Dortmund ta yi canjaras da Fluminense a Club World Cup
Published: 18th, June 2025 GMT
Borussia Dortmund ta soma buɗe wasanninta na gasar FIFA Club World Cup da canjaras a karon-battar da ta yi da kungiyar Fluminense ta Brazil a ranar Talata.
Ana dai ganin babbar kungiyar da ta zama gagarabadau a Rio de Janeiro Fluminense a matsayin mafi hatsari a rukunin F wanda ya kunshi har da kungiyar Ulsan HD ta Koriya ta Kudu.
An dai rika kai wa juna hari a yayin wasan da suka barje gumi a filin wasa na Metlife da ke East Rutherford a wajen birnin New York, sai dai mai tsaron ragar Dortmund, Gregor Kobel ya ceci kungiyarsa bayan wata kwallo da Jhon Arias ya nano masa daga nesa tun kafin tafiya hutun rabin lokaci.
Fluminense wadda tsohon dan wasan PSG da Chelsea, Thiago Silva mai shekaru 40 shi ne kyaftin dinta, ta yi kokarin samun damar Dortmund ana tsaka da kai ruwa na bayan dawowa daga hutun rabin lokaci, amma Kobel ya rike kwallon da Agustin Canobbio ya yi yunkurin tarar numfashinsa.
Golan dai ya sake yin wata bajintar bayan ya tare kwallon da Everaldo ya yi sakada masa a kusurwar kasa, lamarin da haka a karkare wasan babu ci.
Fluminense dai ta samu gurbin zuwa gasar Club World Cup ta bana bayan nasarar lashe Copa Libertadores da ta yi a shekarar 2023.
Bajintar da Fluminense ta yi a karon-battar ta da manyan kungiyoyin da suka kasance zakaran gwajin dafi a nahiyyar Turai ya kara tabbatar da cewa tana iya tabuka abin a-zo-a-gani a gasar Club World Cup ta bana da aka sauyawa fasali.
Dortmund za ta yi fatan samun nasara a wasan gaba da za ta fafata da kungiyar Mamelodi Sundowns ta Afirka ta Kudu.
AFP
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
An tallafa wa mata 250 da abinci da kayan sana’a a Kaduna
Wata ’yar kasuwa mai taimakon al’umma, Barista Catherine Bitrus, ta raba wa mata 250 da abinci da kayan sana’a a garin Manchok da ke Ƙaramar Hukumar Kaura, a Jihar Kaduna.
Tallafin ya haɗa da injinan niƙa, buhunan shinkafa, katan-katan na taliyar yara, da man girki.
Harin Benuwe: ’Yan sanda sun tarwatsa masu zanga-zanga Takarar Tinubu: Rikici ya ɓarke a APC bayan Ganduje ya ƙi goyon bayan ShettimaA lokacin rabon kayan, Catherine, shugabar kamfanin Natural Beauty Secret, ta ce ta yi hakan ne domin taimaka wa matan karkara da ke fama da matsaloli a rayuwa.
“Allah Ya ba ni arziƙi, shi ya sa na ga dacewa na raba da waɗanda ke bukata,” in ji ta.
“Na zaɓi mata ne domin na san irin wahalar da suke sha.”
Ta roƙi matan da su dage da ƙoƙari, ka da su yanke ƙauna, domin komai na duniya yana da mafita idan aka jajirce.
Catherine ta ce tana da niyyar ci gaba da wannan aiki, kuma ta yaba wa Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, saboda irin goyon bayan da yake bai wa mata a jihar.
Kwamishinan Tsaro da Harkokin Cikin Gida na jihar, Barista James Kanyip, ya yaba da wannan aiki, inda ya buƙaci sauran masu hali da ƙungiyoyin su dinga tallafa wa marasa ƙarfi.
Shugaban kwamitin shirya taron, Lucky Ezra, ya bayyana Catherine a matsayin mace mai zuciyar taimako da kishin jama’a.
A madadin sauran matan da suka amfana, Josephine Bature ta nuna farin ciki da godiya, tare da addu’ar Allah Ya saka wa Catherine da alheri.