A yau Alhamis, ma’aikatar cinikayya ta kasar Sin ta bayyana cewa, kasar tana ba da muhimmanci sosai kan kiyaye kwanciyar hankali da tsaron bangaren masana’antu da tsarin samar da kayayyaki a duniya, kana tana kara hanzarta sake duba bukatun samun lasisin fitar da kayayyakin ma’adanai na “rare earth” masu daraja da ake sarrafa kayayyakin fasaha da su kamar yadda yake kunshe a tanade-tanaden dokoki da ka’idoji masu alaka da hakan.

Mai magana da yawun ma’aikatar He Yadong, ya bayyana a wani taron manema labarai lokacin da yake amsa wata tambaya kan fitar da ire-iren wadannan ma’adanan cewa, kasar Sin ta amince da wasu bukatun da suka dace bisa doka, kuma za ta ci gaba da karfafa sake nazari da amincewa da ire-iren wadannan bukatun.

Har ila yau, ya ce, kasar Sin ta ci gaba da zantawa da kungiyar tarayyar Turai a matakai daban-daban ba tare da jinkiri ba, don karfafa bunkasa hadin gwiwar cinikayya da zuba jari mai inganci ba tare da tangarda ba. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Wasu Kungiyoyi Sun Yi Kira Ga Dan Majalisa Aminu Sani Jaji Ya Fito Takarar Gwamnan Zamfara 

Shima da yake gabatar da nasa jawabin, shugaban jam’iyyar APC magoya bayan Aminu Sani Jaji a Zamfara, Honorabul Lawalli Attahiru Dogon Kade, ya bayyana dan majalisar a matsayin Mutum jajirtacce mai hannun kyauta da taimakon jama’a, inda ya ce mutum irin Aminu Sani Jaji ake nema a matsayin Gwamnan Zamfara, domin shi kadai ne zai kai jihar ga tudun mun tsira.

 

Lokacin da ya ke zantawa da manema labarai jim kadan bayan kammala taron, Honorabul Aminu Sani Jaji, ya gode wa al’ummar Zamfara bisa nuna kauna da yarda da suka yi mishi, inda ya sha alwashin yi musu sakayya akan haka.

 

“Dukkanin abubuwan da muke yi muna yin su ne domin al’umma, kuma jama’ar nan ita taga dacewa ta da in tsaya mata takarar gwamna, babu shakka na amince zan amsa kiran da suka yi mini domin fitar da Jihar Zamfara daga mawuyacin halin da take ciki “ in ji shi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wasu Kungiyoyi Sun Yi Kira Ga Dan Majalisa Aminu Sani Jaji Ya Fito Takarar Gwamnan Zamfara 
  • Gwamna Abdulrazaq Ya Duba Titi Mai Tsawo Kilomita 49
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM
  • Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya
  • Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya
  • An Dawo Da Wutar Lantarki A Dukkan Kauyukan Da Aka Tafka Ruwa Da Iska A Beijing
  • Sauya Sheƙa: Sanatoci Biyu APC Ke Buƙata Wajen Samun Kashi Biyu Cikin Uku A Majalisar Dattawa
  • 2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa
  • Kasar Slovenia Da Haramta Tura Makamai Zuwa Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Sin Ta Samarwa Sassan Kasa Da Kasa Damar Shigowa Ba Tare Da Bukatar Biza Ba