“An yi hasashen matsakaicin hadarin ambaliya ga al’ummomi 445 a cikin kananan hukumomi 116 daga Afrilu zuwa Yuni, 1,458 a kananan hukumomi 271 daga Yuli zuwa Satumba, da kuma 1,473 a kananan hukumomi 171 tsakanin Oktoba da Nuwamba,” in ji Ministan.

Matakan aiki

Da yake magana da wannan dan jarida, Shugaban Tsangayar Kimiyyar Muhalli na Jami’ar Jihar Nasarawa dake Keffi, Dokta Kante Pkantisawa, ya bukaci ‘yan Nijeriya da su mai da hankali sosai kan hasashen yanayi da hukumar kula da yanayi ta Nijeriya (NiMET) da NHSA suka yi.

Ya ce, “Ambaliyan da aka yi a Mokwa babbar tunatarwa ce game da tasirin sauyin yanayi da kuma bukatar daukar matakan da suka dace, babu wata fa’ida da ya wuce a ce dole a fadin kasar nan, ya zama al’ummomi da masu ra’ayin su kara taka muhimmiyar rawa wajen hasashen yanayin da NiMET ta yi da kuma hasashen ambaliyar ruwa na shekara-shekara da Hukumar Kula da Ruwa ta Nijeriya ta fitar a duk shekara.

“Har ila yau, yana da mahimmanci a gaggauta yashe fadamu da kogunan ruwa da ake da su, tare da hanzarta samar da sabbin hanyoyi don rage kwararar ruwa da barnar da yake haifarwa amma a yi amfani da shi wajen noma.”

Ya bayyana bukatar a ba da shawarwari ga wadanda suka rasa ‘yan uwa da kuma maido da rayuwar ga wadanda ambaliyar ruwa ta yi wa illa.

“Wannan lokaci ne mafi wahala ga iyalan wadanda abin ya shafa, makwabtansu, da kuma al’ummarsu, zuciyata na kan wadanda suka rasa ‘yan uwansu, tare da dukiyoyinsu, gami da amfanin gona.

“Haka zalika an lalata ababen more rayuwa sakamakon mummunar ambaliyar ruwan, ina addu’ar Allah Madaukakin Sarki ya sanyaya wa wadanda suka rasa rayukansu, ya kuma rage musu radadin bakin ciki,” in ji shi.

Kudade

Hakazalika, wani mai fafutukar kare muhalli kuma mai fafutukar kare hakkin bil’adama, Dakta DuroRasak, ya bayyana ambaliyar Mokwa da ta faru a baya-bayan nan a matsayin “mummunan bala’i.” Ya kuma yi kira ga hukumomi da su kara yawan kudaden da ake ware wa muhallin ga jihohin saboda tasirin sauyin yanayi.

“Malalar ambaliyar ruwa da ta afku a Garin Mokwa na Jihar Neja a baya-bayan nan, wani abin tunawa ne mai ban tausayi game da illar rashin kula da muhalli da ababen more rayuwa, da rashin shirye-shiryen bala’i da sauyin yanayi.

“Ambaliyar ruwan da ta afku a sakamakon ruwan sama mai karfi da ya fara tun a ranar 28 ga watan Mayu, ya yi sanadin asarar rayukan mutane da dama tare da jefa al’ummar Mokwa cikin firgici, asara, da rashin tabbas.

“Yayin da aka tabbatar da mutuwar mutane sama da 200, wasu alkaluma na nuni da cewa adadin wadanda suka mutu zai iya karuwa sosai, har zuwa 700, saboda yawancin wadanda abin ya shafa sun shiga kogin Neja. Sama da mutane 3,000 ne suka rasa matsugunansu, gidaje sama da 265 sun lalace, an yi asara sama da gidaje 503.

Ya ci gaba da cewa, “Baya ga mace-mace, ambaliya ta yi sanadiyyar raba dubban mutane da muhallansu, ta lalata gidaje, tare da durkusar da tattalin arzikin yankin.

