Sojojin Nijeriya sun kashe gomman ’yan ta’adda a Tafkin Chadi
Published: 18th, June 2025 GMT
Rundunar sojin Nijeriya ta sanar dakashe gomman ’yan ta’adda na ISWAP da Boko Haram da suka yi ƙoƙarin kutsawa cikin sansanin sojin ruwan ƙasar a yankin Tafkin Chadi.
Hakan dai na kunshe cikin wata sanarwa da rundunar ta wallafa a shafinta na X ranar Laraba wadda ta ce ‘yan ta’addan sun yi ƙoƙarin kutsawa cikin sansanin sojojin ne da misalin ƙarfe 2 na dare, inda suka yi ƙoƙarin lalata sabbin motocin tafiya a fadama waɗanda gwamnatin Jihar Borno ta saya domin yashe hanyoyin ruwa.
Sai dai jami’ai a sansanin sojin ruwan Nijeriya da ke Tafkin Chadin sun jajirce wajen hana su kutsawa, inda aka yi ta musayar wuta har tsawon sama da sa’o’i biyu kafin aka kai musu ɗauki daga Baga, lamarin da ya tilasta wa ‘yan ta’addan ja da baya ba tare da sun kai ga motocin tafiya cikin fadamar ba, in ji sanarwar.
Baya ga kashe gomman ‘yan ta’addan, sanarwar ta ce sojojin sun yi nasarar kwato ababe masu fashewa yayin da wasu daga cikin jam’ian tsaron suka ji rauni.
“Ɓangaren sojin sama [na rundunar] na bin sawun [‘yan ta’addan] a kan ruwa domin ƙara kassara su,” in ji sanarwar.
A makonnin baya bayan nan dai hare-haren ’yan Boko Haram suna ƙoƙarin dawowa arewa maso gabashin Nijeriya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: yan ta addan
এছাড়াও পড়ুন:
Mutuwar majinyata: Asibitin Aminu Kano na roƙon KEDCO ya dawo da wutar lantarki
Asibitin Koyarwa na Aminu Kano (AKTH) ya roƙi Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na KEDCO ya gaggauta dawo masa da wuta bayan rasuwar wasu marasa lafiya da ke samun kulawa ta ceton rayuwada na’ura.
Wata sanarwa da kakakin asibitin, Hauwa Inuwa Dutse ta fitar ta nuna takaici bisa rasuwar marasa lafiyan, tana mai cewa mace-macen waɗanda za a iya kauce wa ne idan akwai tsayayyiyar wutar lantarki.
Ta bayyana cewa Asibitin yana AKTH yakan biya kuɗin wuta akai-akai daga kuɗaɗen shigansa, kuma yana kashe kuɗaɗe wajen sanya mai a janareto domin amfani idan aka ɗauke wuta daga KEDCO.
Don haka, “Hukumar gudanarwar Asibitin AKTH na roƙon Kamfanin KEDCO da ya taimaka wa ayyukan asibitin ta hanyar dawo da wutar a yayin da muke ƙoƙarin biyan ragowar kuɗin wutar,” in ji sanarwar.
Ambaliya: An gano gawar ’yar shekara 3 da ruwa ya tafi da ita a Zariya Gwamnati ta gargaɗi jihohi 11 kan yiwuwar afkuwar ambaliya a wannan makonTa bayyana cewa a yayin da take ƙoƙarin biyan bashin da kamfanin ke bin sa, yana da muhimmanci a fahimci cewa yanke wutar lantarki daga muhimmiyar cibiyar lafiya babbar barazana ce ga majinyata da danginsu.