Aminiya:
2025-12-14@19:10:35 GMT

An shiga zaman ɗar-ɗar yayin da sojoji suka mamaye Gidan Gwamnatin Ribas

Published: 19th, March 2025 GMT

Mazauna sun shiga zaman ɗar-ɗar a yayin da motocin yaƙi na sojoji suka mamaye Gidan Gwamnatin Jihar Ribas.

Wannan dai na zuwa ne jim kaɗan bayan Shugaba Bola Tinubu ya ayyana dokar ta ɓaci a jihar.

Shugaban Dattawan Arewa ya ajiye sarautar Magajin Rafin Zazzau Tinubu ya sanya dokar ta-baci a Jihar Ribas

Wata majiya ta shaida wa Aminiya cewa fiye da motocin soji 10 aka hanga suna sintiri a kan hanyar zuwa gidan gwamnatin yayin da wasu motocin yaƙi masu sulke suka tsaya wuri-wuri a hanyar.

Majiyar ta ce titunan birnin na Fatakwal sun zama fayau a yayin da mazauna suka tsere gidajensu.

Babu tabbaci ko gwamnan da aka dakatar, Similanayi Fubara yana cikin gidan gwamnatin a halin yanzu.

Sai dai majiyoyi sun ce akwai yiwuwar gwamnan ya samu labarin cewa za a ayyana dokar ta ɓacin tun kafin faruwar lamarin.

Bayanai sun ce gwamnan ya shafe tsawon wunin wannan rana ta Talata yana ganawa da ’yan majalisar zartarwarsa.

A halin yanzu dai birnin na Fatakwal ya zama fayau a yayin mazauna da ’yan kasuwa duk sun koma gidajensu.

Dalilin da Tinubu ya ayyana dokar ta ɓacin

Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci a Ribas bayan rikita-rikitar siyasa da jihar ta daɗe tana fama da shi tare da kuma da naɗa wanda zai riƙe muƙamin gwamnan jihar na tsawon wata shida.

Tinubu ya sanar da matakin ne a wani jawabi da ya yi ta kafafen talabijin na ƙasar da yammacin ranar Talata.

A cikin jawabin nasa, Tinubu ya yi nuni da yadda aka rushe ginin majalisar dokokin jihar watanni 18 da suka gabata, wadda aka kasa sake gina ta har zuwa wannan lokaci.

“Jihar ta tsaya cik tun bayan ɓarkewar rikicin siyasar inda aka tauye wa al’ummar jihar hakkinsu na cin moriyar mulkin dimokuraɗiyya.

“Na yi iyakar bakin ƙoƙarina wajen ganin yadda za a magance matsalar to amma duka ɓangarorin sun yi watsi da yunkurin.

“Bayan nazari kan halin da ake ciki a jihar Rivers, ya zama wajibi na yi amfani da sashe na 305 na Kundin Tsarin Mulkin Najeriya na 1999.

“A kan haka, na ayyana dokar ta-ɓaci daga yau 18 ga watan Maris, 2025.

“Da wannan bayani, gwamnan jihar Rivers, Siminalayi Fubara da mataimakiyarsa Mrs Ngozi Odu da kuma dukkanin zaɓaɓbun ƴanmajalisar dokokin Jihar Ribas, an dakatar da su na wata shida, a matakin farko.

“A halin yanzu, na naɗa Vice Admiral Ibokette Ibas a matsayin wanda zai gudanar da lamurran jihar, domin amfanin al’ummar jihar,” in ji Tinubu.

Sai dai a cikin jawabin nasa, Tinubu ya bayyana cewa wannan doka da ya ƙaƙaba ba ta shafi ɓangaren shari’a na jihar ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Dokar Ta Ɓaci Jihar Ribas Siminalayi Fubara a ayyana dokar ta

এছাড়াও পড়ুন:

Annabi SAW Ya Zarce Duk Sauran Annabawa Yawan Mu’uzijoji

Wata rana, Abu Huraira (RA) yunwa ta kama shi matuka, har yazu wurin mimbarin Annabi SAW da ke cikin masallacin Annabi, sai ya fadi a wurin, duk wadanda suka zo wurin suka ganshi, sai suce Allah Sarki, wane ba shi da lafiya har sai da Annabi ya zo ya ganshi, sai yace masa, Abu Hurairah kana jin yunwa ko? Sai ya amsa da eh. Take Annabi SAW ya ce masa, biyo ni zuwa daki na. Annabi yasa aka kawo masa nono a dan koko kamar yadda aka saba, Abu Hurairah yana jira a ce masa ya sha, sai Annabi SAW ya ce masa ya kira ‘yan uwansa Ahlul suffati, kuma jama’a ne masu yawa, da isowarsu, Annabi SAW ya sa wa Nonon albarka, suka fara sha, tawaga bayan tawaga, har sai da kowa ya sha ma’ishi, babu wanda ya yi saura sai Annabi SAW da Abu Huraira, sai ya ce, Abu Huraira fara sha iya shanka, sannan ya ci gaba da ce masa, kara sha, kara sha, har sai da Abu Huraira ya ce, na rantse da wanda ya aiko ka, ya ishe ni, sannan Annabi SAW ya karba ya yi Bismillah ya sha sannan ya kare.

