Leadership News Hausa:
2025-08-04@15:14:50 GMT

An Kashe Wasu ‘Yan Bindiga 12, An Kwato Makamai A Katsina

Published: 19th, June 2025 GMT

An Kashe Wasu ‘Yan Bindiga 12, An Kwato Makamai A Katsina

Da take aiwatar da rahotannin sirri cikin gaggawa, rundunar hadin gwiwa da ta kunshi jami’an ‘yansandan Nijeriya, Sojoji, jami’an kula da jama’a na jihar, da ’yan banga na yankin sun bi sawun barayin da suka tsere zuwa Dutsen Falale da ke yankin Kurfi-Safana inda aka yi musayar wuta mai tsanani, wanda ya yi sanadin mutuwar ‘yan bindigar 12.

 

Sai dai kuma, yayin da yake yabawa wannan bajinta da jajircewa da jami’an tsaron suka yi, Dakta Mua’zu ya bayyana matukar alhininsa game da rasuwar wani dan banga mai suna Alhaji Danmalam wanda ya rasa ransa a fafatawar.

 

Bugu da kari, soja guda ya samu raunuka kuma a halin yanzu yana samun kulawa a Asibiti.

 

Alhaji Danmalam ya rasu ne sakamakon harbin bindiga a cibiyar kiwon lafiya ta matakin farko da ke Charanchi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Shirin kashe N712bn kan gyaran filin jirgin Legas ya tayar da ƙura

Amincewar Gwamnatin Tarayya da kashe Naira biliyan 712 biliyan don gyaran Filin Jirgin Sama na Murtala Muhammed da ke Legas ya haifar da ce-ce-ku-ce a faɗin Najeriya.

Wannan gagarumin kashe kuɗi, da Majalisar Zartarwa ta Kasa ta amince da shi a ranar Alhamis da ta gabata, ya sanya masana harkar jiragen sama, ’yan adawa, da kuma jama’ar ƙasa yin tambayoyi game da buƙatarsa, tsadarsa, da kuma inda za a samo kuɗin.

Masu suka suna nuna yadda kuɗin ya yi yawa, har ya ninka kuɗin da aka ware wa Ma’aikatar Sufurin Jiragen Sama a kasafin kuɗin 2025 har sau goma. Hasali ma aikin ba ya cikin kasafin 2025.

Wannan ya sa wasu ke kiran aikin a matsayin “almubazaranci,” musamman ganin halin da tattalin arzikin ƙasar ke ciki.

Wani babban abin da ke haifar da surutan shi ne tsarin samo kuɗin. Gwamnati ta sanar da cewa za a samu kuɗin ne daga Asusun Ayyukan Raya Kasa na Renewed Hope Infrastructure Development Fund.

Amma jam’iyyun adawa, ciki har da ADC, sun ce Majalisar Dokoki ta Ƙasa ba ta amince da wannan kashe kuɗi ba, don haka suka kira shi “kashe kuɗi ba tare da kasafi ba.”

Yunkurinmu na jin ta bakin kakakin Majalisar Dattawa da ta Wakilai ya ci tura, wanda hakan ya ƙara ɓoye sirrin aikin.

Gyaran tashar jirgin ta Legas, wanda aka ba kamfanin gine-gine na CCECC kwangilar, zai haɗa da kwance ginin gaba ɗaya sannan a sake gina sabbin na’urorin zamani da tsarin lantarki da ruwa.

Wasu ayyukan sun haɗa da kwangilar Naira biliyan 44.13 na sabbin fitilun titin jirgin, Naira biliyan 24.27 na faɗaɗa wuraren ajiye jiragen sama, da kuma shingen tsaro . mai ɗauke da na’urorin zamani na Naira biliyan 49.9.

Jimillar kuɗin ta kuma haɗa da irin waɗannan gyare-gyaren a filayen jiragen sama na Kano da Fatakwal.

Wannan ba shi ne yunkurin farko na gyara filin jirgin na Legas ba. Tsohuwar gwamnatin Marigayi Muhammadu Buhari ta buɗe wani sabon tashar jirgin a shekarar 2022, wanda aka gina da kuɗin rancen dala miliyan 500 daga ƙasar China.

Amma wannan tashar ta fuskanci matsaloli masu yawa, inda kamfanonin jiragen sama da yawa suka ƙi amfani da ita saboda ƙarancin wurin ajiye manyan jirage.

Sabuwar tashar ta kasance ba a amfani da ita na tsawon fiye da shekara guda, inda yawancin kamfanonin jiragen sama na duniya ke ci gaba da amfani da tsohuwar tashar da yanzu aka shirya wa gagarumin gyara.

Yayin da gwamnati ke ci gaba da shirin ta, cece-kucen ya ƙara ta’azzara.

Tare da rashin samun cikakken bayani daga hukumomin Majalisar Dokoki da kuma tarihin ayyukan filayen jiragen sama da suka tsaya, jama’a na ci gaba da shakkar gaskiyar kuɗin da za a kashe da kuma nasarar da za a samu a wannan sabon aiki.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane Da Dama A Kauyukan Zamfara
  • Gwamnan Neja Ya Bada Umarnin Sake Bude Jami’ar Ibrahim Badamasi Babangida, Lapai.
  • Shirin kashe N712bn kan gyaran filin jirgin Legas ya tayar da ƙura
  • An ƙara hakimai 6 a Masarautar Katsina
  • Dadiyata: Buhari ya gaza nemo shi, Tinubu yana da lokaci — Amnesty
  • Mutum ɗaya ya rasu, an jikkata wasu yayin arangama da ’yan sanda a Abuja
  • Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto
  • An Sake Kashe Wata Ɗalibar Jami’ar Ondo
  • Jami’ar Umaru Yar’adua ta kori ɗalibai 57 kan satar jarabawa
  • MDD: HKI Ta Kashe Falasdinawa 1 Fiye Da 100 A Cikin Kwanaki 2 A Lokacinda Suka Karban Abinci