Rikicin ƙabilanci ya yi ajalin mutum 20 a Chadi
Published: 17th, June 2025 GMT
Akalla mutane 20 sun mutu yayin da wasu 16 suka jikkata a wani rikicin ƙabilanci da ya auku a wani lardi na gabashin kasar Chadi.
A cikin wata sanarwa da ma’aikatar sadarwa ta ƙasar ta fitar, ta ce fadan ya barke ne daga ranar 10 zuwa 14 ga watan Yuni a yankin Molou na lardin Ouaddai da ke gabashin kasar.
Wata majiya ta ce rikicin ya samo asali ne bayan da matasan Zaghawa biyu dauke da makamai suka sace babur na wani dan kabilar Ouaddai a ranar Talata, lamarin da ya haddasa kazamin rikici.
Bayanai sun ce rikicin ya yi kamari ne a ranar Asabar lokacin da aka kashe akalla ‘yan kabilar Ouaddai 12 a wani hari da ‘yan kabilar Zaghawa suka kai.
Kazalika, wata sanarwa da suka fitar a birnin N’djamena, ’yan majalisar dokoki 14 na lardin Ouaddai, sun yi Allah wadai da abin da suke danganta da munanan ayyuka, tare da yin kira ga hukumomin kasar da su kara kokarin tabbatar da tsaron lafiya da dukiyoyin ’yan kasar.
Tun dai shekaru da suka wuce ne, gabashin Chadi da ke kan iyaka da Sudan ke fama da rikici tsakanin manoman kabilar Ouaddai da kuma kabilun Larabawa, wadanda makiyaya ne.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Wutar lantarki ta kashe mutum 5, ta jikkata 13 a Gombe
Rundunar ’Yan Sandan jihar Gombe, ta tabbatar da mutuwar mutum biyar da kuma jikkatar wasu 13, sakamakon tashin wutar lantarki a unguwar Tudun-Wada, Pantami a jihar.
Wutar ta tashi ne da safiyar ranar Asabar sakamakon matsala da ta taso daga wata tiransifoma a yankin, kamar yadda kakakin ’yan sandan jihar, DSP Buhari Abdullahi, ya bayyana.
Sojoji sun kama ɗan China da wasu 4 kan zargin safarar makamai a Borno da Yobe Damina: NiMet ta gargaɗi jihohi 13 kan barazanar ambaliyar ruwaCikin waɗanda suka rasa rayukansu har da Babban Sakatare na Ma’aikatar Ayyuka ta Musamman ta jihar, Alhaji Muhammad Yusuf Kulani, tare da ’ya’yansa da wasu mazauna unguwar.
Marigayin shi ne shugaban ƙungiyar ƙwararrun akantoci ta Jihar Gombe (ANAN).
’Yan sanda daga ofishin Low-Cost sun isa wajen don tabbatar da tsaro da kuma kai waɗanda suka jikkata zuwa asibiti.
Kwamishinan ’Yan Sandan jihar, Bello Yahaya, ya miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan mamatan.
Ya kuma ce za su gudanar da cikakken bincike domin gano musabbabin tashin wutar da kuma ɗaukar matakan kare faruwar hakan a gaba.
Ya kuma roƙi al’umma da su kasance masu bin doka tare da bayar da haɗin kai yayin gudanar da binciken.