Don haka, wata rana, Annabi SAW ya ta shi ya yi kuka yana tuna masoyansa a gaban Sahabbansa, sai suka ce, ya Rasulullah ba mu ne masoyanka ba, sai ya ce, A’a ku Abokaina ne, wadan can sun yi imani da ni, ba suga mu’uzija ko daya ba, ku kuma kun yi imani da ganin irin wannan abu: Nono dan kadan, a shayar da tawaga da shi, ruwa ya fito ta tsakanin ‘yan yatsu, halittarsa mai kyau, sadaukanta, jarumta, Ilimi, fasaha, cika alkawari, Amana, kyauta, ga su nan da yawa ba iyaka.

A yakin Kandak, lokacin da Sayyadina Aliyu ya kashe Amru bin Waddu (mai karfin kasar Larabawa gaba daya a zamanin) bayan ya yi wa Sayyadina Ali rawani, ya ba shi takobin shi sannan ya ce “rabbi la tazarni farda wa anta kairul warisin”, bayan ya kashe shi sai Annabi ya tambaye shi, ya kake jin kanka a yanzu? Sai ya ce, ina jin da za a tattara min mutanen Madina, zan iya kashe su gaba daya! Sai Annabi SAW ya ce masa, to shirya, akwai wani Saurayi sadauki zai fito daga wannan dajin, za ku yi yaki. Bayan fitowar saurayi sadauki, sai ya tambaya, kai ne Ali? wurinka aka turo ni, yau daya ne zai tsira tsakanin ni da kai, bayan gwabzawa, saurayi ya yi wata wujijjiga da Sayyadina Ali, nan take ya ga ne cewa, wannan saurayi ba kowa ba ne face SAW. Don babu wani da ya isa ya yi wa Sayyadina Ali irin haka duk duniya sai Annabi SAW, sai ya fahimci cewa, akwai sama da shi. Fakrurrazi mai Hadisi ne ya fitar da wannan Hadisin.

15 – Annabi Adam da duk ‘ya’yansa Annabawa suna karkashin tutar Annabi Muhammad SAW a ranar Alkiyama: wannan ya tabbatar cewa, duka Annabawa suna kasa da shi. Ya zo cikin Hadisi Annabi SAW yana cewa, “ana sayyadi waladi Adam wala fakr – ni ne shugaban ‘ya’yan Annabi Adam ba alfahari ba”, sabida Manzon Allah SAW, zuciyarsa tana da fuska biyu – yadda yake kallon hadarar Allah da yadda ya ke kallon bayin Allah. Don haka, Annabi SAW in yana gaban Ubangiji, sunan shi “Abdu”, amma in ya taho wurinmu sauran bayi, shugabanmu ne. Annabi Yahya a wurinmu ma, Ubangiji kiranshi ya yi da cewa, “Sayyidan wa hasuran wa nabiyyan minassalihin – Shugaba, katangagge kuma Annabi daga cikin managarta bayi”

A wani wuri kuma, Annabi SAW ya ce, babu wanda zai shiga Aljannah daga Annabawa kafinsa SAW, kuma babu wata al’umma da za ta shiga daga al’ummomin da suka gabata kafin al’ummarsa SAW! Duka wannan saboda albarkar Annabi SAW.

An ruwaito hadisi daga Anas bin Malik yana cewa, manzon Allah SAW ya ce, “ni ne farkon halitta wanda zai fara fita daga kabari idan an tashi al’umma a ranar Alkiyama, ni ne wanda zan wakilce su wurin yin bayani a gaban Ubangiji don kowa ya tsira, ni ne zan yi musu bushara idan gwiwoyinsu sun sage sun ga kamar ba za su tsira ba, tutar godiya tana hannuna, ni ne mafi girman dan Adam a wurin Ubangijina, kuma ba alfahari nake ba, cewa aka yi in fada, “wa amma bini’imati rabbika fahaddis – ka bayyana ni’imomin Ubangijinka a gareka”.

Wannan magana da Annabi ya fada wa Sahabbansa, ita muke kira da Maulidi. A tara Jama’a a fada musu girma da darajar fiyayyen halitta, Annabi Muhammad SAW.

