Sashen Masana’antun Dijital Na Kasar Sin Ya Samu Karin Riba Da Ci Gaba A Shekarar 2024
Published: 19th, March 2025 GMT
Alkaluma daga ma’aikatar masana’antu da fasahar sadarwa ta kasar Sin ko MIIT, sun nuna irin ci gaba bisa daidaito da sashen masana’antun dijital na kasar Sin ya samu a shekarar 2024 da ta gabata, inda a shekarar ta bara sashen ya samu karin kudin shiga da riba.
Alkaluman da MIIT ta fitar a jiya Litinin, sun nuna a baran, sashen ya kudin da ya kai kudin Sin yuan tiriliyan 35, kwatankwacin dalar Amurka tiriliyan 4.
Bugu da kari, a shekarar ta 2024, karin kimar hajoji da manyan masana’antun kirar na’urori masu kwakwalwa ke samarwa, da na na’urorin sadarwa da sauran kayayyakin laturoni, ya karu da kaso 11.8 bisa dari, karin da ya kai na kaso 8.4 bisa dari kan na shekarar da ta gabace ta.
Fannin samar da manhajoji na kasar, shi ma ya samar da karin ribar kaso 10 bisa dari, inda darajarsa ta kai tiriliyan 13.7. Ana kuma danganta ci gaban fannin da fadadar sashen fasahohin kirkirarriyar basira ko AI, da dandalolin adana bayanai, da sauran sassan hada hadar kasuwanci masu alaka da shi. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Karamar Hukumar Agwara ta Jinjinawa Gwamnati Bisa Tabbatar da Tsaron Rayuka da Dukiyoyin Jama’a
Daga Aliyu Lawal
Karamar Hukumar Agwara da ke Jihar Neja ta ce za ta ci gaba da hada kai da Gwamnatin Tarayya ta Jiha Neja wajen tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin jama’arta, musamman masu rauni.
Shugaban Karamar Hukumar, Alhaji Iliyasu Zakari, ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da ya rattaba hannu da kansa, wadda ya rabawa manema labarai a Minna, babban birnin jihar Neja.
Alhaji Iliyasu Zakari, wanda ya jaddada cewa kare rayuka da dukiyoyin jama’a shi ne ginshikin mulkinsa, ya kuma yaba wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu, Mai Ba Shugaban Kasa Shawara Kan Tsaro (NSA) Nuhu Ribadu, hukumomin tsaro da Gwamna Mohammed Umar Bago bisa rawar da suka taka wajen tabbatar da sakin dalibai ɗari da aka sace a makarantar Cocin Saint Mary’s Catholic da ke Papiri.
Alhaji Iliyasu Zakari ya ce: “Muna matuƙar godiya ga Shugaba Tinubu, Gwamna Umar Bago, Mai Ba Shugaban Kasa Shawara Kan Tsaro, Nuhu Ribadu, da jaruman jami’an tsaro bisa jajircewarsu wajen kare lafiyar ’ya’yanmu.”
Shugaban ya kuma yi kira da a ci gaba da yin addu’a da bayar da goyon baya ga hukumomi domin tabbatar da dawowar sauran ɗalibai da malamai da har yanzu ba a same su ba, yana mai cewa: “Muna da yakinin cewa, da irin wannan haɗin kai da kula da tsaro, sauran yara da malamansu za su dawo cikin iyalansu ba da jimawa ba.”
Sai dai Alhaji Iliyasu Zakari ya yi kira ga iyaye, al’ummar Neja da ’yan Najeriya gaba ɗaya da su kwantar da hankalinsu domin Gwamnatin Tarayya da ta Jihar Neja na aiki tare da hukumomin tsaro wajen tabbatar da sakin sauran ɗalibai da malamai da ke tsare a hannun masu garkuwa da mutane.