A yau Alhamis, ma’aikatar cinikayya ta kasar Sin ta bayyana cewa, kasar tana ba da muhimmanci sosai kan kiyaye kwanciyar hankali da tsaron bangaren masana’antu da tsarin samar da kayayyaki a duniya, kana tana kara hanzarta sake duba bukatun samun lasisin fitar da kayayyakin ma’adanai na “rare earth” masu daraja da ake sarrafa kayayyakin fasaha da su kamar yadda yake kunshe a tanade-tanaden dokoki da ka’idoji masu alaka da hakan.

Mai magana da yawun ma’aikatar He Yadong, ya bayyana a wani taron manema labarai lokacin da yake amsa wata tambaya kan fitar da ire-iren wadannan ma’adanan cewa, kasar Sin ta amince da wasu bukatun da suka dace bisa doka, kuma za ta ci gaba da karfafa sake nazari da amincewa da ire-iren wadannan bukatun.

Har ila yau, ya ce, kasar Sin ta ci gaba da zantawa da kungiyar tarayyar Turai a matakai daban-daban ba tare da jinkiri ba, don karfafa bunkasa hadin gwiwar cinikayya da zuba jari mai inganci ba tare da tangarda ba. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Kano Ta Aika Dalibai 588 Zuwa Jihohin Arewa 13 A Karkashin Shirin Musanya

Gwamnatin jihar Kano ta aika dalibai 588 zuwa jihohin Arewa 13 a karkashin shirin musayar dalibai na shekarar 2025/2026.

 

An kai daliban zuwa jihohinsu da suka hada da Adamawa, Bauchi, Gombe, Jigawa, Katsina, Kebbi, Taraba, da Nasarawa. Bugu da kari, an kai dalibai daga Yobe, Kaduna, Sokoto, Borno, da Kwara lafiya zuwa inda suke, yayin da wasu dalibai 78 kuma za a kwashe su zuwa jihohin Neja da Benue a ranar 30 ga Satumba, 2025.

 

Kano dai na daya daga cikin jihohin Arewa 19 da ke halartar wannan shiri, wanda aka tsara shi domin inganta hadin kan kasa, hadewa da fahimtar al’adu tsakanin jahohin mambobin kungiyar.

 

Da yake jawabi ga manema labarai bayan tafiyar da daliban, kwamishinan ilimi, Dakta Ali Haruna Makoda, wanda Daraktan sa ido da tantancewa, Auwal Muhammad Mustapha ya wakilta, ya jaddada kudirin gwamnati na tabbatar da tsaro da walwalar daliban.

 

“Mai girma Gwamna, yana ba mu dukkan kayan aiki da tallafin kudi don saukaka ayyukanmu da kuma tabbatar da cewa an kai daliban jihohinsu lafiya,” inji shi.

 

Dakta Makoda ya kuma yabawa iyaye da masu ruwa da tsaki bisa hadin kai da goyon bayan da suke bayarwa wajen ganin shirin ya samu nasara.

 

COV/Khadija Aliyu

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Yahudawa Suna Ci Gaba Da Yin Hijira Zuwa Wajen HKI
  • Gwamnatin Kano Ta Aika Dalibai 588 Zuwa Jihohin Arewa 13 A Karkashin Shirin Musanya
  • NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawa Na 2025
  • An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 
  • Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • Gwamnati ta fara duba yara marasa galihu kyauta a asibitin Aminu Kano
  • Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban
  • Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire
  • Taron Doha: Daga matakin Allawadai zuwa matakan kalubalantar laifukan Isra’ila
  • Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin