Mun shirya yin sulhu da ’yan bindiga — Gwamnatin Sakkwato
Published: 18th, June 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Sakkwato, ta bayyana cewa ta shirya zama da ’yan bindiga domin tattaunawa idan har suna da niyyar ajiye makamansu su rungumi zaman lafiya.
Wannan bayani ya fito ne daga Hadimi na Musamman kan Harkokin Tsaro na Gwamna Ahmed Aliyu, Kanal Ahmed Usman (mai ritaya).
Sojoji sun raunata shugaban ISWAP na Najeriya, Albarnawi Litar fetur za ta iya komawa N1,000 a Najeriya saboda yakin Isra’ila-Iran – MasanaHadimin ya ce gwamnatin jihar na son tattaunawa don samar da zaman lafiya fiye da ci gaba da tafka yaƙi.
Gwamnatin ta ce a tarihi, an fi samu damar warware rikice-rikice da dama ta hanyar yin sulhu, ba ta hanyar amfani da ƙarfi kaɗai ba.
Saboda haka, jihar za ta iya tattaunawa da duk ’yan bindigar da suka yi niyyar miƙa wuya su dawo cikin al’umma lafiya.
Haka kuma, gwamnatin jihar ta nuna godiya ga Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, shugabannin rundunonin tsaro, da dukkanin jami’an tsaro da ke aiki wajen kare rayuka da dukiyoyin jama’a.
“Muna godiya matuƙa da sadaukarwarsu. Allah Ya jikan jarumanmu da suka rasu, ya bai wa iyalansu haƙuri,” in ji sanarwar.
Gwamnatin ta yaba da shirin da Gwamnatin Tarayya ke yi na tura masu gadi daji domin inganta tsaro.
Amma ta jaddada cewa dole ne a tabbatar da sahihanci da amincewar al’umma wajen ɗaukar aikin.
Ta kuma ce dole ne a sanya masu gadin daji su yi aiki ne ƙarƙashin kulawar hukumomin tsaro domin hana aikata ba daidai ba.
Sanarwar ta ƙara da cewa dole ne a tabbatar da kyakkyawar sadarwa tsakanin masu gadin daji da al’umma.
Ta ce wannan zai taimaka wajen samar da amana da goyon baya daga mutanen da ake son karewa.
Hakazalika, Gwamnatin ta jaddada cewa tana da cikakken ƙudiri wajen samar da zaman lafiya da tsaro ga kowa.
Ta ce ba za ta tsaya ko ta yi ƙasa a guiwa ba wajen tabbatar da tsaro da kwanciyar hankali a faɗin jihar.
Wannan mataki yana nuna cewa gwamnat8i na son yin haɗin gwiwa da al’umma domin samar da dawwamammen zaman lafiya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga gwamnati matsalar tsaro Sakkwato tattaunawa zaman lafiya Gwamnatin ta
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu zai je jaje bayan kisan fiye da mutum 100 a Benuwe
Shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya soke ziyarar aiki da ya shirya zuwa Kaduna, a maimakon haka zai ziyarci Jihar Benuwe domin jajanta wa al’umma sakamakon kashe-kashen da aka samu a jihar a baya-bayan nan.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban ƙasar, Bayo Onanuga ya fitar a ranar Litinin.
Gwamnati ta kasa ɗaukar matakin da ya dace a kan kashe-kashen Benuwe — Atiku Tinubu ya bayar da umarnin binciken hare-haren BenuweKakakin ya ce Shugaba Tinubu zai kai ziyarar ce a ranar Laraba domin duba halin da jihar ke ciki bayan kashe-kashen da aka samu a ’yan kwanakin nan a jihar.
Haka kuma, a yayin ziyarar, shugaba Tinubu zai gana da masu ruwa da tsaki da suka haɗa da sarakuan gargajiya da ’yan siyasa da jagororin addini da shugabannin al’umma da kungiyoyin matasa, da nufin lalubo hanyoyin magance rikicin jihar.
Tuni dai shugaban ya aike da tawagar wakilan Gwamnatin Tarayya a yau da ta ƙunshi Sakataren Gwamnatin Tarayya da Babban Sufeton ’yan sanda da shugabannin hukumomin tattara bayanan sirri ta ƙasa da mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro da shugabannin kwamitsocin tsaro a majalisun dokokin ƙasar.
Fadar shugaban kasar ta ce wata babbar tawagar manyan jami’an tsaron Nijeriya ta isa Jihar Benuwe domin bayar umarnin yadda za a tunkari matsalar rashin tsaron da jihar ke fuskanta da kuma mai do da kwanciyar hankali.
A ƙarshen mako ne dai aka samu munanan hare-haren da suka yi sanadin kashe fiye da mutum 100 a Jihar Benuwe.