Sojojin Nijeriya sun kashe gomman ’yan ta’adda a Tafkin Chadi
Published: 18th, June 2025 GMT
Rundunar sojin Nijeriya ta sanar dakashe gomman ’yan ta’adda na ISWAP da Boko Haram da suka yi ƙoƙarin kutsawa cikin sansanin sojin ruwan ƙasar a yankin Tafkin Chadi.
Hakan dai na kunshe cikin wata sanarwa da rundunar ta wallafa a shafinta na X ranar Laraba wadda ta ce ‘yan ta’addan sun yi ƙoƙarin kutsawa cikin sansanin sojojin ne da misalin ƙarfe 2 na dare, inda suka yi ƙoƙarin lalata sabbin motocin tafiya a fadama waɗanda gwamnatin Jihar Borno ta saya domin yashe hanyoyin ruwa.
Sai dai jami’ai a sansanin sojin ruwan Nijeriya da ke Tafkin Chadin sun jajirce wajen hana su kutsawa, inda aka yi ta musayar wuta har tsawon sama da sa’o’i biyu kafin aka kai musu ɗauki daga Baga, lamarin da ya tilasta wa ‘yan ta’addan ja da baya ba tare da sun kai ga motocin tafiya cikin fadamar ba, in ji sanarwar.
Baya ga kashe gomman ‘yan ta’addan, sanarwar ta ce sojojin sun yi nasarar kwato ababe masu fashewa yayin da wasu daga cikin jam’ian tsaron suka ji rauni.
“Ɓangaren sojin sama [na rundunar] na bin sawun [‘yan ta’addan] a kan ruwa domin ƙara kassara su,” in ji sanarwar.
A makonnin baya bayan nan dai hare-haren ’yan Boko Haram suna ƙoƙarin dawowa arewa maso gabashin Nijeriya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: yan ta addan
এছাড়াও পড়ুন:
Mun bankaɗo sabuwar dabarar ’yan sisaya ta satar kuɗi — EFCC
Hukumar EFCC mai yaƙi da masu yi wa tattalin arzikin Nijeriya ta’annati ta ce ta gano wata sabuwar dabarar satar kudi da wasu ’yan siyasa ke amfani da ita a yanzu ta hanyar amfani da ’yan damfara wadanda aka fi sani da ’yan yahoo a fadin kasar.
Shugaban EFCC, Ola Olukoyede na wannan furuci ne yayin ganawa da manema labarai a hedikwatar hukumar da ke Abuja a ranar Litinin.
Tinubu zai je jaje bayan kisan fiye da mutum 100 a Benuwe Gwamnati ta kasa ɗaukar matakin da ya dace a kan kashe-kashen Benuwe — AtikuOlukoyede wanda ya ce wadannan matasa ’yan yahoo da suke zubar da kimar Nijeriya a idon duniya sun kuma faɗa dumu-dumu ta’adar nan ta garkuwar da mutane domin neman kuɗin fansa.
Ya bayyana cewa kaurin suna da ’yan yahoo suka yi a matsayin miyagu sun shafa wa kowane ɗan Nijeriya bakin fenti da duk inda suka shiga ake ɗari-ɗari da su a matsayin masu laifi.
Shugaban na EFCC ya ce a yanzu da zarar miyagun ’yan siyasa sun samu damar yin ruf da ciki a kan dukiyar kasa, sukan haɗa kai da waɗannan matasa ’yan yahoo-yahoo su boye kuɗaɗen a cikin wani asusun yanar gizo da ake kira wallet.
“Sau tari irin waɗannan ’yan siyasa sukan jibge ’yan yahoo a otel-otel su rika buɗe musu asusun ajiya na kirifto su boye biliyoyin kuɗaɗen da suka sata.”
Olukoyede ya buga misali da wani matashi mai shekaru 22 da hukumar ta kama yana yi wa ’yan siyasa irin wannan aika-aikar wanda aka gano ya samu tukwicin Naira biliyan biyar a tsawon watanni 18 kacal.