“Yankuna da dama a Nijeriya ciki har da Mokwa na fama da rashin isassun kayayyakin more rayuwa kama daga kan magudanar ruwa, magudanan ruwa da ake da su a lokuta da yawa suna cike da sharar gida, tare da hana kwararar ruwa yadda ya kamata. Gaggawa da fadada birane ba tare da ka’ida ba ya haifar da gine-gine a yankunan da ke fama da ambaliyar ruwa, wanda hakan ya rage wa kasa karfin shan ruwan da take yi.

“Yanke ciyayi don noma da bunkasa ya rage karfin da kasa ke da shi na rike ruwan sama, da kara kwararar kasa da hadarin ambaliya.

“Gwamnatin tarayya da Majalisar Dokoki ta kasa su sake duba Asusun Samar da Muhalli da ke tarawa Jihohi, a halin yanzu ya kai kashi 1.0 na asusun tarayya. Ya kamata a kara yawan lamarin idan aka yi la’akari da tasirin canjin yanayi.”

Fadakarwa

A nata ra’ayin, Babbar Jami’iar Kula Da Shirin Raya kasa ta Majalisar Dinkin Duniya, Cibiyar Muhalli ta Duniya, Shirin Ba da Tallafi (UNDP GEF SGP), Misis Ibironke Olubamise, ta bukaci al’umma da su kasance cikin shiri, tare da daukar darussa daga abubuwan da suka faru a baya, kuma kada su yi la’akari da mummunar tasirin ambaliyar ruwa.

“Dole ne mu inganta dabarunmu kuma mu samar da tsare-tsare na ficewa, gami da gano wasu hanyoyin motsi,” in ji ta.

A cewarta, hakan kuma zai taimaka wajen rage matsin lambar da ake yi wa ayyukan bayar da agajin gaggawa idan ambaliyar ruwa ta afku.

Ta kara da cewa “Yana da matukar muhimmanci a tilasta bin ka’idojin tsaro a cikin al’ummomi don tabbatar da cewa mutane sun bi gargadin farko da shawarwarin da hukumomi suka bayar,” in ji ta.

Olubamise ya jaddada cewa Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta kasa (NEMA) za ta iya tallafa wa al’umma ta hanyar samar da kayan agajin gaggawa domin hasashen yiwuwar afkuwar ambaliya, maimakon jira har sai bala’i ya afku.

“Har ila yau, NEMA za ta iya binciken ilimin gargajiya da ayyukan da al’ummomin tarihi suka yi amfani da su wajen shiryawa da sarrafa ruwan sama mai yawa.

“Ya kamata hukumomin da suka dace su hada irin wadannan ayyukan na asali don tabbatar da cewa an watsa sahihan bayanai, kan lokaci, da isassun bayanai ga al’ummomi.”

Karin Nasiha

Har ila yau, wani malami a Sashen Tsare-tsaren Birane da Yanki na Jami’ar Olabisi Onabanjo, Oluwafemi Odunsi, ya ce tsare-tsaren birane da ake da su a Nijeriya sun tsufa, ba a aiwatar da su ba, kuma sun yi nisa da yanayin zamani.

Ya ce, “Manufofin tsare-tsaren biranen Nijeriya suna da cikakkun bayanai a kan takarda, amma tasirinsu ya raunana ta hanyar cin hanci da rashawa, matsalolin fasaha, rashin kudade da kuma rashin aiki na gwamnati, har yanzu muna da matsugunai masu yawa na yau da kullum, masu unguwanni da gidaje masu zaman kansu saboda yawancin garuruwanmu har yanzu ba su da tsare-tsaren ci gaba.

Wadanda ke da tsare-tsaren ba a aiwatar da su ba. Za mu iya yin nuni ga wasu biranen Legas da Abuja.”

Odunsi ya yi nuni da cewa, ba a magance matsalar ambaliyar ruwa yadda ya kamata ba a manufofin da ake ciki yanzu, saboda babu wata dokar kula da ambaliyar ruwa ko kuma hadewa tsakanin tsare-tsare na birane da tsare-tsaren rage hadarin bala’i.

