Sashen Masana’antun Dijital Na Kasar Sin Ya Samu Karin Riba Da Ci Gaba A Shekarar 2024
Published: 19th, March 2025 GMT
Alkaluma daga ma’aikatar masana’antu da fasahar sadarwa ta kasar Sin ko MIIT, sun nuna irin ci gaba bisa daidaito da sashen masana’antun dijital na kasar Sin ya samu a shekarar 2024 da ta gabata, inda a shekarar ta bara sashen ya samu karin kudin shiga da riba.
Alkaluman da MIIT ta fitar a jiya Litinin, sun nuna a baran, sashen ya kudin da ya kai kudin Sin yuan tiriliyan 35, kwatankwacin dalar Amurka tiriliyan 4.
Bugu da kari, a shekarar ta 2024, karin kimar hajoji da manyan masana’antun kirar na’urori masu kwakwalwa ke samarwa, da na na’urorin sadarwa da sauran kayayyakin laturoni, ya karu da kaso 11.8 bisa dari, karin da ya kai na kaso 8.4 bisa dari kan na shekarar da ta gabace ta.
Fannin samar da manhajoji na kasar, shi ma ya samar da karin ribar kaso 10 bisa dari, inda darajarsa ta kai tiriliyan 13.7. Ana kuma danganta ci gaban fannin da fadadar sashen fasahohin kirkirarriyar basira ko AI, da dandalolin adana bayanai, da sauran sassan hada hadar kasuwanci masu alaka da shi. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Limamin Tehran: Idan Abokan Gaba Su Ka Sake Yin Kuskure Akan Iran Za Su Sake Cin Kasa
Limamin Juma’ar Tehran Ayatullah Sayyid Ahmad Khatami ya yi Ishara da yadda tsarin tsaron ‘yan sahayoniya ya rushe a yayin yakin kwanaki 12, yana mai kara da cewa; A wancan yakin na kwanaki 12 an murkushe abokan gaba, don haka idan har su ka sake yin wani gigin to za a sake murkushe su.”
Ayatullah Sayyid Ahmad Khatami ya kuma yi Ishara da jawabin jagoran juyin musulunci na bayan nan da a ciki ya bayyana cewa; Trump da Netanyahu suna cikin wahamin cewa Iran ce aka yi galaba a kanta,amma akasin haka ne ya faru, al’ummar Iran ce ta yi nasara akan Amurka da ‘yan sahayoniya a cikin yakin kwankai 12.
Haka nan kuma limamin na Tehran ya kore cewa; Iran ta aike wa da Amurka wasika, ta hanyar wata kasa, yana mai cewa; Ya kamata su kwana da sanin cewa ba ma aika sako ga Amurkawa wadanda suke cin amanar abokansu ma, kuma ba ma yin tattaunawa da su.
Ayatullah Sayyid Ahmad Khatami ya kuma ce; Ba za mu taba tattaunawa da Amurka ba har sai ta sauta halayyarta, domin abinda Trump yake son fada wa duniya shi ne ya tilasawa Iran zama kan teburin tattaunawa,amma abinda muke fada masa shi ne cewa; wadanda ma su ka gabace ka, daga kan Jimmy Carter har zuwa wadanda su ka biyo bayansu, sun mutu da wannan bakin cikin, kai ma tabbas da wannan bakin cikin za ka shiga kabari.
Ayatullah Sayyid Ahmad Khatami ya kuma ce; Tun tuni jigon da wannan juyin yake bayarsa shi ne cewa; Za ,mu yi yaki, mu kuma mutu,amma ba za mu mika kai ga kaskanci ba.”
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran Da Pakisatan Sun Amince Da Farfado da Layin Dogo Tsakanin Istambul, Tehran Zuwa Islamabad December 5, 2025 Iran Ta Raya Ranar Haramta Takunkuman Bangare Guda A Duniya December 5, 2025 Trump Ya Yabawa Rwanda Da Kongo DMK Kan Sulhuntawa A Yakin Gabancin Kongo December 5, 2025 Najeriya: Tinubu Ya Nada Wasu Karin Jakadu 65, Sanatoci Da Tsoffin Gwamnoni Na Daga Cikinsu December 5, 2025 Shin Ziyarar Putin a Indiya alama ce da ke nuna cewa New Delhi na yin watsi da gargadin Trump? December 5, 2025 Iran Ta Mayar Da Martani Kan Sanarwar Bayan Taron Majalisar Kasashen Yankin Tekun Fasha December 5, 2025 Afirka ta Kudu Za Ta Dauki Hutu Daga Halartar Tarukan G20 A Karkashin Shugabancin Trump December 5, 2025 Microsoft Za Ta Fuskanci Hukunci Kan Taimaka Wa Laifukan Isra’ila A Kan Falasdinawa December 5, 2025 Amurka Tana Sake Yin Bitar Alakar Da Ke Tsakaninta Da Tanzania December 5, 2025 Fadlallah Na Hizbullah Ya Yi Kiran Hadin Kai A Tsakanin Musulmi Da Larabawa Domin Fuskantar Kalubale December 4, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci