Dortmund ta yi canjaras da Fluminense a Club World Cup
Published: 18th, June 2025 GMT
Borussia Dortmund ta soma buɗe wasanninta na gasar FIFA Club World Cup da canjaras a karon-battar da ta yi da kungiyar Fluminense ta Brazil a ranar Talata.
Ana dai ganin babbar kungiyar da ta zama gagarabadau a Rio de Janeiro Fluminense a matsayin mafi hatsari a rukunin F wanda ya kunshi har da kungiyar Ulsan HD ta Koriya ta Kudu.
An dai rika kai wa juna hari a yayin wasan da suka barje gumi a filin wasa na Metlife da ke East Rutherford a wajen birnin New York, sai dai mai tsaron ragar Dortmund, Gregor Kobel ya ceci kungiyarsa bayan wata kwallo da Jhon Arias ya nano masa daga nesa tun kafin tafiya hutun rabin lokaci.
Fluminense wadda tsohon dan wasan PSG da Chelsea, Thiago Silva mai shekaru 40 shi ne kyaftin dinta, ta yi kokarin samun damar Dortmund ana tsaka da kai ruwa na bayan dawowa daga hutun rabin lokaci, amma Kobel ya rike kwallon da Agustin Canobbio ya yi yunkurin tarar numfashinsa.
Golan dai ya sake yin wata bajintar bayan ya tare kwallon da Everaldo ya yi sakada masa a kusurwar kasa, lamarin da haka a karkare wasan babu ci.
Fluminense dai ta samu gurbin zuwa gasar Club World Cup ta bana bayan nasarar lashe Copa Libertadores da ta yi a shekarar 2023.
Bajintar da Fluminense ta yi a karon-battar ta da manyan kungiyoyin da suka kasance zakaran gwajin dafi a nahiyyar Turai ya kara tabbatar da cewa tana iya tabuka abin a-zo-a-gani a gasar Club World Cup ta bana da aka sauyawa fasali.
Dortmund za ta yi fatan samun nasara a wasan gaba da za ta fafata da kungiyar Mamelodi Sundowns ta Afirka ta Kudu.
AFP
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Mutane 44 Suka Mutu Bayan Mamakon Ruwa Da Aka Tafka A Beijing
Ruwan sama kamar da bakin kwarya tare da iska mai karfi da aka tafka a kwanan nan ya yi sanadin mutuwar mutane 44, yayin da wasu tara suka bace a birnin Beijing, kamar yadda aka bayyana a wani taron manema labarai da ya gudana a yau Alhamis.
A yayin taron manema labarai da gwamnatin birnin Beijing ta gudanar a yau game da rigakafin ambaliyar ruwa da bayar da agajin gaggawa, an bayyana cewa, bala’in ambaliyar ruwan da ya auku kwanan nan ya shafi mutane sama da 300,000 tare da lalata gidaje 24,000 a birnin Beijing.
Sai dai, yanzu haka birnin na Beijing na kara kokarin farfado da wutar lantarki, da share tituna, da kai muhimman kayayyaki ga mazauna yankin da suka rasa matsugunansu, sakamakon ambaliyar ruwa da zabtarewar kasa da suka auku sanadin mamakon ruwan sama mai karfi da aka tafka a tsaunukan da ke wajen birnin. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp