Za mu iya galaba kan Iran ko babu Amurka — Isra’ila
Published: 20th, June 2025 GMT
Shugaban Isra’ila, Isaac Herzog, ya bayyana cewa ƙasarsa za ta iya samun nasara a yaƙin da take yi da Iran ko da kuwa Amurka ba ta shigar mata ba.
Sai dai Herzog ya shaida wa ABC News cewa kawar da barazanar nukiliyar Iran yana da muhimmanci ga “duniya mai ’yanci”, ciki har da Amurka.
Nan da mako biyu za mu yanke shawara kan shigar wa Isra’ila yaƙi — Trump Muna shawartar Trump kada ya shiga yaƙin Iran da Isra’ila — BirtaniyaDa yake amsa tambayar ko me zai ce dangane da yiwuwar shigar wa ƙasarsa yaƙin da take yi da Iran da Shugaba Donald Trump ya yi iƙirari, Herzog ya ce “ina da cikakkiyar yarda a kan duk wani hukunci da zai yanke kuma ina da tabbacin duk abin da ya yanke shi ne daidai.
Herzog ya ce mako guda ke nan da fara yaƙin amma ya tabbatar da cewa barazanar Iran ba za ta kau ba nan take.
“Babbar nasarar da za mu samu ita ce kawo ƙarshen barazanar nukiliyar Iran,” a cewar Herzog.
“[Jagoran addini na Iran, Ayotallah Ali Khamenei] shi ne kan macijin da ke jagorantar duk wata barazana da Iran take yi da muke buƙatar mu sare.
“Tun ba yanzu ba yake babatun ganin bayan ƙasarmu da al’ummarta. Saboda haka ba mu da wata manufa a yanzu face mun yi maganinsa,” kamar yadda Herzog ya shaida wa gidan talabijin na ABC.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Benjamin Netanyahu Iran Isaac Herzog
এছাড়াও পড়ুন:
Litar fetur za ta iya komawa N1,000 a Najeriya saboda yakin Isra’ila-Iran – Masana
Masana sun yi gargadin cewa yakin da ake gwabzawa a tsakanin Isra’ila da Iran zai iya shafar farashin man fetur a duniya kuma hakan zai iya yin illa ga tattalin arzikin Najeriya.
Masanan na cibiyar Commercio Partners da ke Legas sun bayyana fargabar ce a cikin wani rahoto da cibiyar ta fitar mai taken: “Farashin kayayyaki ya sauka a Najeriya a watan Mayu, amma akwai matsala a nan gaba” wanda aka wallafa shi ranar 16 ga watan Yunin 2025.
A cewar rahoton, rikicin da ake fama da shi a yankin Gabas ta Tsakiya zai iya rage yawan man fetur din da ake samarwa a duniya wanda kuma zai kai ga tashin farashinsa a kasuwanni.
Ma’aikatan Kwalejin Ilimi ta jihar Kaduna za su tsunduma yajin aiki Ambaliyar Mokwa – Har yanzu muna neman mutum 700 – Gwamnatin NejaSun yi gargadin cewa duk da yake Najeriya kasa ce mai arzikin man na fetur, amma tashin farashin ba lallai ne ya zama alheri ga kasar ba.
Aminiya ta rawaito cewa farashin danyen mai ya rika yin tashin gwauron zabo a ’yan kwanakin nan inda ya haura Dalar Amurka 75 kan kowacce ganga.
Sai dai tashin na nufin farashinsa zai tashi a gida Najeriya, inda farashin zai iya kaiwa Naira 1,000.
A yanzu dai ana sayar da man ne daga tsakanin N870 zuwa N920 a gidajen mai.
“A Najeriya kuwa, inda yanzu aka janye tallafin man fetur kuma farashinsa ya ta’allaka da kasuwar duniya, hakan zai iya shafar tattalin arzikin kasar,” in ji masanan.
Rahoton ya kuma ce duk da cewa matatar mai ta Damngote na aiki, duk da haka kasar ba ta tsira daga barazanar ba.
Ya kuma ce, “Har yanzu shigo da mai ake zuwa Najeriya, kuma tashin farashinsa a kasuwannin duniya na nufin yadda ake tace shi da rarrabawa ko dakon shi su ma za su karu
“Idan danyen man ya kara tsada, farashin man fetur a Najeriya – wanda yanzu haka yake wajen N825 – zai iya komawa kusan N1,000,” kamar yadda masanan suka yi hasashe.