“A halin yanzu, tsare-tsaren tsare-tsare na biranen kasar nan a halin yanzu ba su magance matsalar ambaliyar ruwa ba, sun kafa ka’idoji ne kawai na takaita ambaliya da wuraren da ake fama da ambaliya, wanda wani bangare ke magance haduran ambaliyan ruwa da fallasa. Haka kuma, babau wata doka ta musamman kan ambaliyar ruwa a matsayin tsarin kula da ambaliyar ruwa a Nijeriya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: da ambaliyar ruwa wadanda suka

এছাড়াও পড়ুন:

2027: ‘Sai bayan babban taron APC Tinubu zai bayyana wanda za su yi takara tare’

Fadar Shugaban Kasa ta ce shugaba Bola Tinubu zai zabi wanda zai yi masa takarar mataimaki a zaben 2027 a hukumance ne kawai bayan a kammala babban taron jam’iyyar APC a 2026.

Kakakin shugaban, Bayo Onanuga ne ya bayyana hakan yayin wata tattaunawarsa da jaridar Daily Trust a ranar Alhamis.

Da yake martani kan dalilin da ya sa fadar shugaban ta yi shiru kan zargin cewa Tinubu na son canza mataimaki a 2027 musamman la’akari da yadda ’yan jam’iyyar ke ta nuna goyon bayansu ga shugaban shi kadai, Onanuga ya ce hakan ba gaskiya ba ne.

Nan da mako biyu za mu yanke shawara kan shigar wa Isra’ila yaƙi — Trump Muna shawartar Trump kada ya shiga yaƙin Iran da Isra’ila — Birtaniya

A cewarsa, “Lokacin da na karanta labarin, na karyata shi saboda ba shi da tushe. A tsarin shugaba mai cikakken iko da Najeriya ke bi, dan takarar shugaban kasa ake fara zaba, shi kuma sai ya zabi wanda zai yi masa mataimaki. Abin da ya faru ke nan a lokacin Buhari – an fara zabensa, sai daga baya shi kuma ya dauki mataimaki. Ba a yin duka biyun a lokaci daya.

“Da zarar INEC ta fitar da jadawalin zabuka, jam’iyya za ta shirya babban taronta, idan aka sake tsayar da shugaban kasa, shi kuma zai zabi mataimakinsa,” in ji Onanuga.

Kazalika, ya kuma yi fatali da tarihin da ake daukowa cewa sau biyu tinubu yana canza mataimaka lokacin da ya yi Gwamna a jihar Legas daga 1999 zuwa 2007, cewa irin haka za ta faru da Kashim Shettima a 2027.

Ya kuma ce jita-jitar da ake yadawa a kan yiwuwar canza Shettima tun ma kafin a fara nuna amincewa da sake takarar Tinubu ba ta da tushe.

Ya ce, “Ba ni da masaniya a kan duk wani sabani tsakanin shugaban kasa da mataimakinsa. Iya abin da na sani shi ne akwai kyakkyawar fahimtar juna da alakar aiki mai kyau a tsakaninsu. Duk maganganun da ake yadawa ba su da maraba da na teburin mai shayi. Mutane na ta fadara maganganun rashin kan gado cewa wai Seyi Tinubu ne ma mataimakin shugaban kasa. Wannan shashanci ne.

“A wannan kasar, mukamin mataimaka ko na gwamna ko na shugaban kasa ba a raba su da ’yan tsegungumin mutane. Ko da ana zaune lafiya babu wata matsala, makunsantansu sai sun kirkiri husuma da labaran karya. Amma iya abin da na sani shi ne babu matsala tsakanin Tinubu da Shettima.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Katolika ta horar da shugabannin al’umma da na addini kan zaman lafiya
  • Kotu ta aike da dan TikTok din da ke wanka a kan titi a Kano gidan yari
  • 2027: ‘Sai bayan babban taron APC Tinubu zai bayyana wanda za su yi takara tare’
  • Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya: Akwai Babban Aiki A Gaban Nijeriya
  • Yadda manoma suka yi addu’ar roƙon ruwa a Zamfara
  • Shugaban Najeriya Ya Kaddamar Da Aikin Samar Da Ruwa Da Kamfanin Sin Ya Gudanar A Birnin Abuja
  • Nijeriya za ta fara fitar ta tataccen mai zuwa Asia — Matatar Dangote
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Kwaso ‘Yan Nijeriya Da Suka Maƙale A Isra’ila Da Iran
  • Ambaliyar Mokwa – Har yanzu muna neman mutum 700 – Gwamnatin Neja