Aminiya:
2025-09-18@20:20:22 GMT

Kotu ta aike da dan TikTok din da ke wanka a kan titi a Kano gidan yari

Published: 20th, June 2025 GMT

Wata kotun Majistare da ke zamanta a unguwar Nomansland a Kano ta tura wani matashin dan TikTok din nan da ya yi kaurin suna wajen tare titi yana wanka a Kano gidan kurkuku.

Kotun dai ta sami matashin mai suna Umar Hisham Fagge, wanda aka fi sani da Tsulange, zuwa gidan yari har zuwa ranar 3 ga watan Yulin 2025.

2027: ‘Sai bayan babban taron APC Tinubu zai bayyana wanda za su yi takara tare’ NAJERIYA A YAU: Yadda Tsarin Ilimi Ke Karya Gwiwar ’Yan Najeriya

Kotu, wacce ke karkashin Mai Shari’a Hadiza Muhammad Hassan, ta yanke hukuncin ne ranar Alhamis.

Hukumar Tace Fina-finai ta jihar Kano ce dai ta gurfanar da Tsulange a gaban kotun biyo bayan kama shi da laifin sanya rigar ciki ta mata da kuma tare titi yana yin wanka tare da bidiyon barkwanci, in ji mai magana da yawun hukumar, abdullahi Sani Sulaiman.

Hukumar ta ce hakan ya saɓa wa al’adar bahaushe da tarbiyyar addinin musulunci.

Tuni kotun ta tura matashin gidan gyaran hali, yayin da ake ci gaba da gudanar da bincike da kuma samun damar duba matakin ladabtarwa na gaba.

Hukumar ta kuma ce za ta ci gaba da dauka irin wannan mataki domin kawo karshen aikin rashin da’a a kafafen sada zumunta na zamani ga masu amfani da su a jihar.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

Har kullum, Sin za ta ci gaba da martaba ka’idojin kare hakkokin kamfanoninta. Duba da cewa manhajar TikTok ta shafe tsawon shekaru tana aiki a Amurka, ta kuma samar da dumbin ayyukan yi ga tarin Amurkawa, tare da bayar da gudummawa ga tattalin arzikin kasar, ya kamata gwamnatin kasar ta baiwa manhajar damar cin gajiya daidai da sauran makamantanta dake kasar. Kamar dai ko da yaushe, burin Sin shi ne wanzar da daidaito da cimma moriyar bai daya tare da Amurka.

 

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita
  • Wani ya sace munduwar Fir’auna a gidan tarihin Masar
  • Hukumar Bunkasa Ilimin Manyan Makarantu Ta Shirya Taro Na Musamman Ga Jami’anta
  • Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka
  • Karamar Hukumar Birnin Kano Ta Kaddamar Da Kula Da Lafiyar Ido Kyauta
  • Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok
  • Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala
  • DSS ta maka Sowore da Facebook a Kotu kan cin zarafin Tinubu
  • NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
  • DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu