Alkaluma daga ma’aikatar masana’antu da fasahar sadarwa ta kasar Sin ko MIIT, sun nuna irin ci gaba bisa daidaito da sashen masana’antun dijital na kasar Sin ya samu a shekarar 2024 da ta gabata, inda a shekarar ta bara sashen ya samu karin kudin shiga da riba.

Alkaluman da MIIT ta fitar a jiya Litinin, sun nuna a baran, sashen ya kudin da ya kai kudin Sin yuan tiriliyan 35, kwatankwacin dalar Amurka tiriliyan 4.

9, wanda hakan ya nuna karuwar kaso 5.5 bisa dari a shekara. Kazalika, jimillar ribar da sashen ya samar ta karu da kaso 3.5 bisa dari a shekara, inda ya kai yuan tiriliyan 2.7.

Bugu da kari, a shekarar ta 2024, karin kimar hajoji da manyan masana’antun kirar na’urori masu kwakwalwa ke samarwa, da na na’urorin sadarwa da sauran kayayyakin laturoni, ya karu da kaso 11.8 bisa dari, karin da ya kai na kaso 8.4 bisa dari kan na shekarar da ta gabace ta.

Fannin samar da manhajoji na kasar, shi ma ya samar da karin ribar kaso 10 bisa dari, inda darajarsa ta kai tiriliyan 13.7. Ana kuma danganta ci gaban fannin da fadadar sashen fasahohin kirkirarriyar basira ko AI, da dandalolin adana bayanai, da sauran sassan hada hadar kasuwanci masu alaka da shi. (Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yan Nijeriya Na Dab Da Fita Daga Halin Kuncin Talauci – Shettima 

Mataimakin shugaban kasar ya bayyana cewa, taron goron gayyata ne na kafa Nijeriya a matsayin cibiyar samar da makamashi tare da sabuntawa a Afirka, sannan kuma sauyin da aka samu na makamashi Nijeriya, ya bayar da damar zuba jari na sama da dala biliyan 410, daga tsakanin yanzu zuwa shekarar 2060.

Ya kara da cewa, “Daga cikin wannan, ana kuma bukatar sama da Naira biliyan 23, domin fadada hanyoyin samar da makamashin da kuma hada miliyoyin ‘yan Nijeriya, wadanda har yanzu suke rayuwa cikin matsalar wutar lantarki, amma yanzu babban burinmu shi ne, samar da tsarin samar da wutar lantarki mai karfin mega wat 277, nan da shekarar 2060. Cikar wannan buri, ya wuce batun zuba hannun jari kadai, domin yana bukatar kirkire-kirkire, bayar da gudunmawa a cikin gida da kuma sadaukarwa.

“Wannan shi ne dalilin da yasa taken taron na bana ya kasance a matsayin, Aiwatar da Manufofin Nijeriya na Farko da Gudanar da Ci gaban Abubuwan Cikin Gida da kuma Samar da Makamashi, yana da matukar muhimmanci. Kazalika, yunkurinmu na dabarun masana’antu a Nijeriya na kira gare mu da mu dage kan makomar hanyoyin samar da makamashi na Afirka a nan gida.”

Ya kara da cewa, a karkashin wannan, an hada sama da dala miliyan 400 na sabbin alkawuran saka hannun jari a bangaren sabunta makamashi mai a Nijeriya.

“Wannan ya hada da na’urorin hasken rana na sola da fanel-fanel, mita ta zamani, batiri da sauran makamantansu. Babu shakka, ana hasashen wadannan kayayyaki za su samar da ayyukan yi kai tsaye sama da 1,500 a fadin jihohi da dama da kuma nuna kwarin gwiwa a duniya, kan shirin samar da makamashi mai tsafta a Nijeriya”.

A nasa bangaren, Ministan Wutar Lantarki, Adebayo Adelabu ya ce; taron NRIP na 2025, ba wani taro ne da kawai aka shirya ba, sai dan shelanta cewa, Nijeriya a shirye take ta jagoranci sauye-sauyen makamashin da ake samu a Afirka.

Taken taron na bana shi ne, ‘Aiwatar da Manufofin Najeriya na Farko’, yana magana ne a kan wani abu mai mai muhimmanci da ya dara masana’antu, wanda ya kunshi jajircewa, kwarewar masana’antu da kuma dorewar tattalin arziki na tsawon lokaci.

“A bangaren samar da wutar lantarki, manufar Najeriya ta farko ta nuna aniyar tabbatar da cewa; zamani na gaba na fasahar samar da makamashi mai inganci, tun daga na’urori masu amfani da hasken rana har zuwa na’urorin adana makamashin batiri da aka baza a fadin kasar, na alfahari tare da dauke da lakabin, “Wanda aka samar a cikin gida Nijeriya’.”

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai Yadda ‘Yan Bindiga Ke Zafafa Hare-hare A Jihohin Arewa Maso Yamma October 17, 2025 Manyan Labarai Afuwar Tinubu Ga Masu Manyan Laifuka: Ta Bar Baya Da Ƙura October 17, 2025 Labarai Ranar Abinci Ta Duniya: NAWIA Ta Tallafawa Mata 114  Da Kayan Aikin Gona A Zamfara October 16, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO
  • An Kara Habaka Sabon Karfin Samar Da Kayayyaki Da Hidimomi Mai Dorewa a Cikin Watannin Tara Na Farkon Bana
  • Marziyeh Jaafari Ta Kafa Tarihi Na Samu Kyautar Kociyar Da Tafi Kwazo A Asiya.
  • ‘Yan Nijeriya Na Dab Da Fita Daga Halin Kuncin Talauci – Shettima 
  • Alkaluman Jin Ra’ayi na CGTN Sun Shaida Amincewar Al’umma Da Karfin Tattalin Arzikin Kasar Sin
  • Xi Jinping Ya Yi Kira Da a Kara Horar Da Kwararrun Masana A Fannin Aikin Gona
  • Za a kafa kamfanin ƙera kayan sola a Kano
  • Kasar Afirka Ta Kudu Ta Jaddada Aniyarta Ta Ci Gaba Da Shari’ar Neman Hukunta Isra’ila Kan Batun Gaza
  • Sashen Cinikayyar Kamfanonin Sarrafa Hajoji Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso 4.7 Bisa Dari Cikin Watanni Tara Na Farkon Shekarar Nan
  • Kaso 92 cikin 100 na ’yan Najeriya ba su iya wanke hannu ba — UNICEF