Masana sun yi gargadin cewa yakin da ake gwabzawa a tsakanin Isra’ila da Iran zai iya shafar farashin man fetur a duniya kuma hakan zai iya yin illa ga tattalin arzikin Najeriya.

Masanan na cibiyar Commercio Partners da ke Legas sun  bayyana fargabar ce a cikin wani rahoto da cibiyar ta fitar mai taken: “Farashin kayayyaki ya sauka a Najeriya a watan Mayu, amma akwai matsala a nan gaba” wanda aka wallafa shi ranar 16 ga watan Yunin 2025.

A cewar rahoton, rikicin da ake fama da shi a yankin Gabas ta Tsakiya zai iya rage yawan man fetur din da ake samarwa a duniya wanda kuma zai kai ga tashin farashinsa a kasuwanni.

Ma’aikatan Kwalejin Ilimi ta jihar Kaduna za su tsunduma yajin aiki Ambaliyar Mokwa – Har yanzu muna neman mutum 700 – Gwamnatin Neja

Sun yi gargadin cewa duk da yake Najeriya kasa ce mai arzikin man na fetur, amma tashin farashin ba lallai ne ya zama alheri ga kasar ba.

Aminiya ta rawaito cewa farashin danyen mai ya rika yin tashin gwauron zabo a ’yan kwanakin nan inda ya haura Dalar Amurka 75 kan kowacce ganga.

Sai dai tashin na nufin farashinsa zai tashi a gida Najeriya, inda farashin zai iya kaiwa Naira 1,000.

A yanzu dai ana sayar da man ne daga tsakanin N870 zuwa N920 a gidajen mai.

“A Najeriya kuwa, inda yanzu aka janye tallafin man fetur kuma farashinsa ya ta’allaka da kasuwar duniya, hakan zai iya shafar tattalin arzikin kasar,” in ji masanan.

Rahoton ya kuma ce duk da cewa matatar mai ta Damngote na aiki, duk da haka kasar ba ta tsira daga barazanar ba.

Ya kuma ce, “Har yanzu shigo da mai ake zuwa Najeriya, kuma tashin farashinsa a kasuwannin duniya na nufin yadda ake tace shi da rarrabawa ko dakon shi su ma za su karu

“Idan danyen man ya kara tsada, farashin man fetur a Najeriya – wanda yanzu haka yake wajen N825 – zai iya komawa kusan N1,000,” kamar yadda masanan suka yi hasashe.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Iran Isra ila Najeriya

এছাড়াও পড়ুন:

Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

 

Ya kuma bayyana cewa kasar Sin wuri ne mai kyau ga harkokin zuba jari ga ‘yan kasuwa na duniya. Ya ce hadin gwiwa da kasar Sin yana nufin hadin gwiwa da damammaki, imani da kasar Sin yana nufin imani da kyakkyawar makoma, zuba jari a kasar Sin yana nufin zuba jari mai riba ta dogon zango.(Safiyah Ma)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare October 31, 2025 Daga Birnin Sin Xi Jinping Ya Halarci Kwarya-Kwaryan Taron Shugabannin APEC Na 32 Tare Da Gabatar Da Jawabi October 31, 2025 Daga Birnin Sin An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo October 30, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu ya yanke hulɗa da Amurka kawai — Sheikh Gumi
  • Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba
  • Pezeshkian: Bunkasa Masana’antar Makamashin Nukiliyar Iran Don Inganta Rayuwar Al’ummar Iran Ne
  • Araqchi: Da Hadin Bakin Amurka, Gwamnatin Isra’ila ta kaddamar Da Hari Kan Kasar Iran
  • Iran Ta Gargadi Isra’ila Kuma Tasha Alwashin Kare Shirinta Na Nukiliya
  • Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar
  • An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano
  • Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC
  • Ya Kamata Shugaba Tinubu Ya Ƙulla Alaƙa Ta Kut-da-kut Tsakanin Hukumar Shige Da Fice Da Kwastam – Babandede
  • Ana zargin ɗa da kashe mahaifinsa a Kano saboda hana shi ƙara aure