Aminiya:
2025-08-04@18:55:51 GMT

NAJERIYA A YAU: Yadda Tsarin Ilimi Ke Karya Gwiwar ’Yan Najeriya

Published: 20th, June 2025 GMT

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Yan Najeriya da dama ne dai da suka yi ilimin zamani dole ta sa suka rungumi sana’o’in da a baya ake ganin na kaskantattu ne don su samu na sakawa a bakin salati.

Mai yiwuwa hakan ne ya sa wasu, musamman matasa, suka yanke kauna da cewa shafe lokaci ana karatun kan iya taimaka wa mutum magance bukatunsa nay au da kullum.

NAJERIYA A YAU: Yadda Cutar Amosanin Jini Ta Hana Ni Cimma Buri Na DAGA LARABA: Ko Kare Kai Daga Harin ‘Yan Ta’adda Zai Kawo Karshen Matsalar Tsaro?

Wannan shi ne batun da shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi nazari a kai.

Domin sauke shirin, latsa nan

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ma aikatar ilimi ta kasa

এছাড়াও পড়ুন:

Har yanzu ana fama da cutar kwalara a Najeriya – UNICEF

Asusun kula da Ƙananan Yara na Majalisar Ɗinkin Duniya, UNICEF, ya ce Najeriya ce ƙasa ta biyu da aka fi samun ɓullar cutar kwalara a yammacin Afirka da tsakiyar Afirka.

Darektan Hukumar UNICEF mai kula da yammacin Afirka da Afirka ta tsakiya, Gilles Fagninou  ne ya bayyana hakan tare da cewar annobar kwalara ta zama tamfar alaƙaƙai a Najeriya.

Haɗarin tirela ya yi sanadin asarar awaki sama da 100 a Zariya Martani: Har yanzu muna ci gaba da yajin aiki — Ma’aikatan jinya  

“A cewarsa cutar Kwalara na ci gaba da yaɗuwa a Najeriya, inda ƙasar ke fama da ɓarkewar cutar a ‘yan shekarun nan.”

“Ya zuwa ƙarshen watan Yuni, Najeriya ta samu adadin mutane 3,109 da ake zargin sun kamu da cutar kwalara da kuma mutuwar mutane 86 a cikin jihohi 34,” in ji Fagninou.

Jami’in na Majalisar Ɗinkin Duniya ya ƙara da cewa, wannan adadi ya sanya Najeriya ta zama ƙasa ta biyu da cutar ta fi ƙamari a yankin yammacin Afirka da Afirka ta tsakiya kamar yadda aka ambata a baya.

Ya yi nuni da cewa ɓarkewar cutar kwalara a yankin yammaci da Afirka ta Tsakiyar ta haifar da matsala ga yara.

Ya ce, an ƙiyasta kimanin yara 80,000 na fuskantar barazanar kamuwa da cutar kwalara a yammacin Afirka da Afirka ta Tsakiya yayin da aka fara damina a faɗin yankin.

A cewarsa, ruwan sama kamar da bakin kwarya da yawaitar ambaliya da kuma yawan matsugunan su na haifar da haɗarin kamuwa da cutar kwalara da kuma jefa rayuwar yara cikin haɗari.

Ya bayyana cewa cutar kwalara cuta ce mai saurin yaɗuwa ta hanyar abinci ko ruwan da ke gurɓata da ƙwayoyin cuta.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Malamai A Najeriya Suna Goyon Bayan Iran A Yadda Take Fuskantar HKI
  • Najeriya na hasashen samun N300bn a shekara daga noman dabino
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Talauci Ke Hana Shayar Da Yara Nonon Uwa Zalla A Najeriya
  • Sake zaɓen Tinubu zai lalata makomar Najeriya — El-Rufai 
  • Sojoji sun ceto malamin Jami’a da aka sace a Taraba
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Aiwatar da Shirin Daƙile Sulalewar Kuɗaɗen Haraji
  • Dadiyata: Buhari ya gaza nemo shi, Tinubu yana da lokaci — Amnesty
  • Etsu Nupe Ya Jaddada Buƙatar Sama Wa Sarakunan Gargajiya Gurbi A Tsarin Mulki
  • Ma’aikatan jinya sun dakatar da yajin aiki a faɗin Najeriya
  • Har yanzu ana fama da cutar kwalara a Najeriya – UNICEF