Yaƙin Iran da Isra’ila: Amurka za ta tura jami’anta don tattaunawa da Tehran
Published: 17th, June 2025 GMT
Shugaban Ƙasar Amurka, Donald Trump ya ce yana neman ganin an kawo karshen rikicin nukiliyar ƙasar Iran gaba ɗaya, a yayin da aka shiga kwana na biyar a yaƙin da ya ɓarke tsakanin Iran da Isra’ila.
Trump ya bayyana shirinsa na tura manyan jami’an ƙasarsa zuwa birnin Tehran domin tattaunawa da hukumomin Iran a game da lamarin.
Ya bayyana haka ne a yayin da yake hawa jirgi domin barin ƙasar Kanada, inda ya halarci taron ƙasashen G7.
A yayin taron, shugabannin ƙasahen sun bayyana Iran a matsayin barazana, da bai kamata a bari ta mallaki makaman nukiliya ba. A ɗaya bangaren kuma sun bayyana ’yancin Isra’ila na kare kanta.
Matatar man Isra’ila ta daina aiki bayan harin Iran Sarki ya yi barazanar hana yin Musulunci a garinsa bayan dodanni sun kai wa Musulmi hari NAJERIYA A YAU: Yadda Cin Ganyayyaki Ke Yi Wa ‘Yan Najeriya WahalaTrump wanda ya bar taron tun kafin a kammala ya bayyana cewa abin da ke gabansa na wuce batun tsagaita wuta da Amurka ke nema tsakanin Iran da Isra’ila.
Ya bayyana cewa ƙasashen biyu da a halin yanzu suke ci gaba da yi wa juna luguden bama-bamai ba su sassauta ba, amma ya sha nanata cewa akwai yiwuwar kawo ƙarshen rikicin da wuri, idan Iran ta amince da tayin da Amurka ta yi mata.
Makon jiya ne jiragen Isra’ila suka ƙaddamar da hare-haren ba-zata a Iran inda suka kashe wasu manyan kwamandoji da masana kimiyyar nukiliya.
Isra’ila ta yi iƙirarin karɓe ikon sararin samaniyar Iran, kuma za ta tsananta kai hare-hare a nan gaba.
Hare-haren sun halaka mutane da dama a sassan kasashen biyu.
Rahotanni a cikin dare sun nuna yadda na’urorin tsaron sararin samaniyar Iran ke kakkaɓo makamai a sassan ƙasar.
Rundunar juyin juya halin Musulunci na Iran ta bayyana cewa za ta sake harba tarin rokoki zuwa Isra’ila.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Iran Isra ila makaman nukiliya
এছাড়াও পড়ুন:
Jami’an Tsaron Kan Iyakar Iran Sun Harbo Jiragen Masara Matuka 44 Na Sojojin H.K.Isra’ila
Jami’an tsaron kan iyakokin Iran sun harbo jiragen saman yaki marasa matuki ciki guda 44 a cikin sa’o’i 48 da suka gabata
Kwamandan rundunar tsaron kan iyakokin kasar Iran Birgediya Janar Ahmad Ali Goudarzi ya bayyana cewa: An harbo jiragen sama marasa matuka ciki guda 44 da kananan jiragen saman yakin gwamnatin ‘yan sahayoniyya tare da lalata su a wasu kan iyakokin kasar.
Birgediya Janar Goudarzi ya bayyana a ranar Lahadi cewa: “Bayan harin da gwamnatin ‘yan Sahayoniyya ta kaddamar kan Iran, a cikin sa’o’i 48 da suka gabata, jami’an tsaron Iran sunsamu nasarar kakkabo jiragen sama marasa matuka ciki na gwamnatin ‘yan sahayoniyya guda 44 da kananan jiragen sama na wannan muguwar gwamnati, sakamakon Sanya ido kan shige da ficen kan iyaka ta sararin samaniyya.”
Haka nan kuma yayin da yake ishara da cikakken shirin da dakarun tsaron kan iyakokin kasar suka yi na sa ido da kuma kiyaye iyakokin kasar Iran, ya kara da cewa: Jajirtattun jami’an tsaron kan iyakokin kasar Iran, tare da cikakken shirinsu na kula da tsaron kan iyakokin, sun gargadi dukkan makiya, ‘yan ta’adda, kungiyoyin masu dauke da makamai, da masu fasa kwauri da cewa za su mayar da martani da karfi kan duk wani hari da aka kai kan tsaron kan iyakokin kasar.
Birgediya Janar Goudarzi ya tabbatar da cikakken goyon bayansa ga sauran sojojin kasar, inda ya jaddada sanya ido kan bayanan sirri don tabbatar da tsaron Jamhuriyar Musulunci ta Iran da kuma tunkarar duk wata barazana a kan iyakar.