Aminiya:
2025-06-20@14:58:19 GMT

Kotu ta aike da dan TikTok din da ke wanka a kan titi a Kano gidan yari

Published: 20th, June 2025 GMT

Wata kotun Majistare da ke zamanta a unguwar Nomansland a Kano ta tura wani matashin dan TikTok din nan da ya yi kaurin suna wajen tare titi yana wanka a Kano gidan kurkuku.

Kotun dai ta sami matashin mai suna Umar Hisham Fagge, wanda aka fi sani da Tsulange, zuwa gidan yari har zuwa ranar 3 ga watan Yulin 2025.

2027: ‘Sai bayan babban taron APC Tinubu zai bayyana wanda za su yi takara tare’ NAJERIYA A YAU: Yadda Tsarin Ilimi Ke Karya Gwiwar ’Yan Najeriya

Kotu, wacce ke karkashin Mai Shari’a Hadiza Muhammad Hassan, ta yanke hukuncin ne ranar Alhamis.

Hukumar Tace Fina-finai ta jihar Kano ce dai ta gurfanar da Tsulange a gaban kotun biyo bayan kama shi da laifin sanya rigar ciki ta mata da kuma tare titi yana yin wanka tare da bidiyon barkwanci, in ji mai magana da yawun hukumar, abdullahi Sani Sulaiman.

Hukumar ta ce hakan ya saɓa wa al’adar bahaushe da tarbiyyar addinin musulunci.

Tuni kotun ta tura matashin gidan gyaran hali, yayin da ake ci gaba da gudanar da bincike da kuma samun damar duba matakin ladabtarwa na gaba.

Hukumar ta kuma ce za ta ci gaba da dauka irin wannan mataki domin kawo karshen aikin rashin da’a a kafafen sada zumunta na zamani ga masu amfani da su a jihar.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Wasu ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Gidan Sanata Natasha A Kogi

Idan dai za a iya tunawa, a baya an kai hari gidan dangin Sanata Akpoti-Uduaghan a ranar 15 ga Afrilu, 2025, ba tare da an kama ko daya daga cikin maharan ba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ambaliyar Ruwan Mokwa: Masana Sun Shawarci Gwamnati Kan Matakin Kariya A Nan Gaba
  • Kotu ta daure mutumin da yake yada bidiyon tsiraici shekara 76 a kurkuku
  • Ɗan TikTok Tsulange Ya Shiga Hannu Bisa Wanka Da Rigar Mama A Titi
  • Hisbah ta lalata katan 243 na barasa da wasu kayan maye a Yobe
  • Kotun Amurka ta daure ’yan Najeriya 5 shekaru 159 kan aikata damfara
  • An ɗaure mutum 7 kan yi wa ɗan sanda rauni a Kano
  • Wasu ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Gidan Sanata Natasha A Kogi
  • Wani Matashi Ya Ƙone Kansa A Kano Saboda Yana Son Zuwa Aljanna 
  • Sin Ta Fara Aiwatar Da Matakin Soke Haraji Kan Kayayyakin Kasashen Afirka 53