Aminiya:
2025-09-17@23:08:33 GMT

Matatar man Isra’ila ta daina aiki bayan sabon harin Iran

Published: 17th, June 2025 GMT

Hukumar gudanarwar matatar man ƙasar Isra’ila da ke yankin Haifa ta sanar cewa matatar ta dakatar da ayyukanta ɗungurungum bayan harin da Iran ta kai mata.

Kamfanin Bazan Group da ke kula da matatar ya ce harin na Iran ya tilasta musu tsayar da gaba ɗaya — a yayin da sabon rikicin na yankin Gabas ta Tsakiya ke ɗaukar zafi tsakanin ƙasashen biyu da suka jima suna yi wa juna kallon hadarin kaji.

Bazan Group ya bayyana harin rokokin Iran ya lalata tashar wutar lantarki da matatar ke amfani da shi.

Harin na Iran ya kuma halaka ma’aikata uku a matatar ta Haifa, kamar yadda hukumomin Isra’ila suka sanar.

Wannan na faruwa a ci gaba hare-haren ramuwar gayya da makamai masu linzami da Iran ke kaiwa, bayan jiragen Isra’ila sun ƙaddamar da hare-hare da kawo yanzu suka yi ajalin mutane sama da 220 a sassan Iran, har da Tehran, Babban birnin ƙasar.

Kashi 70 na mutanen da Isra’ila ta kashe a Iran da mata da ƙananan yara ne; da wasu manyan jami’an tsaro da wani masanin kimiyyar makamashin nukiliya.

Aminiya ta ruwaito Isra’ila na cewa ta ƙaddamar da hare-haren ne domin daƙile Iran, wadda ke dab da mallakar makamin nukiliya a cikin wannan shekara, ko cikin watanni kaɗan masu zuwa.

Ana iya tuna cewa Fira Minista Banjamin Netanyahu ya bayyana cewa hallaka shugaban addinin Iran, Ayatullah Alkhamene’i zai yi tasiri wajen kawo karshen ta’addnacin Iran.

A nata bangaren Iran ta Bayyana cewa Isra’ila za ta yaba wa aya zaƙi, kan waɗannan hare-haren ragoncin da ta kai wa fararen hula da cibiyoyin soji da tashoshin makamashin nukiliyarta.

Ta kuma bayyana harin bai tsayar da shirinta na nukiliya domin Samar da wata lantarki da sauran abubuwa na zaman lafiya ba.

Ramuwar gayyar Iran ta shafi cibiyoyin sojin Isra’ila da tashar wutar lantarki da matatar mai, baya ga halaka mutane sama da 24 da lalata gine-gine a wurare daban-daban, ciki har da birnin Kudus, da kuma Tel Aviv, babban birnin ƙasar Isra’ila.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gabas ta Tsakiya hare hare Iran Isra ila Matatar mai nukiliya

এছাড়াও পড়ুন:

An Fara Taron Hukumar Makamashin Nukliya Ta Duniya IAEA Karo Na 69 A Birnin Vienna

An fara taron hukumar IAEA ta kasa da kashe karo na  69TH  a jiya Litinin, inda a taron ne ake fayyana al-amura masu muhimmanci da ya shafi makamashin Nukliya a duniya, kuma tuni shugaban hukumar makamashin Nukliya ta kasar Iran Muhammad Eslami yakejagorantar tawagar Iran a taron.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran, ya bayyana cewa a irin wannan taron na shekara-shekara inda kuma aka tattauna abubuwa masu muhimmanci dangane da makamashin Nukliya.

Kafin ya bar nan Tehran Eslami ya ce zai gabatar da al-amura wadanda suka shafi sabawa dokokin hukumar da IAEA ta kasa. Ya kuma kara da cewa JMI ba zata saba barin hakkinta tashe makamashin Uranium wanda ya zo cikin yarjeniyar NPT.

Eslami ya kammala da cewa wannan taron wuri ne na bayyana sabbin ra’a yi da kuma damuwar da kasashen duniya suke fauskanta da ya shafi makamashion nukliya.

Daga karshe shugaban hukumar makamashin nukliyata kasar Iran ya ce,Iran zata gabatar da korafi kan hare-haren HKI  da Amurka kan cibiyoyin makamacin Nukliya na kasar Iran, amma kumahukumar ta kasa yin allawadai da hare-haren.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Espania Ta Soke Cinikin Makamai Na EUR Miliyon 700 Da HKI Saboda Kissan Kiyashi A Gaza September 16, 2025 Makaman ‘Drons’ Na Yemen Sun Fada Kan Wurare Masu Muhimmanci A  HKI September 16, 2025 Taron Doha: Daga matakin Allawadai zuwa matakan kalubalantar laifukan Isra’ila September 16, 2025 Ministan Tsaron Venezuela Ya Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Juyin Mulki A Kasar September 16, 2025 Pezeshkian: Ya kamata kasashen musulmi su yanke alaka da gwamnatin sahyoniya September 16, 2025 Bayanin Bayan Taron Doha Ya Yi Kira Da A Kafa Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kare Kai September 15, 2025 Fira Ministan Spain: Bai Kamata A Rika Barin “Isr’ila” Tana Shiga Gasar September 15, 2025 Shugaban Kasar Iran Ya Gana Da Sarkin Kasar Qatar A Birnin Doha September 15, 2025  Dan Kasar Iran Mai Kirkira Ya Sami Kyautar Yabo A Kasar China September 15, 2025 Fizishkiyan:  Wajibi Ne Musulmi Su Hada Kai Domin Dakatar Da Laifukan HKI September 15, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwara ETF Ya Dauki Nauyin Karatun Fitattun Dalibai A Matakin Sakandare
  • Iran Ta Bayyana Abubuwan Da Bata Amince Da Su Ba A Jawabin Bayan Taro Na Kungiyar OIC A Birnin Doha
  • Iran Ta Bukaci Musulmi Su Goyi Bayan Yunkurin Kasa da Ka Na Kauracewa Isra’ila
  • Duniya na tir da sabon farmakin Isra’ila kan Gaza
  • Akalla Falasdinawa 78 ne sukayi shahada a hare-haren Isra’ila a Gaza
  • Iran Ta Bukaci IAEA Tayi Tir Da Harin Da Isra’ila Ta Kai A Tashoshin Nukiyarta.
  • ’Yan ‘Mafiya’ na ƙoƙarin kashe matatar man fetur da na gina —Ɗangote
  • An Fara Taron Hukumar Makamashin Nukliya Ta Duniya IAEA Karo Na 69 A Birnin Vienna
  • Shugaban Kasar Iran Ya Gana Da Sarkin Kasar Qatar A Birnin Doha
  • Kasashen Larabawa da na Musulmi na taron gaggawa kan harin Isra’ila a Qatar