Leadership News Hausa:
2025-06-19@01:13:06 GMT

An Kashe Wasu ‘Yan Bindiga 12, An Kwato Makamai A Katsina

Published: 19th, June 2025 GMT

An Kashe Wasu ‘Yan Bindiga 12, An Kwato Makamai A Katsina

Da take aiwatar da rahotannin sirri cikin gaggawa, rundunar hadin gwiwa da ta kunshi jami’an ‘yansandan Nijeriya, Sojoji, jami’an kula da jama’a na jihar, da ’yan banga na yankin sun bi sawun barayin da suka tsere zuwa Dutsen Falale da ke yankin Kurfi-Safana inda aka yi musayar wuta mai tsanani, wanda ya yi sanadin mutuwar ‘yan bindigar 12.

 

Sai dai kuma, yayin da yake yabawa wannan bajinta da jajircewa da jami’an tsaron suka yi, Dakta Mua’zu ya bayyana matukar alhininsa game da rasuwar wani dan banga mai suna Alhaji Danmalam wanda ya rasa ransa a fafatawar.

 

Bugu da kari, soja guda ya samu raunuka kuma a halin yanzu yana samun kulawa a Asibiti.

 

Alhaji Danmalam ya rasu ne sakamakon harbin bindiga a cibiyar kiwon lafiya ta matakin farko da ke Charanchi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Sarki ya yi barazanar hana yin Musulunci a garinsa bayan dodanni sun kai wa Musulmi hari

Sarkin yankin Oke Agbe a Jihar Ondo ya ci Musulmi tara, tare da barazanar koran su da kuma haramta yin addinin Musulunci a garinsa bayan da wasu dodanni suka kai hari a wani masallaci da gidan limami.

Aminiya ta samu rahoto cewa, wasu dodanni sun kai hari a masallaci da gidan wani limami, suka lakaɗa wa matansa da ’ya’yansa duka a yankin Oke Agbe, da ke shiyyar Akoko a Ƙaramar Hukumar Akoko ta Arewa a Jihar Ondo Jihar Ondo.

Ƙungiyar Kare Haƙƙin Musulmi (MURIC), ta bayyana cewa, “Basaraken yankin ya yi Musulmin tara da aka ci zalinsu tara, saboda sun yi ihu tare da zagin dodannin, maimakon su riƙa yin kuka suna roƙon dodannin.

“Basaraken ya umarci matan limamin su biya tarar awaki tara da tumaki bakwai da kuma ƙwarya biyu na hoto, cikin kwana uku, kafin ranar Litinin da ta gabata, ko kuma a haramta musu zama a garin.”

Ɗan shekara 10 ya harbe mahaifinsa ɗan sanda a Anambra Yadda Cin ganyayyaki ke gagarar ’yan Najeriya

Shugaban Ƙungiyar, Farfesa Ishaq Akintola, ya bayyana a cikin wata sanarwa cewa, dodannin sun kai wannan harin ne a ranar Alhamis 12 ga watan Yuni, nan da muke ciki.

Farfesa Ishaq Akintola, ya bayyana harin a matsayin wata shaida da ke nuna yadda ake tsananin cin zarafin Musulmi a yankin Yarabawa, don haka ya kira da a ɗauki matakin shari’a a kan duk masu hannu a wannan aika-aika.

Ya ci gaba da cewa abin da ya faru ya ƙara girman fargabar da ƙungiyar take da shi gane da makomar al’ummar Musulmi a yankin Kudu maso yammacin Najeriya, “saboda abin sai ƙara muni yake ta yi.”

Don haka muna Allah-wadai da wannan hari na jahiliyya, da kuma zaluncin wannan sarki, wanda ya ci karo da kundin tsarin mulkin ƙasa, a ƙarƙashin tsarin dimokuraɗiyya a ƙarni na 21.

“Muna kira da a yi wa waɗannan Musulmi adalci, kuma muna kira ga Gwamnatin Jihar Ondo ya taka wa Sarkin Oke Agbe Akoko bukri, tare da tabbatar da cewa wani abin ƙi bai samu limamin ko ’ya’yansa ko matansa ba. Sa’annan dole a janye maganar haramta musu zama a garin,” in ji kungiyar Musulmin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wasu ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Gidan Sanata Natasha A Kogi
  • Sojojin Nijeriya sun kashe gomman ’yan ta’adda a Tafkin Chadi
  • Hare-haren Benuwe: Tinubu ya ziyarci waɗanda suka jikkata a asibiti 
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Ƙauyen Kebbi, Sun Kashe Mutane Da Dama
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Jami’an Tsaro 4 Da Manoma A Katsina
  • Sarki ya yi barazanar hana yin Musulunci a garinsa bayan dodanni sun kai wa Musulmi hari
  • Sabon Shirin Gwamnatin Katsina: Za A Fara Sauya Tunanin Tubabbun ‘Yan Bindiga
  • Dan shekara 10 ya kashe mahaifinsa ɗan sanda da bindiga
  • Sojoji Sun Damƙe Ɗan Fashi, Sun Kwato Makamai A Kaduna Da Filato