Majalisa ta aike wa Tinubu kudurorin dokar haraji domin ya rattaba musu hannu
Published: 18th, June 2025 GMT
Majalisar Dokoki ta kasa ta ce ta aike wa Shugaban Kasa Bola Tinubu kudurorin dokar harajin da ta amince da su a hukumance domin ya rattaba musu hannu su zama doka.
Shugaban Kwamitin Yada Labarai na Majalisar Dattawa, Sanata Yemi Adaramodu (APC, Ekiti) ne ya bayyana hakan yayin wani taron manema labarai ranar Talata a Abuja.
A bara ne dai Tinubu ya aike wa majalisar kudurorin domin su yi nazarinsu sannan su amince da su a matsayin doka.
Ambaliyar Mokwa: Har yanzu muna neman mutum 700 – Gwamnatin Neja DAGA LARABA: Ko Kare Kai Daga Harin ‘Yan Ta’adda Zai Kawo Karshen Matsalar Tsaro?Kudurorin dai a baya sun yamutsa hazo sosai a zaurukan majalisun da ma a fadin kasa, kafin daga bisani majalisun na wakilai da dattawa su amince da su.
Sanata Yemi ya ce, “Eh, yanzu kudurin ya bar hannunmu, yana kan hanyarsa ta zuwa wajen Shugaban Kasa domin ya sanya masa hannu ya zama doka.
“Kudurorin haraji irin wadannan suna bukatar taja da tsifa sosai. Dole bangarorin masana shari’a na zaurukan majalisun biyu su tabbatar kudurorin sun yi daidai da dokokin da ake da su a kasa kafin su tura wa Shugaban Kasa.
“Ba aiki ba ne na kwana biyu ko uku. Bayan an kammala aikin daidaita su kuma Akwun Majalisar Dokoki ta Kasa zai mayar da su kundi daya. Bayan haka ne kawai Shugaban Majalisar Dattawa da ta Wakilai za su sa hannu a aike da su,” in ji Sanatan.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Kudurin dokar haraji
এছাড়াও পড়ুন:
Sin Ta Fara Aiwatar Da Matakin Soke Haraji Kan Kayayyakin Kasashen Afirka 53
Kwanan baya, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya bayyana cewa, kasar Sin ta shirya tsaf wajen aiwatar da soke haraji da kashi 100 bisa 100 a kan kayayyakin kasashen Afirka 53 da suka kulla huldar jakadanci da kasar ta hanyar rattaba hannu kan yarjejeniyar hadin gwiwa a fannin raya tattalin arziki.
A yau, wani jami’in ma’aikatar kasuwancin kasar Sin ya gabatar da wani batu da ya dace da hakan. Inda ya bayyana cewa, a mataki na gaba, ma’aikatar kasuwanci za ta yi aiki tare da sassan da abin ya shafa, wajen inganta kulla yarjejeniyar hadin gwiwa ta fuskar tattalin arziki don samun ci gaba na bai-daya tare da kasashen Afirka bisa ka’idojin tuntubar juna da samun moriyar juna dai-dai-wa-daida. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp