Aminiya:
2025-07-08@05:23:45 GMT

Muna shawartar Trump kada ya shiga yaƙin Iran da Isra’ila — Birtaniya

Published: 20th, June 2025 GMT

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer ya buƙaci Donald Trump kada ya ɗauki matakin soji kan Iran, yana mai kiran da a biyo wa lamarin ta hanyar lalama.

Mista Starmer ya ce akwai “mummunan hatsarin bazuwar” yaƙin, inda ya yi kira ga duka ɓangarorin sun rungumi sulhu.

Ba zai yiwu mu bar Khamenei a raye ba — Isra’ila Hisbah ta lalata katan 243 na barasa da wasu kayan maye a Yobe

Ya ƙara da cewa a baya an samu “jerin tattauna masu yawa da Amurka, kuma ina ganin wannan ita ce hanyar warware matsalar.

Kalaman nasa na zuwa ne yayin da sakataren harkokin wajensa, David Lammy ke shirin ganawa da takwaransa na Amurka, Marco Rubio kan yadda za a taƙaita bazuwar yaƙin.

Da maraicen yau Alhamis ne kuma Mista Lammy da Mista Rubio suka gana domin tattauna halin da ake ciki a yankin Gabas ta Tsakiya.

Su ma shugabannin China da na Rasha sun yi Alla-wadai da hare-haren Isra’ila kan Iran tare da kiran a tsagaita wuta.

Shugaba Xi Jinping da Vladimir Putin sun tattauna ta waya inda suka nuna goyon-bayan amfani da hanyoyin diflomasiya wajen shawo kan rikicin.

Ministan Harkokin Wajen Iran, Abbas Aragchi zai tattauna da takwarorinsa na Faransa da Jamus da Birtaniya a Geneva a gobe Juma’a.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Birtaniya Iran Keir Starmer

এছাড়াও পড়ুন:

Amurka za ta ɗauki nauyin ’yan tawaye domin yaƙi da ta’addanci

Ma’aikatar Tsaron Amurka Pentagon ta ware dala miliyan 130 a kasafin kudinta na 2026 karkashin Yaƙi da ISIS da Kudin Kayan Aiki (CTEF) don taimaka wa kungiyoyi masu dauke da makamai a Syria, cikin su har da SDF da YPG ta mamaye.

Wannan dai na zuwa ne a yayin da Siriya ke ci gaba da fuskantar rashin kwanciyar hankali da kalubale masu yawa tun bayan kawo karshen mulkin Bashar al-Assad.

Bidiyon tsiraici: Babiana ta sake jawo ce-ce-ku-ce Madatsar Ruwan Lagdo na yi wa jihohi 3 na Nijeriya barazanar ambaliya

Manyan matsaloli sun haɗa da kasancewar kungiyoyi masu dauke da makamai daban-daban, rikice-rikicen filaye da ba a warware ba, tsoma bakin sojojin ƙasashen waje, da tattalin arziki mai rauni wanda ke fama da talauci da kuma ƙaura ta yawan jama’a.

Gwamnatin rikon kwarya ƙarƙashin jagorancin Ahmed al-Sharaa na fuskantar ƙalubale wajen neman sahihanci da amincewa, tare da barazana daga mabiyan Assad, ragowar mayakan ISIS, da hare-haren ‘yan tawayen.

Akwai kuma damuwa kan rawar da HTS ke takawa — kungiyar da ta jagoranci kifar da mulkin Assad — da kuma yiwuwar ta zama mai mulkin danniya.

Sai dai asu takardu na Ma’aikatar Tsaron Amurka sun kare kasafin kudinta na 2026, inda suka ce kudaden na da manufar horarwa, bayar da kayan aiki, da albashin wata-wata ga SDF da Mayakan Sa Kai na Syria dubu 19 da Amurka ke goya wa baya a Kudu maso Gabashin Syria, tare da wasu abokan aiki a Iraƙi da Lebanon.

Bayanan sun nuna cewa kayayyakin sun haɗa da ƙananan makamai tare da kayan kula da lafiya a kayan gyara, “kuma dawowar ‘yan ta’addar Daesh na barazana ga tsaron Amurka, jama’ar Iraƙi, Syria, Lebanon da ma jama’ar duniya baki ɗaya.’

YPG reshen PKK ne a Syria, kungiyar da Turkiyya, Amurka da Tarayyar Turai suka ayyana a matsayin ta ta’adda, kuma kaso mafi tsoka da Pentagon ta ware a kasafin ya tafi ga ’yan tawayen PKK/YPG.

Daga cikin dala miliyan 130 da aka ware saboda Syria a kasafin kudin Pentagon na 2026, dala miliyan 7.42 za ta tafi ga Mayakan Sa Kai na Syria PKK/YPG, inda bayanan suka ce ana sa ran “kara karfinsu” wajen yaki da gyaran ‘yan ta’addar Daesh a Saharar Badiyah, sai dai kuma mafi yawan kudaden za su tafi ne ga ’yan tawayen SDF.

Kudaden baya-bayan nan na zuwa ne bayan an ba su dala miliyan 147.9 a 2025 da dala miliyan 156 a 2024, duk da sunan yaki da ‘yan ta’addar Daesh, matakin da Turkiyya ta nuna kin amincewa da shi saboda ana fakewa da hakan ana bai wa ‘yan ta’adda makamai a kan iyakarta.

A Ayyukan ta’addancin da ta ɗauki shekaru 40 tana yi, PKK, kungiyar da Turkiyya, Amurka da Tarayyar Turai suka ayyana a matsayin ta ta’adda, ta kashe fiye da mutum 40,000, ciki har da fararen hula, mata, da yara kanana.

Jaridar Kurdistan ta ruwaito Turkiyya nanata cewa bai wa ‘yan ta’addar PKK/YPG makamai ko ma da sunan mene ne, taimaka wa ta’addanci ne kai tsaye.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Amurka za ta ɗauki nauyin ’yan tawaye domin yaƙi da ta’addanci
  • Sojan Isra’ila ya kashe kansa saboda firgicin yaƙin Gaza
  • China Ta Mayar Da Martani Kan Barazanar Trump Na Ƙarin Haraji Ga Kasashen BRICS
  • Trump Ya Yi Barazanar Ƙarin Haraji Ga Ƙasashen Da Suka Rungumi BRICS
  • Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin
  • Elon Musk zai kafa sabuwar jam’iyyar siyasa a Amurka
  • Jaridar Telegraph: Makaman Iran Masu Linzami Sun Sauka Kai Tsaye Akan  Cibiyoyin Sojan Isra’ila Guda 5  
  • Al’ummar Iran Ba Zasu Amince Da Ci Gaba Da Zaman Tattaunawa Da Amurka Ba Saboda Fushin Da Suke Ciki Na Kai Musu Hari
  • Kasar Iran Ta Jaddada Wajabcin Hukunta Gwamnatin Mamayar Isra’ila Dangane Da  Ta’addancinta Kan Iran
  • Kungiyar Hamas Ta Sanar Da Matsayinta Kan Shirin Dakatar Da Bude Tsakaninta Da Gwamnatin Mamayar Isra’ila