Aminiya:
2025-06-19@19:02:39 GMT

Za a dawo da dukkan Alhazai gida ranar 28 ga Yuni – NAHCON

Published: 19th, June 2025 GMT

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta tabbatar da aniyarta na dawo da dukkan Alhazan Najeriya da ke Saudiyya zuwa ranar 28 ga watan Yunin, 2025.

Rahotanni daga Hukumar NAHCON da ke birnin Makkah na cewa, alhazan Najeriya 6,528 ne suka dawo Najeriya, yayin da Kamfanin Max Air ya kammala jigilar Alhazai jirgi na 16 a ranar Talata.

Kotu ta ba da belin Natasha kan N50m kan zargin bata sunan Akpabio Ba Atiku kaɗai ba ne matsalar PDP — Gwamna Lawal

Wata sanarwa da Mataimakiyar Daraktan yaɗa labarai Fatima Sanda Usara ta fitar ta ce NAHCON tare da hukumar jin daɗin alhazai ta jiha, da kuma masu jigilar jiragen sama na shekarar 2025 suna yin duk abin da za su iya don ƙara saurin jigilar.

“Hukumar ta shirya dawo da dukkan alhazan nan da ranar 28 ga watan Yuni 2025 kuma ta ci gaba da zage damtse don jigilar.

“A cikin wannan lokaci, dukkan ƙasashen suna ƙoƙarin dawo da alhazansu a lokaci guda, kuma hakan ya haifar da tsananin buƙatar filayen jiragen sama.

“Waɗannan gurbi na Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Sama (GACA) da ke Saudi Arabiya ne ke kula da su, kuma a halin yanzu, ba a ware wa Nijeriya gurabe masu yawa kamar yadda ake buƙata domin tafiyar da alhazai masu yawa cikin gaggawa.

“Saboda haka, manyan masu ruwa da tsaki a harkar sufurin jiragen sama guda uku sun tsara dabarun ƙara yawan wuraren da za a samu a ƙasar.

“Ana fatan tattaunawa mai ƙarfi da mahukuntan Saudiyya za ta taimaka wajen ƙara yawan filayen jiragen.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON Saudiyya

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Yadda Cin Ganyayyaki Ke Yi Wa ‘Yan Najeriya Wahala

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Karancin kayan ganyayyaki na cigaba da barazana ga lafiyar ‘yan Najeriya.

 

Masana sun bayyana cewa akwai gibi mai girma na rashin kayan ganyayyaki da ya kamata cike.
Sai dai hakan na fuskantar tasgaro sakamakon wasu dalilai.

NAJERIYA A YAU: Dalilan Durƙushewar Sababbin Sana’o’i Tun Ba A Je Ko’ina Ba DAGA LARABA: Dalilan Rashin Jituwa Tsakanin Marasa Lafiya Da Jami’an Kiwon Lafiya

Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne kan wannan matsala da zummar nemo hanyoyin magance ta.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hisbah ta lalata katan 243 na barasa da wasu kayan maye a Yobe
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Cutar Amosanin Jini Ta Hana Ni Cimma Buri Na
  • Tinubu Ya Kai Ziyara Benuwe Sakamakon Kisan Kiyashi Da Aka Yi Wa Jama’a
  • Ma’aikatan Kwalejin Ilimi ta jihar Kaduna za su tsunduma yajin aiki
  • Iran ta kai hari hedikwatar hukumar leƙen asirin Isra’ila
  • Jirgin alhazai ya yi saukar gaggawa kan barazanar harin bom
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Cin Ganyayyaki Ke Yi Wa ‘Yan Najeriya Wahala
  • Dan shekara 10 ya harbe mahaifinsa ɗan sanda a Anambra
  • Dan shekara 10 ya kashe mahaifinsa ɗan sanda da bindiga