Kotu ta daure mutumin da yake yada bidiyon tsiraici shekara 76 a kurkuku
Published: 20th, June 2025 GMT
Babbar Kotun Tarayya da ke Legas ta yanke wa wani mai suna Olukoye Olalekan hukuncin daurin shekaru 76 a kukuku saboda yada hotunan tsiraicin yara kanana da kuma aikata damfara.
Alkalin kotun, Mai Shari’a Alexander Owoeye, ne ya yanke hukuncin ranar Alhamis, bayan ya samu mutumin da aikata laifukan da aka zarge shi da su.
An dai gurfanar da Olukoye ne a gaban kotun ana zarginsa da laifuka 18 da suke da alaka da yada hotunan tsiraicin yara kanana, damfara ta intanet, boye kudaden haram da kuma mallakar kadarori ta haramtacciyar hanya, wanda Hukumar Yaki da Rashawa ta EFCC ta zarge shi da aikatawa.
A cewar lauyar masu kara, Bilkisu Buhari-Bala, laifukan sun saba wa tanade-tanaden sassa na 23(1)(c) da 23(1)(f) na kundin laifukan intanet da kuma sassa na 18(3),16(2)(a),16(3),1(1)(a), da 1(2) na kundin hana almundahanar kudade.
Yayin shari’ar, lauyar ta EFCC ta shaida wa kotun cewa Olukoye ya bude wasu shafukan sada zumunta a dandalin sada zumunta irin su Snapchat da Instagram, wadanda ya rika amfani da su a matsayin mace daga jihar North Carolina ta Amurka.
Lauyar ta ce mutumin ya rika amfani da shafukan wajen damfarar mutane har ta kai ga ya mallaki wani gida, ta hanyar yin barazanar wallafa hotunan tsiraicin yara kanana a shafukan.
Da yake yanke shukunci, Mai Shari’a Alexander ya sami Olukoye da dukkan laifukan sannan ya yanke masa hukuncin jimillar daurin shekara 76 a gidan kaso.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Damfara Yada tsiraici
এছাড়াও পড়ুন:
UNICEF Tayi Gargadi Game Da Mawuyacin Hali Da Yara Ke Ciki A Gaza
Kakakin hukumar kula da kanana yaran ta majalisar dinkin duniya tess ingram ta bayyana cewa yanayin da yara ke ciki a yankin gaza yayi muni sosai, inda sama da yara miliyan daya dake gaza suke bukatar taimakon gaggawa na ruwan sha da kuma abinci
Ingram ta fadi a wata hira da aka yi da ita cewa dubban yara a falasdinu suna kwana da yunwa kusan kowanne dare, kuma akalla yara 650,000 ba su koma makaranta ba duk da yarjejeniyar dakatar da bude wuta da aka cimamma a baya –bayan nan tsakanin bangarori biyu,
Har ila yau ta bayyana batun dakatar da bude wuta a matsayin labari mai kyau, da ya kawo karshen ci gaba da lugudan wuta da israila ke yi kowanne lokaci da ya ci rayukan dubban yara kanana, sai dai ta jaddada cewa yarjejeniyar dakatar da bude wuta ba za ta wadatar ba dole ne sai an kawo karshen yunwa da kuma samar da ruwan sha ga sauran iyalai yankin gaza.
A ranar 10 ga watan okotba ne yarjejeniyar dakatar da bude wuta ta fara aiki a gaza amma duk da haka yanayin da ake ciki ya kara tsananta baka iya zuwa wasu yankuna da dama a yankin saboda ci gaba da kasancewar sojojin isra’ila a wajen.
Isra’ila tana ci gaba da keta yarjejeniyar da ta cimma da kungiyar Hamas, tana ci gaba da kai hare-hare da harbe harbe kuma tana hana shigar da kayan agaji da ake bukata zuwa yankin na Gaza, kuma kashi 2 cikin 3 na adadin wadanda aka kashe mata ne da yara kanana.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Hamas Ta yi Watsi Da Zargin Da Amurka Tayi Mata Kan Batun Motocin Agaji A Gaza November 3, 2025 El-Zakzaki: Yakin Sudan Yana Kare Maslahar Kasashen Yamma ne Kawai November 3, 2025 Iran Ta Karbi Sako Kan Batun Komawa Teburin Tattaunawa Ba Kai Tsaye Ba November 3, 2025 Ministar Jin Dadin Jama’a ta Sudan: Mayakan RSF Sun Kashe Mata 300 Da Yi Wa 25 Fyade A El Fasher November 3, 2025 Pezeshkian: Bunkasa Masana’antar Makamashin Nukiliyar Iran Don Inganta Rayuwar Al’ummar Iran Ne November 2, 2025 Araqchi: Da Hadin Bakin Amurka, Gwamnatin Isra’ila ta kaddamar Da Hari Kan Kasar Iran November 2, 2025 Larijani: Iran Ba Ta Tsoron Gudanar Da Tattaunawa, Amma Ta Zama Mai Amfani November 2, 2025 Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza November 2, 2025 Kasar Qatar Ta Ba Da Tallafin Gaggawa Ga Al’ummar Sudan Bayan Gumurzun El-Fasher November 2, 2025 IAEA : Babu wata shaida da ke nuna cewa Iran na kera makaman nukiliya November 2, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci