Jihar Legsa

Manajar  ofishin na NIWA,  da ke a jihar ta Legas Injiniya Sarat Braimah ta bayyana cewa, tura ma’ikatan hukumar domin yin aikin, zai taimaka wajen gudanar da aikin a cikin inganci.

Kazalika, ya sanar da cewa, hakan zai kuma bayar da damar yin safarar kaya a cikin sauki da kuma safarar matafiya da ke bin hanyar ruwa ta yankin na Ikorodu.

“Mun yi nazari a cikin kwanciyar hankali kan yadda za a tabbatar da an cire fulawar da ke a cikin kasan ruwan ba tare da wata miskila ba tare da kuma bai wa jiragen ruwan damar yin zirga-zirgarsu a hanyoyin ruwan, ba tare da wata matsala ba, “ Inji Injiya Braimah.

“ Aikin ya wuce batun fannin samar da saukin yin sufurin jiragen ruwan har da tabbatar da an kiyaye janyo matsala ga ayyukan kamun Kifi a hanyoyin na ruwan, “ A cewar Inji Manajar.

Ta kara da cewa, babban shugabanmu na hukumar ta NIWA,  Bola Oyebamiji, ne tuni ya riga ya bayar da kwangilar yin aikin, ba wai a jihar Legas kawai ba, har da a sauran hanyoyin ruwa  da ke a sassan kasar.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka November 2, 2025 Labarai Barazanar Amurka Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya: Tinubu Da Trump Za Su Gana Kwanan Nan — Bwala November 2, 2025 Manyan Labarai An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano November 2, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Fursunan da aka yanke wa hukuncin kisa ya tsere daga gidan yari a Yobe
  • Maganin Nankarwa (3)
  • Dalilin Da Ya Sa Hukumar NIWA Ta Fara Gyaran Hanyoyin Ruwa A Jihar Legsa
  • Sanata Sunday Marshall Katung Ya Sauya Sheka Zuwa Jam’iyyar APC
  • An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano
  • Kotu ta dakatar da gudanar da babban taron PDP
  • Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba
  • Kotu ta dakatar da babban taron PDP na ƙasa
  • Kotu ta dakatar da babban taron PDP
  • Xi Jinping Ya Halarci Kwarya-Kwaryan Taron Shugabannin APEC Na 32 Tare Da Gabatar Da Jawabi