Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Sin Sun Samar Da Sabuwar Hanyar Sufuri Ga Al’Ummun Kasashen Shiyyar Tsakiyar Asiya
Published: 19th, June 2025 GMT
A watan Afrilun bana, wata farar mota kirar bas mai tsawo mita 12, ta yi tafiya a kan titunan Ashgabat, hedkwatar kasar Turkmenistan. Bas din da kamfanin Yutong na kasar Sin ya kera ta dace da ma’aunin kiyaye muhalli da kasar ta tanada, kuma tana dauke da na’urar ba da jagorancin sufuri mai amfani da tauraron dan Adam, da na’urar biyan kudi ta yanar gizo, matakin da ya bullo da sabuwar hanyar zirga-zirga ga jama’ar wurin.
A wannan shekara, Sin za ta samar da irin wannan bas har 700 ga Ashgabat, matakin da zai biya bukatun zirga-zirgar jama’ar kasar da yawansu ya zarce miliyan 1.
Tun da aka bude taron koli na Sin da kasashen shiyyar tsakiyar Asiya karon farko a shekarar 2023, Sin da kasashen shiyyar Asiya, sun rika bullo da boyayyen karfin hadin gwiwarsu, sun kuma cimma nasarar fitar da sabuwar hanyar hada hannu ba tare da gurbata muhalli ba.
Daga cikin bangarorin hadin gwiwarsu, sana’ar kera motoci na kan gaba. Kamfanonin Sin da dama sun kafa sassansu a wuri, matakin da ya zurfafa hadin gwiwarsu, da samarwa jama’ar wurin wata sabuwar hanyar zirga-zirga, har ma ya samar da karin guraben aikin yi, da karawa jama’ar wurin kudin shiga, kana da horar da ma’aikata a wannan sana’a, matakin da ya kara bunkasa kwarewarsu. (Amina Xu)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Mun bankaɗo sabuwar dabarar ’yan siyasa ta satar kuɗi — EFCC
Hukumar EFCC mai yaƙi da masu yi wa tattalin arzikin Nijeriya ta’annati ta ce ta gano wata sabuwar dabarar satar kudi da wasu ’yan siyasa ke amfani da ita a yanzu ta hanyar amfani da ’yan damfara wadanda aka fi sani da ’yan yahoo a fadin kasar.
Shugaban EFCC, Ola Olukoyede na wannan furuci ne yayin ganawa da manema labarai a hedikwatar hukumar da ke Abuja a ranar Litinin.
Tinubu zai je jaje bayan kisan fiye da mutum 100 a Benuwe Gwamnati ta kasa ɗaukar matakin da ya dace a kan kashe-kashen Benuwe — AtikuOlukoyede wanda ya ce wadannan matasa ’yan yahoo da suke zubar da kimar Nijeriya a idon duniya sun kuma faɗa dumu-dumu ta’adar nan ta garkuwar da mutane domin neman kuɗin fansa.
Ya bayyana cewa kaurin suna da ’yan yahoo suka yi a matsayin miyagu sun shafa wa kowane ɗan Nijeriya bakin fenti da duk inda suka shiga ake ɗari-ɗari da su a matsayin masu laifi.
Shugaban na EFCC ya ce a yanzu da zarar miyagun ’yan siyasa sun samu damar yin ruf da ciki a kan dukiyar kasa, sukan haɗa kai da waɗannan matasa ’yan yahoo-yahoo su boye kuɗaɗen a cikin wani asusun yanar gizo da ake kira wallet.
“Sau tari irin waɗannan ’yan siyasa sukan jibge ’yan yahoo a otel-otel su rika buɗe musu asusun ajiya na kirifto su boye biliyoyin kuɗaɗen da suka sata.”
Olukoyede ya buga misali da wani matashi mai shekaru 22 da hukumar ta kama yana yi wa ’yan siyasa irin wannan aika-aikar wanda aka gano ya samu tukwicin Naira biliyan biyar a tsawon watanni 18 kacal.