Takun Saka Tsakanin Rasha Da Faransa Kan Batun Kayyade Makaman Nukiliya
Published: 7th, March 2025 GMT
Ana ci gaba da takun saka tsakanin Rasha da Faransa biyo bayan kalaman Emmanuel Macron na baya-bayan nan game da kayyade makaman nukiliya.
Moscow ta dauki wadannan kalamai a matsayin barazana kai tsaye, yayin da Paris ke kare matsayinta ta hanyar jaddada bukatar kare Turai, Wanda ya nuna yadda ake samun rashin jituwa sosai kan batun Ukraine.
Moscow ta yi imanin cewa Emmanuel Macron, wanda ya yi Allah wadai da “tashin hankali” na Rasha yayin jawabinsa a yammacin Laraba, yana son “yakin (a Ukraine) ya ci gaba.”
Ministan harkokin wajen Rasha ya yi la’akari da cewa kalaman shugaban Faransa Emmanuel Macron, wanda ya nuna yuwuwar kariyar Turai da laima ta nukiliya “barazana” ce ga Rasha.
A sa’i daya kuma, Sergei Lavrov ya yi watsi da duk wata yuwuwar yarjejeniya da Moscow kan batun tura dakarun wanzar da zaman lafiya na Turai a Ukraine domin tabbatar da tsagaita bude wuta.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Sin Ta Gano Wani Dutse Mai Sassaka Na Daular Qin A Kan Tsaunin Qinghai-Tibet
Hukumar kula da al’adun gargajiya ta kasar Sin ta sanar a yau cewa, an gano wani dutsen da aka yi sassaka kan sa a kan tsaunin Qinghai-Tibet, wanda ya kasance irinsa daya tilo na daular Qin da har yanzu ke mazauninsa na asalin, kuma a wuri mafi tsawo.
Dutsen wanda ke arewacin bakin tabkin Gyaring na gundumar Maduo, dake arewa maso yammacin lardin Qinghai, na wuri mai tsawon mita 4,300.
Gano dutsen na tattare da wata muhimmiyar daraja ga tarihi da fasaha da kimiyya. Sarki Qinshihuang na daular Qin ne ya fara hada kan kasar Sin. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp