Kotu ta daure mutumin da yake yada bidiyon tsiraici shekara 76 a kurkuku
Published: 20th, June 2025 GMT
Babbar Kotun Tarayya da ke Legas ta yanke wa wani mai suna Olukoye Olalekan hukuncin daurin shekaru 76 a kukuku saboda yada hotunan tsiraicin yara kanana da kuma aikata damfara.
Alkalin kotun, Mai Shari’a Alexander Owoeye, ne ya yanke hukuncin ranar Alhamis, bayan ya samu mutumin da aikata laifukan da aka zarge shi da su.
An dai gurfanar da Olukoye ne a gaban kotun ana zarginsa da laifuka 18 da suke da alaka da yada hotunan tsiraicin yara kanana, damfara ta intanet, boye kudaden haram da kuma mallakar kadarori ta haramtacciyar hanya, wanda Hukumar Yaki da Rashawa ta EFCC ta zarge shi da aikatawa.
A cewar lauyar masu kara, Bilkisu Buhari-Bala, laifukan sun saba wa tanade-tanaden sassa na 23(1)(c) da 23(1)(f) na kundin laifukan intanet da kuma sassa na 18(3),16(2)(a),16(3),1(1)(a), da 1(2) na kundin hana almundahanar kudade.
Yayin shari’ar, lauyar ta EFCC ta shaida wa kotun cewa Olukoye ya bude wasu shafukan sada zumunta a dandalin sada zumunta irin su Snapchat da Instagram, wadanda ya rika amfani da su a matsayin mace daga jihar North Carolina ta Amurka.
Lauyar ta ce mutumin ya rika amfani da shafukan wajen damfarar mutane har ta kai ga ya mallaki wani gida, ta hanyar yin barazanar wallafa hotunan tsiraicin yara kanana a shafukan.
Da yake yanke shukunci, Mai Shari’a Alexander ya sami Olukoye da dukkan laifukan sannan ya yanke masa hukuncin jimillar daurin shekara 76 a gidan kaso.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Damfara Yada tsiraici
এছাড়াও পড়ুন:
Najeriya na hasashen samun N300bn a shekara daga noman dabino
Gwamnatin Najeriya ta ce tana sa ran samun kimanin Naira biliyan 300 a duk shekara daga noman dabino a ƙasar.
Ta ce tana fatan samun wannan kuɗaɗen shiga ne daga rabon irin dabino guda miliyan biyar da ta samar ga manoma a wannan shekara ta 2025.
Darakta-Janar na Hukumar Yaƙi da Kwararowar Hamada (NAGGW), Alhaji Saleh Abubakar, ya ce, “Kowane iri ƙwaya ɗaya na iya samar da miliyan 100 na dabino, wanda kuɗinsa ya kai Naira miliyan ɗaya. Ga shi kuma sau biyu dabino ke yin ’ya’ya a shekara.
“Muna hasashen manoma za su samar da Naira biliyan 300, wanda tabbas zai bunƙasa tattalin arzikin Najeriya,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa hukumar za ta raba irin dabino miliyan biyar da ta samar ga jihohi 11 da ke maƙwabtaka da saharar hamada domin su ci gajiyar tattalin arzikin noman dabino.
Ya sanar da haka ne a yayin taron ƙaddamar sashen itatuwa a ƙauyen Maimalari da ke Ƙaramar Hukumar Yusufari ta Jihar Yobe.
A cewarsa, manufar shirin ita ce bunƙasa tattalin da ke cikin ɓangaren gandun daji wajen samar da ƙarin kuɗaɗen shiga da harkokin kasuwanci a jihohi takwas da ke gaɓar hamada.