Guguwar ruwan sama ta yi ɓarna a Kwalejin Kimiyya da Fasaha a Kogi
Published: 19th, June 2025 GMT
An samu rahoton cewa guguwar ruwan sama ta yi ɓarna a Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Tarayya (Federal Polytechnic), Idah a Jihar Kogi, inda ta ɓarnata kadarori da gine-gine da dama.
Rahoton na cewa, wata mummunar guguwar ruwan sama da ta biyo bayan ruwan sama da aka kwashe tsawon sa’o’i ana yi a ranar Laraba ce ta haddasa barnar, inda ta lalata rufin gine-gine da tagar gine-gine da dama a makarantar.
Ana cikin haka, an ba da rahoton cewa ɗakunan karatu da ɗakunan gwaje-gwaje da ɗakunan kwanan ɗalibai da ke cikin harabar kwalejin guguwar ruwan saman ta haddasa mummunar ɓarna.
Shugaban Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Tarayya Idah, Dokta Yakubu Usman, ya ce, “Wannan abu ne mai ban tsoro ga Kwalejin a irin wannan lokaci, muna baƙin ciki da irin ɓarnar da guguwar ta yi.
“Har yanzu muna kan tantance irin ɓarnar da guguwar ta yi domin sanin asarar kuɗi wajen gyarawa da kuma dawo da wuraren da suka lalace yadda suke.
“Ya zuwa yanzu matakin ɓarnar ya kai ga Gwamnatin Tarayya ce kawai za ta iya shiga tsakani a iya fitar da cibiyar daga wannan yanayin cikin sauri”.
Dakta Usman ya ƙara da cewa, cibiyar za ta yi duk mai yiwuwa wajen bayar da tallafin da ya dace ga wuraren da abin ya shafa domin ɗalibai su ci gaba da harkokin karatu ba tare da ɓata lokaci ba
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: guguwar ruwan sama
এছাড়াও পড়ুন:
Sharrin son auren Mai Wushirya aka yi min — Mansura Isa
Tsohuwar jarumar Kannywood, Mansurah Isa, ta ƙaryata labarin da wata jaridar intanet ta yaɗa cewa wai tana son ta auri shahararren dan TikTok, Ashiru Mai Wushirya, wanda ya yi tashe a kafafen sada zumunta a ’yan kwanakin nan.
A wani saƙo da ta wallafa, Mansurah ta ce labarin ƙarya ne kuma ya jefa ta da iyalinta cikin ruɗani da damuwa.
Ta ce, “Na shiga firgici bayan na ga wannan labarin. Ba ni da wata alaka da Mai Wushirya. Wannan sharri ne tsagwaron karya.”
Rahoton da aka yada a jaridar AMC Hausa ya yi iƙirarin cewa wai Mansurah ta ce ta shirya auren Mai Wushirya idan har yana son ta da gaske.
Kofin kofi mafi tsada a duniya ya shiga kasuwa a kan Naira miliyan 1.5m An yi garkuwa da Mataimakin Shugaban Majalisar Dokokin KebbiAmma jarumar ta yi watsi da wannan iƙirarin, tana mai cewa jaridar ta ɓata mata suna kuma ta karya ƙa’idojin aikin jarida.
Ta ce, “Na kira su, na ba su awa 24 su sauke labarin, amma har yanzu ba su yi hakan ba. Sun kira ni sun ba ni hakuri a waya, amma labarin har yanzu yana nan. Wannan abu ya zubar min da mutunci kuma ya saka iyalina cikin tashin hankali,” ina ji ta.
Mansurah ta bayyana cewa yanzu tana cikin shirin ‘WalkAwayCancer’, wani gagarumin shiri na wayar da kan jama’a kan mcutar daji, amma wannan labarin karya ya yi ƙoƙarin karkatar da hankalin mutane daga ainihin aikinta.
“Kun hana ni barci da kwanciyar hankali saboda labarin da babu gaskiya a cikinsa. Amma in sha Allahu, za ku ji daga gare mu,” in ji ta cikin fushi.
Har zuwa lokacin da muka kammala wannan labarin dai, kamfanin AMC Hausa bai fitar da wata sanarwa ba dangane da ƙarar da Mansurah ke shirin kai musu bisa zargin yaɗa labarin ƙarya.