Yaƙin Iran da Isra’ila: Amurka za ta tura jami’anta don tattaunawa da Tehran
Published: 17th, June 2025 GMT
Shugaban Ƙasar Amurka, Donald Trump ya ce yana neman ganin an kawo karshen rikicin nukiliyar ƙasar Iran gaba ɗaya, a yayin da aka shiga kwana na biyar a yaƙin da ya ɓarke tsakanin Iran da Isra’ila.
Trump ya bayyana shirinsa na tura manyan jami’an ƙasarsa zuwa birnin Tehran domin tattaunawa da hukumomin Iran a game da lamarin.
Ya bayyana haka ne a yayin da yake hawa jirgi domin barin ƙasar Kanada, inda ya halarci taron ƙasashen G7.
A yayin taron, shugabannin ƙasahen sun bayyana Iran a matsayin barazana, da bai kamata a bari ta mallaki makaman nukiliya ba. A ɗaya bangaren kuma sun bayyana ’yancin Isra’ila na kare kanta.
Matatar man Isra’ila ta daina aiki bayan harin Iran Sarki ya yi barazanar hana yin Musulunci a garinsa bayan dodanni sun kai wa Musulmi hari NAJERIYA A YAU: Yadda Cin Ganyayyaki Ke Yi Wa ‘Yan Najeriya WahalaTrump wanda ya bar taron tun kafin a kammala ya bayyana cewa abin da ke gabansa na wuce batun tsagaita wuta da Amurka ke nema tsakanin Iran da Isra’ila.
Ya bayyana cewa ƙasashen biyu da a halin yanzu suke ci gaba da yi wa juna luguden bama-bamai ba su sassauta ba, amma ya sha nanata cewa akwai yiwuwar kawo ƙarshen rikicin da wuri, idan Iran ta amince da tayin da Amurka ta yi mata.
Makon jiya ne jiragen Isra’ila suka ƙaddamar da hare-haren ba-zata a Iran inda suka kashe wasu manyan kwamandoji da masana kimiyyar nukiliya.
Isra’ila ta yi iƙirarin karɓe ikon sararin samaniyar Iran, kuma za ta tsananta kai hare-hare a nan gaba.
Hare-haren sun halaka mutane da dama a sassan kasashen biyu.
Rahotanni a cikin dare sun nuna yadda na’urorin tsaron sararin samaniyar Iran ke kakkaɓo makamai a sassan ƙasar.
Rundunar juyin juya halin Musulunci na Iran ta bayyana cewa za ta sake harba tarin rokoki zuwa Isra’ila.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Iran Isra ila makaman nukiliya
এছাড়াও পড়ুন:
Jagora: Iran Ta Bayyana Karfinta Da Jajircewarta A Yakin Kwanaki 12 Ga Duniya
Jagoran juyin juya halin musulunci a nan Iran Imam Sayyid Aliyul Khaminai, ya bayyana cewa a cikin yakin kwanaki 12 da ya gabata JMI ta bayyanawa duniya karfinta da jajircewar a ga duniya. Da kuma tabbatan JM tayi a kasar.
Kamfanin dillancin labaran Tasnim na kasar Iran ya nakalto jagoran yana fadar haka a lokacinda yake jawabi a taron cika kwanaki 40 da shahadar wadanda suka yi shahada a yankin. Labarin ya kara da cewa mafi yawan wadanda suka halarci tarun iyalan shahidan yakin kwanaki 12 ne da jami’an gwamnati da kuma manya-manyan sojojin kasar da sauran Jama’a.
Jagoran ya kara da cewa, HKI da Amurka basu fadawa JMI da yaki don shirin ta makamashin Nukliya ko don take hakkin bil’adama ba, sai dai dukkan wadan nan wasila ne na yakar Imani da kuma addininku da kuma ci gaban da mutanen Iran suke samu. Har’ila yaum da kuma hadin kan da kuke da shi. Sun kasa raba kan iraniyawa don gwara kansu su su lalata kasarsu da kansu. Ya ce yakin kwanaki 12 da makiya suka dora mana baa bin mamaki bane, bai zo mana ba zata ba, mun san watarana zasu farmana da yaki, kuma yaki ba sabo ne a wajemmu ba, mun yi yakin shekaru 8 mun gamu da tashe-tashen hankula da dama a cikin gida. Ya ce amfanin wannan yakin a wajemmi shi ne duniya da ga ciki har da su makiya sun ga irin karfin da muke da shi. Da kuma irin shirin yaki da muka bayyana.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Mutum daya Yayi Shahada 4 Sun Ji Rauna Sanadiyar Hare-Haren HKI A Lebanon July 29, 2025 EU Tace Zata Dakatar Da HKI Daga Cibiyar Bincikenta Saboda Gaza July 29, 2025 Ma’aikatar Leken Asirin JMI Ta Ce Ta Gano Shirin Kashe Manyan Mutane 35 a kasar July 29, 2025 Najeriya: Likitoci a Lagas Sun Shiga Yajin Aiki July 29, 2025 Wani Dan Majalisar Iran Ya Yi Kira Ga A Yi Siyasar Kin Gabatar Da Bayanai A Tattaunawa Da Kasashen Turai July 29, 2025 Sojojin HKI Sun Ci Gaba Da Kashe Kawunansu July 29, 2025 Kasar Holland Ta Hana MInistocin HKI Biyu Shiga Cikin Kasarta July 29, 2025 Manjo Janar Musawi: Ko Kadan Ba Mu Yarda Da Amurka Ba July 29, 2025 Araqchi: Iran Zata Mayar Da Martanin Da Ba Zai Yiwu A Boye Ba Kan Duk Wani Harin Wuce Gona Da Iri Kanta July 29, 2025 Kasar Iran Ta Musanta Yin Katsalandan A Tattaunawar Neman Tsagaita Bude Wuta A Gaza July 29, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci