Masu Karanta Adabin Shafin Intanet Na Sin Sun Kai Miliyan 575
Published: 17th, June 2025 GMT
Yawan masu karanta adabin da aka dora a shafin intanet na kasar Sin ya karu zuwa miliyan 575, lamarin da ya nuna yadda ake samun karuwar karanta labarai da rubutun zube ta fasahar zamani a fannin al’adun kasar.
Masu karatu da aka haifa bayan shekarar 2000 su ne suka kara yawan ci gaban da aka samu a baya-bayan nan, wadanda suka dauki kusan kashi hudu na dukkan masu karatu a shafin na intanet, kamar yadda wani rahoto da kungiyar marubuta ta kasar Sin ta fitar a yau Talata ya bayyana.
Bisa bayanan da aka samu daga manyan dandalolin adabi na intanet guda 50 a fadin kasar Sin, rahoton ya kiyasta cewa, masana’antar adabin ta samar da kudin shiga kusan yuan biliyan 44, kimanin dalar Amurka biliyan 6.1 a shekarar 2024. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Iran ta sake kai hare-haren martani kan Isra’ila
Dakarun kare juyin juya halin Musulunci (IRGC) sun kaddamar da wani sabon harin makamai masu linzami da jirage marasa matuka kan Isra’ila a cikin daren jiya Asabar, biyo bayan matakin farko na harin ramuwar gayya na kan harin Isra’ila na ranar Juma’a.
Jim kadan bayan harba makamai masu linzami da jirage marasa matuka, sashen hulda da jama’a na IRGC ya ba da sanarwar kaddamar da wani sabon shiri na manyan makamai masu linzami da jiragen sama marasa matuka.
Sanarwar ta yi nuni da cewa, sashen kula da sararin samaniya na IRGC ya fara wannan sabon mataki na aikin a matsayin mayar da martani kai tsaye ga sabbin ta’addancin gwamnatin sahyoniyawan.
Babban abin da aka fi mayar da hankali kan wannan sabon farmakin na ‘Operation True Promise III’ an bayar da rahoton cewa, birnin Haifa mai tashar jiragen ruwa ya kunshi muhimman wuraren soji da masana’antu na gwamnatin.
Hare-haren sun shafi wasu muhimman cibiyoyin soji da masana’antu na Isra’ila, da suka hada da matatun mai da na wutar lantarki a Haifa, inda aka ce gobara ta tashi a sanadiyar haka.
Daya daga cikin faifan bidiyon ya nuna wata gagarumar gobara da ta tashi a matatar mai ta Haifa bisa tasirin da manyan makamai masu linzami na Iran suka yi, wanda ya haskaka sararin samaniyar yankunan da aka mamaye.