Aminiya:
2025-12-11@09:36:42 GMT

An shiga zaman ɗar-ɗar yayin da sojoji suka mamaye Gidan Gwamnatin Ribas

Published: 19th, March 2025 GMT

Mazauna sun shiga zaman ɗar-ɗar a yayin da motocin yaƙi na sojoji suka mamaye Gidan Gwamnatin Jihar Ribas.

Wannan dai na zuwa ne jim kaɗan bayan Shugaba Bola Tinubu ya ayyana dokar ta ɓaci a jihar.

Shugaban Dattawan Arewa ya ajiye sarautar Magajin Rafin Zazzau Tinubu ya sanya dokar ta-baci a Jihar Ribas

Wata majiya ta shaida wa Aminiya cewa fiye da motocin soji 10 aka hanga suna sintiri a kan hanyar zuwa gidan gwamnatin yayin da wasu motocin yaƙi masu sulke suka tsaya wuri-wuri a hanyar.

Majiyar ta ce titunan birnin na Fatakwal sun zama fayau a yayin da mazauna suka tsere gidajensu.

Babu tabbaci ko gwamnan da aka dakatar, Similanayi Fubara yana cikin gidan gwamnatin a halin yanzu.

Sai dai majiyoyi sun ce akwai yiwuwar gwamnan ya samu labarin cewa za a ayyana dokar ta ɓacin tun kafin faruwar lamarin.

Bayanai sun ce gwamnan ya shafe tsawon wunin wannan rana ta Talata yana ganawa da ’yan majalisar zartarwarsa.

A halin yanzu dai birnin na Fatakwal ya zama fayau a yayin mazauna da ’yan kasuwa duk sun koma gidajensu.

Dalilin da Tinubu ya ayyana dokar ta ɓacin

Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci a Ribas bayan rikita-rikitar siyasa da jihar ta daɗe tana fama da shi tare da kuma da naɗa wanda zai riƙe muƙamin gwamnan jihar na tsawon wata shida.

Tinubu ya sanar da matakin ne a wani jawabi da ya yi ta kafafen talabijin na ƙasar da yammacin ranar Talata.

A cikin jawabin nasa, Tinubu ya yi nuni da yadda aka rushe ginin majalisar dokokin jihar watanni 18 da suka gabata, wadda aka kasa sake gina ta har zuwa wannan lokaci.

“Jihar ta tsaya cik tun bayan ɓarkewar rikicin siyasar inda aka tauye wa al’ummar jihar hakkinsu na cin moriyar mulkin dimokuraɗiyya.

“Na yi iyakar bakin ƙoƙarina wajen ganin yadda za a magance matsalar to amma duka ɓangarorin sun yi watsi da yunkurin.

“Bayan nazari kan halin da ake ciki a jihar Rivers, ya zama wajibi na yi amfani da sashe na 305 na Kundin Tsarin Mulkin Najeriya na 1999.

“A kan haka, na ayyana dokar ta-ɓaci daga yau 18 ga watan Maris, 2025.

“Da wannan bayani, gwamnan jihar Rivers, Siminalayi Fubara da mataimakiyarsa Mrs Ngozi Odu da kuma dukkanin zaɓaɓbun ƴanmajalisar dokokin Jihar Ribas, an dakatar da su na wata shida, a matakin farko.

“A halin yanzu, na naɗa Vice Admiral Ibokette Ibas a matsayin wanda zai gudanar da lamurran jihar, domin amfanin al’ummar jihar,” in ji Tinubu.

Sai dai a cikin jawabin nasa, Tinubu ya bayyana cewa wannan doka da ya ƙaƙaba ba ta shafi ɓangaren shari’a na jihar ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Dokar Ta Ɓaci Jihar Ribas Siminalayi Fubara a ayyana dokar ta

এছাড়াও পড়ুন:

Zanga-zanga ta ɓarke kan zargin sojoji da kashe mata a Adamawa

Zanga-zanga ta ɓarke a yankin Numan da ke Jihar Adamawa, kan zargin sojoji da kashe wasu mata a garin Lamurde.

Mata sun fito zanga-zangar ne sakamakon rikicin da ya ɓarke tsakanin kabilu Bachama da Chobo.

An kama wani mutum a Abuja yana ƙoƙarin kai harsasai ga ’yan bindiga a Zamfara Sakkwatawa na murnar kisan da sojoji suka yi wa mataimakin Bello Turji

A lokacin zanga-zangar an ruwaito cewar mata bakwai ne suka mutu sannan wasu 11 suka jikkata.

Shaidu sun ce sojoji sun buɗe musu wuta yayin da suke tare hanya, suna zargin rundunar da goyon bayan wata ƙabila.

Sai dai rundunar Sojin Najeriya ta musanta wannan zargi.

Ta ce dakarun sun yi artabu ne da wasu ‘yan bindiga a yankin, kuma ta ce mutuwar wasu mata biyu ya faru ne sakamakon buɗe wuta da ‘yan bindigar suka yi, ba wai sojoji suka harbe su ba.

Gwamnatin Jihar Adamawa, ta ayyana dokar hana fita na awa 24 a Lamurde domin daidaita al’amura da zaman lafiya.

A Numan, matan da suka sanya riga ɗauke da launin baƙi ne suka fara zanga-zangar a manyan tituna, inda suke neman yi wa waɗanda aka kashe adalci.

An riga an binne wasu daga cikin waɗanda suka rasu, lamarin da ya ƙara haifar da damuwa a tsakanin al’ummar yankin.

Ɗan Majalisa mai wakiltar yankin, Kwamoti Laori, ya yi Allah-wadai da kisan, inda ya ce ya kamata a gudanar da bincike mai zurfi.

Ya buƙaci hukumomin tsaro da su ɗauki matakin da ya dace, tare da tabbatar da zaman lafiya ba tare da tauye haƙƙin ɗan Adam ba.

Mazauna yankin sun ce rigimar ta jefa mutane cikin tsoro, wanda hakan ya sa da dama suka tsare daga gidajensu.

Shugabannin al’umma a yankin, sun yi kira da a yi sulhu domin kaucewa ƙarin tashin hankali.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ba ni da shirin ficewa daga PDP — Gwamnan Bauchi
  • Najeriya da Saudiyya sun rattaba hannu kan yarjejeniyar samar da tsaro
  • Zanga-zanga ta ɓarke kan zargin sojoji da kashe mata a Adamawa
  • Sakkwatawa na murnar kisan da sojoji suka yi wa mataimakin Bello Turji
  • Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara Ta Taya Oluremi Tinubu Murnar Nadin Sarauta a Ile-Ife
  • Australia ta Fara Aiwhatar da Dokar Hana Yara Amfani da Shafukan Sada Zumunta
  • Majalisar Dattawa ta amince Tinubu ya tura sojojin Najeriya zuwa Jamhuriyar Benin
  • Gwamnan Jihar Ribas ya sauya sheka zuwa APC
  • Juyin Mulki: ECOWAS ta ayyana dokar ta-baci a kasashenta
  • Sojoji sun kashe ’yan bindiga 13, sun ceto ’yan kasuwa a Sakkwato