Aminiya:
2025-08-04@12:54:14 GMT

Za mu iya galaba kan Iran ko babu Amurka — Isra’ila

Published: 20th, June 2025 GMT

Shugaban Isra’ila, Isaac Herzog, ya bayyana cewa ƙasarsa za ta iya samun nasara a yaƙin da take yi da Iran ko da kuwa Amurka ba ta shigar mata ba.

Sai dai Herzog ya shaida wa ABC News cewa kawar da barazanar nukiliyar Iran yana da muhimmanci ga “duniya mai ’yanci”, ciki har da Amurka.

Nan da mako biyu za mu yanke shawara kan shigar wa Isra’ila yaƙi — Trump Muna shawartar Trump kada ya shiga yaƙin Iran da Isra’ila — Birtaniya

Da yake amsa tambayar ko me zai ce dangane da yiwuwar shigar wa ƙasarsa yaƙin da take yi da Iran da Shugaba Donald Trump ya yi iƙirari, Herzog ya ce “ina da cikakkiyar yarda a kan duk wani hukunci da zai yanke kuma ina da tabbacin duk abin da ya yanke shi ne daidai.

Herzog ya ce mako guda ke nan da fara yaƙin amma ya tabbatar da cewa barazanar Iran ba za ta kau ba nan take.

“Babbar nasarar da za mu samu ita ce kawo ƙarshen barazanar nukiliyar Iran,” a cewar Herzog.

“[Jagoran addini na Iran, Ayotallah Ali Khamenei] shi ne kan macijin da ke jagorantar duk wata barazana da Iran take yi da muke buƙatar mu sare.

“Tun ba yanzu ba yake babatun ganin bayan ƙasarmu da al’ummarta. Saboda haka ba mu da wata manufa a yanzu face mun yi maganinsa,” kamar yadda Herzog ya shaida wa gidan talabijin na ABC.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Benjamin Netanyahu Iran Isaac Herzog

এছাড়াও পড়ুন:

Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa

Gargaɗin ya yi daidai da irin wannan sanarwar da ofisoshin jakadancin Amurka a Jamaica da Uganda suka fitar kwanan nan, a wani ɓangare na yaƙi da dabi’ar karya ƙa’ida shige da fice. 

A cikin watan Janairun 2025, hukumomin Amurka sun sake jaddada aniyarsu na ƙarfafa ikon kula da iyakoki kan yin amfani da damar zama dan ƙasa ta haihuwa.

A farkon wannan shekara, shugaban ƙasar ɗonald Trump ya sake nanata matsayinsa na cewa yaran da aka haifa a Amurka ga baƙin haure ba su da takardun zama ƴan ƙasa kai tsaye.

A bisa dokar da aka yi wa kwaskwarima na Amurka kan shaidar zama dan ƙasa, ta fayyace cewa duk wani jaririn da aka haifa sai an duba matakin damar zaman iyayensa a ƙasar kafin a amince da shaidar zamansa dan ƙasar ko akasin hakan, inda jami’an suka ce ba za a amincewa da wadanda suka shiga ƙasar kawai don an ba su biza ba.  

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Son Zai Bar Tottenham Zuwa Amurka Bayan Shafe Shekaru 10 A Ingila
  • Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa
  • Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto
  • Rahoton Majalisar Dinkin Duniya Ya Yi Gargadi Kan Barazanar Kungiyoyin ‘Yan Ta’adda A Afirka
  • Shugaban Ansarullah: Amurka Tana Da Hannu A Ta’asar Da HKI Take Aikatawa A Gaza
  • Iran ta yi gargadi game da makirce-makircen Isra’ila na kawo cikas ga tsaron yankin
  • Gaza: Witfkoff ya yi rangadi a wuraren da Amurka ta kafa domin tallafi
  • Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine
  • Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili
  • Limamin Sallar Juma’a Ya Ce; Iran Zata Mayar Da Isra’ila Kufai Idan Ta Sake Kai Hari Kan Kasarta