An cimma jerin yarjejeniyoyin hadin gwiwa a taron koli na biyu na kasar Sin da tsakiyar Asiya da aka gudanar a birnin Astana na kasar Kazakhstan a ranar 17 ga watan nan agogon kasar. Shugabannin kasashen biyar na tsakiyar Asiya sun yaba wa kasar Sin a matsayin babbar abokiyar hadin gwiwa kuma kawa ta gaskiya da kasashen yankin tsakiyar Asiya za su iya amincewa da ita har abada.

Ana iya sa ran cewa, hadin gwiwar da Sin za ta yi da tsakiyar Asiya ba wai kawai za ta inganta manyan ayyukan hadin gwiwa ba ne, har ma za ta kara karfafa kokarin “neman sabbin abubuwa masu dadi” da “sabbin kirkire-kirkire”, da sa kaimi ga kasashen shida wajen cimma zamanantarwa tare da juna.

Shugabannin kasashe biyar na yankin tsakiyar Asiya sun nuna goyon baya sosai ga tunanin kasar Sin game da samar da al’umma mai makoma ta bai-daya ga bil’adama, da kuma manyan tsare-tsare guda uku na duniya, da tabbatar da yin ciniki cikin ‘yanci da tsarin ciniki tsakanin bangarori daban-daban, da hada karfi da karfe wajen kare adalci a duniya. Wadannan yarjejeniyoyi za su haifar da karin kwanciyar hankali ga zaman lafiya da ci gaban duniya. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: tsakiyar Asiya

এছাড়াও পড়ুন:

Tankokin Isra’ila sun kashe mutum 51 a wurin karbar abinci a Gaza

Tankokin yaƙin Isra’ila sun i kashe kimanin mutun 51 a yankin Khan Younis da ke Zirin Gaza, a yayin da mutanen suke tsaka da karbar abincin tallafi.

Jami’ain lafiya sun sun ce mutum 51 sun mutu, wasu 200 sun samu raunuka — 20 daga cikinsu suna cikin halin rai-kwakwai-mutu-kwakwai — bayan harin.

Sun bayyana harin a matsayin daya daga cikin mafiya muni da sojojin Isra’ila suka kai a baya-bayan nan a yayain da Falasdinawa ke kokarin samun abinci domin su rayu.

Bidiyon lamarin da suka karade kafofin sada zumunta sun nuna wasu gomman gawarwaki da ake zargin tankokin yakin Isra’ila sun mutsuttsuke a kan titi a Khan Younis.

Shaidu sun bayyana cewa sai da sojojin Isra’ilan suka sa mutanen suka taro a wuri guda sa’annan tankokin suka bude musu wuta.

Tankokin sun bude wuta ne a daidai lokacin da suke kokarin karbar tallafin abinci daga wata babbar motar kungiyar agaji.

Rundunar sojin Isra’ila ta tabbatar da aukuwar harin na ranar Litinin, wanda ta ce tana gudanar da bincike a kai.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Sin Sun Samar Da Sabuwar Hanyar Sufuri Ga Al’Ummun Kasashen Shiyyar Tsakiyar Asiya
  • Wang Yi Ya Yi Tsokaci Kan Sakamakon Ziyarar Shugaba Xi A Kazakhstan
  • Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta
  • Xi Da Shugabannin Kasashe 5 Na Tsakiyar Asiya Sun Halarci Bikin Rattaba Hannu
  • An Gudanar Da Bikin Mu’amalar Jama’a Da Al’adu A Tsakanin Sin Da Tsakiyar Asiya A Astana
  • Xi Ya Gabatar Da Muhimmin Jawabi A Taron Koli Na Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu
  • Daga Taklimakan Zuwa Sahara: Karin Abubuwan Al’ajabi Na Faruwa Bisa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Yaki Da Kwararar Hamada
  • Tankokin Isra’ila sun kashe mutum 51 a wurin karbar abinci a Gaza
  • Shugaba Xi Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan Kassym-Jomart Tokayev