Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [11]
Published: 19th, March 2025 GMT
Ibnu Juzai Allah Ya yi masa rahama, ya yi bayanin kushu’i a matsayin wani yanayi na zuciya wanda yake cike da tsoron Allah, da girmamawa, da ƙasƙantar da kai saboda girman Allah Ta’ala. Wannan yana ɗaya daga cikin manyan halayen da ake buƙata a cikin ibada, musamman salla, domin ya zamanto salla ta yi tasiri da amfani a cikin zuciyar bawa.
Ma’anar Kushu’i a Mahangar Ibnu Juzai: Ibnu Juzai ya bayyana kushu’i da wasu manyan sifofi guda uku:
Tsoro (الخوف): Wanda yake nufin jin tsoron Allah a cikin zuciya, wanda ke hana mutum ya yi sakaci ko saɓo.
Kusantar Allah (التقرب إلى الله): Wanda yake nufin yin ibada da zuciya mai tsarki da nufin neman kusanci zuwa ga Allah.
Ƙasƙantar da kai (التذلل لله): Wanda yake nufin fahimtar girman Allah da rusuna Masa da kuma ƙanƙantar da kai a bisa neman yardarsa.
Kushu’i a Cikin Gaɓoɓi: Ibnu Juzai ya ce wannan yanayin da yake cikin zuciya yana bayyana a zahiri ta hanyoyi daban-daban:
Nutsuwa a cikin salla: Wanda yake hana mutum yawan motsi ko wasa da abu a lokacin salla da zai shagaltar da shi daga sallarsa.
Mai da hankali a cikin salla: Wanda ke nufin cewa mutum ya fahimci kowace kalma da yake karantawa, kuma ya ji zurfin ma’anar abin da yake yi.
Rashin waiwaye: Ma’ana, mutum ya zamanto shagala da tunanin duniya ko kallon gefe a lokacin salla.
Kuka da rusunawa Allah: Wannan yana nuna tsananin tasirin kushu’i a zuciyar mai ibada, har ta kai yana kuka saboda tsoron Allah da soyayyarsa.
Dalilan da ke haifar da Kushu’i: Don samun kushu’i mai ƙarfi a cikin salla da sauran ibadu, dole ne mutum ya yi aiki da wasu abubuwa kamar:
Sanin Allah (معرفة الله): Wanda ke nufin mutum ya fahimci sunayen Allah da siffofinsa, hakan na haifar da tsoron Allah da girmamawa gare Shi.
Sanin lahira da azabar Allah: Wannan yana sanya zuciya ta kasance cikin jin tsoron Allah da ƙasƙantar da kai a gabansa.
Guje wa zunubi: Domin aikata zunubi na rage tasirin imanin ɗan’adam, wanda hakan ke hana zuciya samun kushu’i.
Fahimtar ma’anar Alkur’ani da addu’o’in salla: Idan mutum ya fahimci abin da yake karantawa a cikin salla, hakan yana ƙarfafa kushu’insa.
Amfanin Kushu’i: Kushu’i yana da matuƙar muhimmanci ga mai ibada, domin ya na ƙarfafa soyayya da tsoron Allah a zuciya, sannan ya na hana mutum yin sakaci a cikin ibada.
Kushu’i Yana kare mutum daga wasi-wasin Shaiɗan a cikin salla, sannan ya na haifar da ɗaukakar mutum a wurin Allah, saboda Allah ya na son bayinsa masu tawali’u.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Abu Razina Nuhu Ubale Paki Ramadan
এছাড়াও পড়ুন:
Illolin Neman Kudi Ido Rufe Ba Tare Da Kula Da Halal Ko Haram Ba
Sunana Hassana Yahaya Iyayi (Maman Noor) daga Jihar Kano:
Gaskiya ba abu ne mai kyau ba, ka nema ta hanyar halal din ma ya aka kare da kudin yanzu, bale kuma ta hanyar haram. Tsabar son abin duniya ne da rashin tsoron Allah, aji tsoron Allah a nemi halal, a nemi kudi ta tsabtatacciyar hanya.
Sunana Abba Abubakar Yakubu, daga Jos, a Jihar Filato:
Wannan maudu’i ne mai matukar muhimmanci, saboda talauci da son zuciya ya yi wa mutane yawa. Idanun mutane sun rufe, ba sa tunanin ya dace ko bai dace ba. Burinsu kawai shi ne a ina za su samu kudin da za su kashe wutar gabansu, ko kuma su cika burinsu na rayuwa. Lallai kuskure ne babba, a ce mutum ya zama idanunsa sun rufe akan abin duniya, ba ya tsoron Allah akan abin da zai ciyar da iyalinsa. A yayin da mutum ke neman kudi ido rufe, ba ya tunanin lahira ko hakkin wani, ko sakamakon abin da zai same shi, burinsa kawai abin da zai samu. Allah ya sa mu fi karfin zuciyar mu, mu dage da neman halal, mu tsira da mutuncin mu da imanin mu.
