Sin Ta Fatattaki Laifukan Zamba Ta Shafin Intanet 294,000 A Bara
Published: 17th, June 2025 GMT
A wani gangamin magance aikata laifukan zamba da damfara ta shafukan intanet da kasar Sin ta kaddamar a fadin kasar baki daya, ‘yan sandan kasar ta Sin sun fatattaki laifuka 294,000 a shekarar 2024, inda suka kama mutane da dama da ake zargi ciki har da shugabanni gungu-gungu fiye da 570, da masu samar musu da kudi, da kuma kasurguman da ke da hannu a wannan ta’asar.
‘Yan sanda sun durfafi cibiyoyin sadarwa na masu aikata laifuka da ke ba da haramtaccen tallafi ga aikata ayyukan zamba a kasashen ketare. A cewar ma’aikatar kula da tsaron al’umma, wadannan kungiyoyin sun tafka ta’asa masu yawa da suka hada da tallata laifukan a shafin intanet, da satar kudi, da amfani da fasaha, da kuma taimakawa wajen saukake hanyoyin tsallaka kan iyakokin kasa.
Tun daga farkon shekarar 2024, cibiyar yaki da zamba ta kasar Sin ta kara kaimi wajen yin gargadi a kan lokaci da kuma daukar matakan dakile ta’asar ta hanyar amfani da fasahohin zamani, inda ta ba da sanarwa game da hakan sau miliyan 1.8. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Ce Ba’a Rufe Kofar Diblomasiyya Ba, Matukar HKI Ta Dakatar Da Kaiwa Kasar HKI
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araghchi ya bayyaana cewa kasarsa bata rufe kofar diblomasiyya dangane da shirinta na makamashin Nukliya ba, matukar HKI zata dakatar da hare-haren da take kaiwa kasar.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto ministan yana fadar haka a yau Lahadi a taron yan jaridun da ya kira a birnin Tehran. Ya kuma kara da cewa Iran tana son ta ci gaba da shirinta na makamashin Nukliya ta zaman lafiya ta hanyar diblomasiyya idan an bata damar yin haka.
Ministan ya ce ikidar JMI ne warware dukkan matsaloli da farko ta hanyar Diblomasiyya, da kuma tattaunawa amma ba zamu taba amincewa wani ya hanamu hakkimu na mallakar makamashi nukliya ta zaman lafiya ba. Kuma mun bayyana cewa a shirye muke a gudanar da bincike a ayyukammu. Sojojin Iran sun cilla wasu sabbin hare-hare a kan HKI a yau Lahadi da rana.
Yakin da HKI ta fara a safiyar jumma’an da ta gabata, mai kuma samun goyon bayan Amurka, don tilsatawa Iran amincewa da sharuddanta na shirin Iran na makamashin nukliya ne.