An shiga zaman ɗar-ɗar yayin da sojoji suka mamaye Gidan Gwamnatin Ribas
Published: 19th, March 2025 GMT
Mazauna sun shiga zaman ɗar-ɗar a yayin da motocin yaƙi na sojoji suka mamaye Gidan Gwamnatin Jihar Ribas.
Wannan dai na zuwa ne jim kaɗan bayan Shugaba Bola Tinubu ya ayyana dokar ta ɓaci a jihar.
Shugaban Dattawan Arewa ya ajiye sarautar Magajin Rafin Zazzau Tinubu ya sanya dokar ta-baci a Jihar RibasWata majiya ta shaida wa Aminiya cewa fiye da motocin soji 10 aka hanga suna sintiri a kan hanyar zuwa gidan gwamnatin yayin da wasu motocin yaƙi masu sulke suka tsaya wuri-wuri a hanyar.
Majiyar ta ce titunan birnin na Fatakwal sun zama fayau a yayin da mazauna suka tsere gidajensu.
Babu tabbaci ko gwamnan da aka dakatar, Similanayi Fubara yana cikin gidan gwamnatin a halin yanzu.
Sai dai majiyoyi sun ce akwai yiwuwar gwamnan ya samu labarin cewa za a ayyana dokar ta ɓacin tun kafin faruwar lamarin.
Bayanai sun ce gwamnan ya shafe tsawon wunin wannan rana ta Talata yana ganawa da ’yan majalisar zartarwarsa.
A halin yanzu dai birnin na Fatakwal ya zama fayau a yayin mazauna da ’yan kasuwa duk sun koma gidajensu.
Dalilin da Tinubu ya ayyana dokar ta ɓacinTinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci a Ribas bayan rikita-rikitar siyasa da jihar ta daɗe tana fama da shi tare da kuma da naɗa wanda zai riƙe muƙamin gwamnan jihar na tsawon wata shida.
Tinubu ya sanar da matakin ne a wani jawabi da ya yi ta kafafen talabijin na ƙasar da yammacin ranar Talata.
A cikin jawabin nasa, Tinubu ya yi nuni da yadda aka rushe ginin majalisar dokokin jihar watanni 18 da suka gabata, wadda aka kasa sake gina ta har zuwa wannan lokaci.
“Jihar ta tsaya cik tun bayan ɓarkewar rikicin siyasar inda aka tauye wa al’ummar jihar hakkinsu na cin moriyar mulkin dimokuraɗiyya.
“Na yi iyakar bakin ƙoƙarina wajen ganin yadda za a magance matsalar to amma duka ɓangarorin sun yi watsi da yunkurin.
“Bayan nazari kan halin da ake ciki a jihar Rivers, ya zama wajibi na yi amfani da sashe na 305 na Kundin Tsarin Mulkin Najeriya na 1999.
“A kan haka, na ayyana dokar ta-ɓaci daga yau 18 ga watan Maris, 2025.
“Da wannan bayani, gwamnan jihar Rivers, Siminalayi Fubara da mataimakiyarsa Mrs Ngozi Odu da kuma dukkanin zaɓaɓbun ƴanmajalisar dokokin Jihar Ribas, an dakatar da su na wata shida, a matakin farko.
“A halin yanzu, na naɗa Vice Admiral Ibokette Ibas a matsayin wanda zai gudanar da lamurran jihar, domin amfanin al’ummar jihar,” in ji Tinubu.
Sai dai a cikin jawabin nasa, Tinubu ya bayyana cewa wannan doka da ya ƙaƙaba ba ta shafi ɓangaren shari’a na jihar ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Dokar Ta Ɓaci Jihar Ribas Siminalayi Fubara a ayyana dokar ta
এছাড়াও পড়ুন:
MAAUN: Ƙungiyar iyaye ta musanta zargin ƙara ƙudin yaye ɗalibai a jami’ar
Shugaban Ƙungiyar Iyaye na Jami’ar MAAUN, Alhaji Mustapha Balarabe, ya ƙaryata rahotannin da ke cewa jami’ar ta yanke wasu kuɗi masu yawa domin yaye ɗalibai.
A wata sanarwa da ya fitar tare da sakataren ƙungiyar, Hajiya Habiba Sarki, ya ce koken da aka kai wa PCACC da kuma rahotannin da aka wallafa ba su da tushe.
Sarkin Musulmi ya buƙaci gwamnonin Arewa suke saurarar ƙorafin jama’a ’Yan sanda sun gano zinaren N23m bayan shekara 13 da ɓacewarsu a BornoYa bayyana zargin a matsayin yunƙurin ɓata wa jami’ar suna.
Ya ce MAAUN na daga cikin jami’o’in masu zaman kansu mafi sauƙin farashi a Kano, kuma tana ba da ingantaccen ilimi.
“MAAUN na ɗaya daga cikin jami’o’i masu zaman kansu masu sauƙin farashi a Kano, tana ba da ingantaccen ilimi tare da ƙayatattun gine-gine.
“Wasu jami’o’in a jihar suna cajin kuɗin makaranta ninki uku a kan na MAAUN, amma ba a jin kukan kowa game da su. Me ya sa sai MAAUN?
“Idan ɗalibi ya biya kuɗin makaranta na tsawon shekaru huɗu, me ya sa za a ga laifi idan aka nemi ya biya kuɗin yayewa a jami’a mai zaman kanta?
“Wannan ba wani sabon abu ba ne. Wannan batu gaba ɗaya na nuna wata maƙarƙashiya ce da ke nufin ɓata suna da barazana daga wanda ba a san ko waye ba da yake iƙirarin cewa yana kare muradun ɗalibai da iyaye,” in ji shi.
Ya kuma yi tambaya: “Me ya haɗa MAAUN da hukumar PCACC a kan wannan batu?”
A ƙarshe, ya shawarci wanda ya kafa jami’ar da ya ci gaba da jajircewa wajen samar da ilimi mai inganci.
A gefe guda kuma, ya yaba masa saboda ƙin ƙara kuɗin makaranta duk da halin matsin tattalin arziƙi da ya sa wasu jami’o’i ƙara ƙudinsu.