Indomie Arewa Ta Ƙaddamar da AI Career Generator Domin Ranar Yara
Published: 20th, June 2025 GMT
A ranar 27 ga Mayu, 2025, Indomie Arewa ta ƙara ɗanɗano da armashi a cikin tasowar yara. Babban kamfanin abincin tana alfaharin ƙaddamar da Indomie AI Career Generator, wata dandalin zamani irinsa na farkon da aka ƙirƙira don nuna irin baiwar da yara ke da ita ta hanyar ba su damar ganin makomarsu ta wata sabuwar hanya.
Indomie tun da dadewa tana da kaimin ciyarwa da abincin dake gina jiki da kuma cincidar Mafarkin
kowanne yaro. Wannan dandalin na Indomie AI Career Generator ya tunkari wannan manufa, na taimakawa yara su fahimci ƙarfin gwiwarsu, su yi manyan mafarkai, kuma su san cewa makomarsu tana gab da su.
“Indomie ta tallafa wa yarada dama wajen girma, koyo, da zama ababen Alfahari. Tare da wannan Manhajar,
muna ɗaukar wannan goyon baya ne zuwa mataki na gaba. muna taimakawa yara wajen hango makomarsu kuma su haɗa tunaninsu da nasarar da ke gaba.”
— Tawagar Indomie Arewa
Wannan dandali, wanda aka fassara zuwa harshen Hausa, yana amfani da fasahar zamani ta Artificial Intelligence (AI) don haɗa hoton yaro a matsayi da kuma Shiga irinta aikin da ya zaɓa a matsayin mafarkinsa. Sakamakon kuwa shi ne kyakkyawan hoto da zai ba yaron damar ganin kansa a matsayin wanda ya cimma burinsa a nan gaba.
Domin fara amfani da dandalin, iyaye na iya bin hanyoyin da aka saka a kafafen sada zumunta ko su duba
QR code. Bayan haka, za su shigar da sunan yanka na yaron, jinsin sa, zaɓin aikin da yaron ke mafarki, da kuma lambar WhatsApp. Bayan ɗaukar hoton yaron da karɓar sharudda, AI zai sarrafa hoton ya kuma ƙirƙiri hoton aiki mai ƙayatarwa wanda za a iya sauke shi a Watsa a ko ina.
Wannan dandali yana ba yara damar yin murnar baiwarsu, jin daɗin mafarkinsu, da kuma matso dasu kusa da makomarsu ta hanya mai kayatarwa da damar mu’amala.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Rikicin ƙabilanci ya yi ajalin mutum 20 a Chadi
Akalla mutane 20 sun mutu yayin da wasu 16 suka jikkata a wani rikicin ƙabilanci da ya auku a wani lardi na gabashin kasar Chadi.
A cikin wata sanarwa da ma’aikatar sadarwa ta ƙasar ta fitar, ta ce fadan ya barke ne daga ranar 10 zuwa 14 ga watan Yuni a yankin Molou na lardin Ouaddai da ke gabashin kasar.
An garzaya da ’yan Isra’ila 154 asibiti bayan harin Iran Tankokin Isra’ila sun kashe mutum 51 a wurin karbar abinci a GazaWata majiya ta ce rikicin ya samo asali ne bayan da matasan Zaghawa biyu dauke da makamai suka sace babur na wani dan kabilar Ouaddai a ranar Talata, lamarin da ya haddasa kazamin rikici.
Bayanai sun ce rikicin ya yi kamari ne a ranar Asabar lokacin da aka kashe akalla ‘yan kabilar Ouaddai 12 a wani hari da ‘yan kabilar Zaghawa suka kai.
Kazalika, wata sanarwa da suka fitar a birnin N’djamena, ’yan majalisar dokoki 14 na lardin Ouaddai, sun yi Allah wadai da abin da suke danganta da munanan ayyuka, tare da yin kira ga hukumomin kasar da su kara kokarin tabbatar da tsaron lafiya da dukiyoyin ’yan kasar.
Tun dai shekaru da suka wuce ne, gabashin Chadi da ke kan iyaka da Sudan ke fama da rikici tsakanin manoman kabilar Ouaddai da kuma kabilun Larabawa, wadanda makiyaya ne.