Za a dawo da dukkan Alhazai gida ranar 28 ga Yuni – NAHCON
Published: 19th, June 2025 GMT
Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta tabbatar da aniyarta na dawo da dukkan Alhazan Najeriya da ke Saudiyya zuwa ranar 28 ga watan Yunin, 2025.
Rahotanni daga Hukumar NAHCON da ke birnin Makkah na cewa, alhazan Najeriya 6,528 ne suka dawo Najeriya, yayin da Kamfanin Max Air ya kammala jigilar Alhazai jirgi na 16 a ranar Talata.
Wata sanarwa da Mataimakiyar Daraktan yaɗa labarai Fatima Sanda Usara ta fitar ta ce NAHCON tare da hukumar jin daɗin alhazai ta jiha, da kuma masu jigilar jiragen sama na shekarar 2025 suna yin duk abin da za su iya don ƙara saurin jigilar.
“Hukumar ta shirya dawo da dukkan alhazan nan da ranar 28 ga watan Yuni 2025 kuma ta ci gaba da zage damtse don jigilar.
“A cikin wannan lokaci, dukkan ƙasashen suna ƙoƙarin dawo da alhazansu a lokaci guda, kuma hakan ya haifar da tsananin buƙatar filayen jiragen sama.
“Waɗannan gurbi na Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Sama (GACA) da ke Saudi Arabiya ne ke kula da su, kuma a halin yanzu, ba a ware wa Nijeriya gurabe masu yawa kamar yadda ake buƙata domin tafiyar da alhazai masu yawa cikin gaggawa.
“Saboda haka, manyan masu ruwa da tsaki a harkar sufurin jiragen sama guda uku sun tsara dabarun ƙara yawan wuraren da za a samu a ƙasar.
“Ana fatan tattaunawa mai ƙarfi da mahukuntan Saudiyya za ta taimaka wajen ƙara yawan filayen jiragen.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON Saudiyya
এছাড়াও পড়ুন:
INEC za ta fara rajistar ƙuri’a a ranar 18 ga Agusta
Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC), za ta fara rajistar ƙuri’a ta intanet a ranar 18 ga watan Agusta, 2025, domin tunkurar zaɓen 2027.
Shugaban hukumar, Farfesa Mahmood Yakubu, ne ya bayyana hakan yayin wata ziyarar ban girma da Hukumar NOA ta masa a hedikwatar INEC da ke Abuja.
Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansaninta a Kebbi Ɗaliban da aka sace a Binuwai sun kuɓutaYa kuma ce sai a ranar 25 ga watan Agusta, 2025 za a fara rajistar ƙuri’a a zahiri.
“Za a fara rajistar ƙuri’a ta Intanet a faɗin ƙasa daga ranar 18 ga watan Agusta,” in ji Farfesa Yakubu.
“Rajistar ƙuri’ar a zahiri kuma za ta fara daga 25 ga watan Agusta, 2025,” a cewarsa.
Hukumar INEC na shirin fara wannan rajista ne domin zaɓen gwamnan Jihar Anambra da za a yi a ranar 8 ga watan Nuwamba, 2025, da kuma babban zaɓen 2027.
INEC da NOA sun amince da ci gaba da yin haɗin gwiwa a fannin wayar da kai game da harkokin zaɓe da amfani da ƙirƙirarriyar fasaha (AI) don bunƙasa harkokin zaɓe.
“Ayyukan gudanar da zaɓe ba za su yi tasiri ba sai an wayar da kan ‘yan ƙasa, kuma wannan shi ne babban aikin NOA a Najeriya,” in ji Farfesa Yakubu.
Shugaban NOA, Malam Lanre Issa-Onilu, ya ce suna kan aikin yin gyara da sabunta ayyukansu domin amfanar da dimokuraɗiyya.
Ya ce yanzu NOA na da sassa 16 da ke kula da shirye-shirye, ciki har da sabuwar Ma’aikatar Koyar da Darusan Dimokuraɗiyya.
“A yanzu muna da sassa 16, ciki har da sabuwar Ma’aikatar Koyar Darusan Dimokuraɗiyya,” in ji shi.
INEC ta buƙaci NOA ta ci gaba da amfani da kafafen watsa labarai da na zamani don jawo hankalin mata, matasa da nakasassu don shiga harkokin zaɓe.