An karbo Hadisi daga Abdullahi bin Abbas yana cewa, wasu daga cikin sahabban Annabi SAW sun taru suna hirar karatu, sai wasu suka ce, ” ittakazallahu Ibrahima kalila – mamakin yadda Allah ya riki Annabi Ibrahim Badadi (Kalila)”, wasu kuma suka ce, “wannan ai ba abin mamaki ba ne, kamar yadda Ubangiji ya yi hira da Annabi Musa, – wakallamallahu Musa taklima,” wasu kuma suka ce, ina kuka bar Annabi Isa, “Kalimatullahi wa ruhuhu – Kalmar Allah kuma ruhinsa yadda ya dace da shi”, wasu kuma Adamu “isdafahu – Allah ya zabe shi”, kuma duk babu wanda ya san Annabi SAW yana jinsu.

Da Annabi SAW, ya fahimci abun na su ya ki kare wa kuma suna shirin fadawa hadari, sai ya fito ya dakatar da su, ya ce musu, na ji duk batutuwanku da hujjojinku, kuma duk abinda kuka fada haka ne! Kun ce, “Annabi Ibrahim Kalilullah, Musa kalimullahi wa najiyyahu, Adamu isdafahu, duka haka ya ke, amma duk ku saurara kuji! Ni Habibullahi ne ba alfahari ba, saboda mukamin na shi ne! Ni nake rike da tutar godiya, ni ne wanda zai yi ceto, ni ne farkon wanda za a karbi cetonsa a ranar Alkiyama, ba alfahari ba! Ni zan fara kwankwasa kofar Aljannah don a bude, sai a bude in shiga, tare da ni akwai Mu’uminai fukara’u.

Don haka, ya tabbata a hadisi, ranar Alkiyama, ana neman ceto, kowa ya dimauce, sai a tafi wurin Annabi Adam, ya ce, ba ni ba, sai a tafi wurin Annabi Musa, shi ma ya ce ba ni ba, a tafi wurin Annabi Isa, shi ma haka, a tafi wurin Annabi Ibrahim shi ma haka, amma dai a tafi wurin Rasulullah SAW.

A ranar Alkiyama, bayan Annabi SAW ya bude kofar shiga Aljannah, Shahidai za su taho zuwa shiga Aljannah, sai a tambayesu, waye ya kira ku? Sai suce Malamai suka gaya mana cewa, mune farko, sai a ce musu, to kubari Malamai su fara shiga; Malamai da jin haka, sai su ta so za su shiga, sai a tambayesu, ku su waye? Sai su ce, mu ne Malamai, to ya aka yi kowa bai zama Malami ba sai ku kadai, sai suce, saboda duk sun tafi wurin neman abinci muka muna wurin koyon ilimi, to ku ba ku cin abinci? Muna ci, wasu ne suka dauki nauyin cin abincinmu, to ku bari masu ciyarwa su fara shiga. Don haka, sai mai ciyarwa ya fara shiga Aljannah, sannan Malami sannan Shahidi.

Annabi SAW, ya kara ce musu, kuma ni ne mafificin mutanen farko da na karshe, ba alfahari ba!

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Dausayin Musulunci Allah Ya Bai Wa Annabi (SAW) Mu’ujizozi Fiye Da 2,000 A Alƙur’ani   December 5, 2025 Dausayin Musulunci Allah Ya Bai Wa Annabi (SAW) Mu’ujizozi Fiye Da 2,000 A Alƙur’ani November 28, 2025 Dausayin Musulunci Allah Ya Tsarkake Iyalan Annabi (SAW) Daga Kazanta November 21, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kashe mai ciki da ɗanta a Kano
  • An kashe mutum 11 da jikkata wasu 29 a bikin Yahudawa a Ostireliya 
  • Me Ke Kawo Yawaitar Juyin Mulki A Nahiyar Afirka?
  • Sojoji sun daƙile harin ’yan ta’adda a Borno
  • Gwamnatin Kano ta haramta kafa hukumar Hisbah mai zaman kanta
  • Farashin Kayan Abinci Na Sauka Yayin Da Bikin Kirsimeti Da Sabuwar Shekara Ke Matsowa
  • Annabi SAW Ya Zarce Duk Sauran Annabawa Yawan Mu’uzijoji
  • ‘Sojojin Najeriya da na Ivory Coast 200 sun shiga domin tsaftace Jamhuriyar Benin’
  • Jam’iyyar PDP ta tabbatar da mutuwar mataimakin Gwamnan Bayelsa
  • An kai hari gidan jami’in ɗan sanda a Yobe