Sin Ta Cimma Sabuwar Nasarar Bincike Duniyar Wata
Published: 18th, June 2025 GMT
Kasar Sin ta cimma nasarar aikin gwajin tserewa lokacin da ake gamu da matsala a matakin farko na harbar kumbo mai dauke da mutane na “Mengzhou” a yau Talata, a cibiyar harbar taurori dan Adam dake birnin Jiuqiu, abin da ya alamanta cewa, Sin ta cimma sabuwar nasara a aikin binciken duniyar wata tare da kumbo mai daukar mutane.
Wannan ita ce nasara irinta ta biyu da Sin ta samu a wannan bangare, bayan shekaru 27 da suka gabata, da samun nasara ta farko a aikin gwajin da ta gudanar a shekarar 1998.
Aikin gwajin tserewar da aka gudanar ya kasance muhimmin mataki na ba da tabbaci ga rayukan ’yan saman jannati, wato idan an gamu da hadari ko matsala ba zato ba tsammani, za a iya samar da jagoranci ga sashen kumbo mai dawowa ya bar wuri ma hadari, tare da dawo da ’yan saman jannati doron duniyarmu lami lafiya.
Kumbo mai daukar mutane na “Mengzhou”, sabuwar na’ura ce da Sin ta kera bisa dogaro da karfin kashin kanta, da zummar gudanar da nazarin sararin samaniya a nan gaba lami lafiya, wanda ke iya tashi zuwa sararin samaniya da dawowa doron kasa, wannan kumbo mai iya daukar mutane 7 na kunshe da fasaha ta sahun gaba a duniya. (Amina Xu)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Babu dalilin kai wa Iran farmaki — Putin
Shugaban Ƙasar Rasha, Vladimir Putin, ya ce babu wata hujja ko dalilin kai wa Iran hari.
Putin ya yi wannan furuci ne yayin wata tattaunawa da Ministan Harkokin Wajen Iran, Abbas Agarachi a fadar Kremlin da ke birnin Moscow.
Akwai ƙasashen da ke shirin bai wa Iran makaman nukiliya — Rasha Fararen hula sun yi garkuwa da sojoji 57 a ColumbiaA jawabin da ya gabatar a farkon tattaunawar wanda aka yada a gidan talabijin na gwamnatin Rasha, shugaba Putin ya ce: “Babu wata hujja ko dalili da zai sa a kai wa Iran farmaki.”
Ya ƙara da cewa “na ji daɗin zuwan ka [Agarachi] Moscow a yau. Wannan zai ba mu damar tattauna waɗannan batutuwa masu wahala da kuma hanyar shawo kan lamarin.”
A nasa jawabin, Ministan Harkokin Wajen na Iran ya ce ƙasarsa na da “ƙawance ta ƙut da ƙut” da Rasha.
Ya ce hare-haren da Isra’ila da Amurka suka kai wa Iran “sun saɓa wa dokoki da ƙa’idojin ƙasa da ƙasa.”
A farkon shekarar nan Iran da Rasha sun sanya hannu kan wata yarjejeniyar fahimtar juna.
Sai da ba ta haɗa da ƙawancen soji ba kuma ba ta buƙaci Rasha ta kai wa Iran ɗaukin kariya ba.