An shiga zaman ɗar-ɗar yayin da sojoji suka mamaye Gidan Gwamnatin Ribas
Published: 19th, March 2025 GMT
Mazauna sun shiga zaman ɗar-ɗar a yayin da motocin yaƙi na sojoji suka mamaye Gidan Gwamnatin Jihar Ribas.
Wannan dai na zuwa ne jim kaɗan bayan Shugaba Bola Tinubu ya ayyana dokar ta ɓaci a jihar.
Shugaban Dattawan Arewa ya ajiye sarautar Magajin Rafin Zazzau Tinubu ya sanya dokar ta-baci a Jihar RibasWata majiya ta shaida wa Aminiya cewa fiye da motocin soji 10 aka hanga suna sintiri a kan hanyar zuwa gidan gwamnatin yayin da wasu motocin yaƙi masu sulke suka tsaya wuri-wuri a hanyar.
Majiyar ta ce titunan birnin na Fatakwal sun zama fayau a yayin da mazauna suka tsere gidajensu.
Babu tabbaci ko gwamnan da aka dakatar, Similanayi Fubara yana cikin gidan gwamnatin a halin yanzu.
Sai dai majiyoyi sun ce akwai yiwuwar gwamnan ya samu labarin cewa za a ayyana dokar ta ɓacin tun kafin faruwar lamarin.
Bayanai sun ce gwamnan ya shafe tsawon wunin wannan rana ta Talata yana ganawa da ’yan majalisar zartarwarsa.
A halin yanzu dai birnin na Fatakwal ya zama fayau a yayin mazauna da ’yan kasuwa duk sun koma gidajensu.
Dalilin da Tinubu ya ayyana dokar ta ɓacinTinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci a Ribas bayan rikita-rikitar siyasa da jihar ta daɗe tana fama da shi tare da kuma da naɗa wanda zai riƙe muƙamin gwamnan jihar na tsawon wata shida.
Tinubu ya sanar da matakin ne a wani jawabi da ya yi ta kafafen talabijin na ƙasar da yammacin ranar Talata.
A cikin jawabin nasa, Tinubu ya yi nuni da yadda aka rushe ginin majalisar dokokin jihar watanni 18 da suka gabata, wadda aka kasa sake gina ta har zuwa wannan lokaci.
“Jihar ta tsaya cik tun bayan ɓarkewar rikicin siyasar inda aka tauye wa al’ummar jihar hakkinsu na cin moriyar mulkin dimokuraɗiyya.
“Na yi iyakar bakin ƙoƙarina wajen ganin yadda za a magance matsalar to amma duka ɓangarorin sun yi watsi da yunkurin.
“Bayan nazari kan halin da ake ciki a jihar Rivers, ya zama wajibi na yi amfani da sashe na 305 na Kundin Tsarin Mulkin Najeriya na 1999.
“A kan haka, na ayyana dokar ta-ɓaci daga yau 18 ga watan Maris, 2025.
“Da wannan bayani, gwamnan jihar Rivers, Siminalayi Fubara da mataimakiyarsa Mrs Ngozi Odu da kuma dukkanin zaɓaɓbun ƴanmajalisar dokokin Jihar Ribas, an dakatar da su na wata shida, a matakin farko.
“A halin yanzu, na naɗa Vice Admiral Ibokette Ibas a matsayin wanda zai gudanar da lamurran jihar, domin amfanin al’ummar jihar,” in ji Tinubu.
Sai dai a cikin jawabin nasa, Tinubu ya bayyana cewa wannan doka da ya ƙaƙaba ba ta shafi ɓangaren shari’a na jihar ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Dokar Ta Ɓaci Jihar Ribas Siminalayi Fubara a ayyana dokar ta
এছাড়াও পড়ুন:
Kamaru: Sojoji da ministoci sun taya ni murnar cin zabe —Issa Tchiroma
Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar adawa a Kamaru, Issa Tchiroma Bakary, ya yi iƙirari cewa ministoci da manyan hafsoshin sojin ƙasar sun taya shi murnar bayan bayyana kansa a matsayin wanda ya lashe zaɓen shugaban ƙasar da aka kammala.
Issa Tchiroma Bakary ya bayyana cewa ministoci da manyan jami’an tsaron da ministocin sun kira shi a waya suna jaddada goyon bayansu da niyyar biyayya ga kundin tsarin mulkin ƙasar da kuma abin da al’umma suka zaɓa.
Ya bayyana haka ne wani a wata sanarwa da ya fitar a ranar Asabar, yana mai nuna godiya ga waɗanda suka goyi bayansa, tare da jaddada cewa wannan lokaci yana da muhimmanci matuka ga kasa.
Ya ce, “Ina godiya daga zuciyata ga ministoci da jami’an gwamnati da suka kira ni kwanan nan domin nuna goyon bayansu. Wannan ba lokaci ba ne na wasa ko lissafi — lokacin ne da makomar ƙasa da zaman lafiya ke cikin haɗari, kowa sai ya zaɓi bangarensa, kuma da dama sun riga sun yi hakan,” in ji shi.
Rashin tsaro: An rufe makarantu sama da 180 a Arewa Ma’aurata 136 sun kashe juna a shekara 4Bakary ya ƙara da cewa wasu manyan hafsoshin soji sun tabbatar masa da cewa suna tare da al’umma, ba tare da la’akari da matsayi ko iko ba.
“Ina godiya ga wasu manyan hafsoshin soji da suka bayyana cewa ba za su ci amanar aikinsu na kare al’umma ba. Ina fatan sauran za su bi sahu nan gaba, domin tarihi zai tuna da waɗanda suka zaɓi al’umma fiye da jin daɗin kansu.”
Ya kuma yi kira ga ’yan jarida da su guji yaɗa labaran karya ko na son zuciya.
“’Yan jarida, kada ku bari a mayar da ku kayan aikin yaɗa labaran da ba su da tushe saboda neman matsayi ko abin duniya. Matasa na kallon ku a matsayin abin koyi — kada ku zama abokan gaba ga al’umma.”
A ƙarshe, Bakary ya yi kira da a haɗa kai da a zauna cikin shiri da kwarin gwiwa.
“Lokaci yana da tsanani, amma kyakkyawan fata ya fi ƙarfi. Mu tashi tsaye, mu haɗa kai, mu kasance cikin shiri. Makomar ƙasar nan tana hannunmu.”
Sai dai har yanzu hukumar zabe ta Kamaru ba ta fitar da sakamakon zaɓen ba.
Ana sa ran nan da ranar 26 ga watan nan da muke ciki hukumar za ta sanar da sakamakon zaɓen da aka gudanar a ƙarshe makon da ya gabata.