Sunana Hauwa Abubakar Sarki:
Lokaci ne da Allah ya kaho mu idan ba kana da shi ba ba za a yi da kai ba. Shi ne dalilin da ya sa wasu mutane suka fada neman kudi ta kowani irin hanya. Abun da za a ce shi ne, mu yi hakuri mu zauna a inda Allah ya aje mu, domin kuwa ba kowa ne Allah ya rubuta yana daga cikin masu arziki ba. Talauci shi ne dalili na farko dake janyo hakan da kuma hangen abun hannun wani, ko nace abun da wani ya samu kai ma kace lallai sai ka samu, wanda hakan ba daidai bane. Mu kasance masu taimako kana mu tsaftace neman mu sai mu ga Allah ya albarkaci abun da zamu samu.
Sunana Aminu Adamu, Malam Maduri, A Jihar Jigawa:
To magana ta gaskiya rashin yadda da kaddara ce ke jawo haka, domin duk mutumin da ya yadda da kaddara ya san duk wani rabon na dukiya ba zai wuce shi ba don haka ba zai bi hanya mara kyau wajen neman kudi ba. Eh to, dalilan dake jawo hakan suna da yawa, to amma jahilci da rashin tsoron Allah, sune a gaba, domin sune suke jawo haka ga mafi yawan mutane. To hanyoyin dai guda biyu ne, na farko neman ilimin addini domin da shi ne za ka san halak da haramin za kuma ka kiyaye su, sai na biyun tsoron Allah, domin koda kana da ilimi sai kana da tsoron Allah za ka kiyaye halak da haramin.
Sunana Hafsat Sa’eed, Jihar Neja:
Taulauci da rashin aikin yi, ga tsadar rayuwa da kullum take karuwa, nauyi na yi wa al’umma yawa suna rasa mafita a rayuwarsu, shi yake haifar da hakan. Wasu kuma son zuciya ne. Kowa ya rika tuna cewa akwai mutuwa, wanda ya yi daidai ya sani, haka ma wanda bai yi ba ya sani.
Sunana Lawan Isma’il (Lisary), Rano, A Jihar Kano:
Neman kudi ya dace, amma ta hanyar halal. Abin da yake kawo hakan talauci da aka jefa al’ummar wannan kasar. Babbar hanyar ita ce, mu ji tsoron Allah muna tuna cewa bawa ba zai taba wuce rabonsa ba. Shawarata a nan ita ce mu tuna cewa babu bawan da zai koma ga ubangijinsa ba tare da ya bar daidai da kwayar zarra na arzikinsa ba, don haka mu tsaya mu nemi halal dinmu domin mu zauna lafiya. Allah ya sa mu dace amin.
Sunana Aisha T. Bello, daga Jihar Kaduna:
Gaskiya wasu talauce ne, wasu kuma san abu duniya ne ya yi masu yawa, shi ya sa suke neman kudi ta kowace hanya. Ni na ga wata da idona wanda har sai da nasa baki, amma na ga ta yi nisa ba ta jin kira. Wai za ta kasar waje neman kudi, babu inda ya fi gida dadi. Shawara ta a nan shi ne, in zamu nemi kudi mu neme shi ta hanya mai kyau, kuma mu kula. Allah ya ba mu dace wa.
Sunana Abubakar Usman Malam Madori:
A yau, yawaitar matsin rayuwa da kalubalen yau da kullum ya sa mutane da dama ke neman kudi ba tare da la’akari da halal ko haram ba. Wani zai nemi hanyar kirki ya samu na halak, amma wasu kuma za su zabi hanyar da ba ta dace ba kamar sata, damfara, ko karuwanci, duka da nufin biyan bukatunsu na yau da kullum. Wannan hali yana da illa ga dabi’a, addini da tsaron al’umma. Idan kowa zai nemi kudi ta kowacce hanya, to rayuwar al’umma za ta zama barazana, domin ba za a samu gaskiya, aminci da mutunci ba. Mu fahimci cewa arziki na gaskiya yana zuwa ne da hakuri, tawakkali, da bin hanyoyi na gaskiya da halal. Duniya ba za ta kare da wahala ba, amma samun riba ta haram tana da sakamako mai muni a nan duniya da lahira.
Sunana Hussy Saniey, daga Katsina:
Rashin tawakkali shi ne linzamin da ke kai wasu mutanen ga aikata haka. Ya kamata a kodayaushe mutane su rika jin tsoron Allah tare da tunawa yana kallonsu a duk wani motsinsu, don haka su kiyaye jikinsu daga haram, domin duk jikin da aka gina da haram ba ya shiga aljanna. Mutane su jajirce a wurin neman halal, duk wanda ya tashi ya nema Allah zai sanya ma shi albarka a cikin neman, a guji cin dukiyar da ba ta da tsarki.
Sunana Nura Garba, Tsanyawa, A Jihar Kano:
Yana da alaka da sauyin zamani da al’umma suke son yin kitsan wance amma basu da gashin wance, ga kuma tarun bukatu marasa manufa, da yanzu sai ka ga mutum yana neman kudi ta kowace hanya don kawai ya sai mota irin ta wani. Abin da yake kawo haka shi ne, rayuwar karya da yin gasa da wasu ke yi, sai rashin godiya ta rufin asiri da cikakkiyar lafiyar da Allah ya bawa dan’adam. Hanyoyin magance hakan yadda da samu da rashin na Allah ne, kuma kowa rabonsa zai ci kafin ya bar duniya, don haka ya kamata al’umma su nemi halak ta halastacciyar hanya.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA