Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [11]
Published: 19th, March 2025 GMT
Ibnu Juzai Allah Ya yi masa rahama, ya yi bayanin kushu’i a matsayin wani yanayi na zuciya wanda yake cike da tsoron Allah, da girmamawa, da ƙasƙantar da kai saboda girman Allah Ta’ala. Wannan yana ɗaya daga cikin manyan halayen da ake buƙata a cikin ibada, musamman salla, domin ya zamanto salla ta yi tasiri da amfani a cikin zuciyar bawa.
Ma’anar Kushu’i a Mahangar Ibnu Juzai: Ibnu Juzai ya bayyana kushu’i da wasu manyan sifofi guda uku:
Tsoro (الخوف): Wanda yake nufin jin tsoron Allah a cikin zuciya, wanda ke hana mutum ya yi sakaci ko saɓo.
Kusantar Allah (التقرب إلى الله): Wanda yake nufin yin ibada da zuciya mai tsarki da nufin neman kusanci zuwa ga Allah.
Ƙasƙantar da kai (التذلل لله): Wanda yake nufin fahimtar girman Allah da rusuna Masa da kuma ƙanƙantar da kai a bisa neman yardarsa.
Kushu’i a Cikin Gaɓoɓi: Ibnu Juzai ya ce wannan yanayin da yake cikin zuciya yana bayyana a zahiri ta hanyoyi daban-daban:
Nutsuwa a cikin salla: Wanda yake hana mutum yawan motsi ko wasa da abu a lokacin salla da zai shagaltar da shi daga sallarsa.
Mai da hankali a cikin salla: Wanda ke nufin cewa mutum ya fahimci kowace kalma da yake karantawa, kuma ya ji zurfin ma’anar abin da yake yi.
Rashin waiwaye: Ma’ana, mutum ya zamanto shagala da tunanin duniya ko kallon gefe a lokacin salla.
Kuka da rusunawa Allah: Wannan yana nuna tsananin tasirin kushu’i a zuciyar mai ibada, har ta kai yana kuka saboda tsoron Allah da soyayyarsa.
Dalilan da ke haifar da Kushu’i: Don samun kushu’i mai ƙarfi a cikin salla da sauran ibadu, dole ne mutum ya yi aiki da wasu abubuwa kamar:
Sanin Allah (معرفة الله): Wanda ke nufin mutum ya fahimci sunayen Allah da siffofinsa, hakan na haifar da tsoron Allah da girmamawa gare Shi.
Sanin lahira da azabar Allah: Wannan yana sanya zuciya ta kasance cikin jin tsoron Allah da ƙasƙantar da kai a gabansa.
Guje wa zunubi: Domin aikata zunubi na rage tasirin imanin ɗan’adam, wanda hakan ke hana zuciya samun kushu’i.
Fahimtar ma’anar Alkur’ani da addu’o’in salla: Idan mutum ya fahimci abin da yake karantawa a cikin salla, hakan yana ƙarfafa kushu’insa.
Amfanin Kushu’i: Kushu’i yana da matuƙar muhimmanci ga mai ibada, domin ya na ƙarfafa soyayya da tsoron Allah a zuciya, sannan ya na hana mutum yin sakaci a cikin ibada.
Kushu’i Yana kare mutum daga wasi-wasin Shaiɗan a cikin salla, sannan ya na haifar da ɗaukakar mutum a wurin Allah, saboda Allah ya na son bayinsa masu tawali’u.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Abu Razina Nuhu Ubale Paki Ramadan
এছাড়াও পড়ুন:
ISWAP ta ɗauki alhakin kashe mutum 26 a Borno
Ƙungiyar ISWAP mai yaƙi da tayar da ƙayar baya a yammacin Afirka, ta ɗauki alhakin harin da ya yi ajalin mutum 26 a Jihar Borno.
Ƙungiyar ta iƙirarin ɗaukar alhakin harin ne a wani saƙo da ta wallafa a shafin Telegram kamar yadda BBC ya ruwaito.
Aminiya ta ruwaito yadda wani abin fashewa da ake zargin bam ne ya kashe aƙalla mutum 26, ciki har da mata da yara a kan hanyar Rann zuwa Gamboru Ngala da ke Jihar Borno.
Lamarin ya faru ne da yammacin ranar Litinin a lokacin da motoci suka tayar da bama-baman da aka ɗana a gefen hanyar, da ya rutsa da maza 16 da mata huɗu da ƙananan yara guda shida.
Ta yi wa saurayinta ƙaryar shekarunta 27 maimakon 47 An dawo da wutar lantarki a Sifaniya da PortugalMajiyoyi, ciki har da wani babba soja, sun tabbatar wa kamfanin dillancin labarai na Anadolu da harin na baya bayan da safiyar ranar Talata.
Sun bayyana cewa waɗanda lamarin ya rutsa da su suna kan hanyarsu ta tafiya Gamboru Ngala ne daga Rann lokacin da suka isa inda ‘yan ta’addan ISWAP suka ɗana bam ɗin.
Bayanai sun ce baya ga mutum 26 da suka mutu, ƙarin mutum uku sun ji munanan raunuka.
“Mun tura wasu masu ba da agajin gaggawa inda lamarin ya auku domin kwashe mutane tare da tabbatar da tsaron sauran fararen-hula a wurin,” kamar yadda wata majiyar sojin da ba ta yarda a bayyana sunanta ba ta shaida wa Anadolu.
Ali Abass, wani ganau wanda ke tafiya a kan hanyar a lokacin da lamarin ya auku, ya ce sojojin da ‘yan sa-kai sun kai waɗanda suka jikkata wani asibiti.
Ya ƙara da cewa ɗaya daga cikin ‘yan’uwansa na cikin waɗanda lamarin ya rutsa da su.
Harin yana zuwa ne yayin da hare-hare ke ƙara ƙaruwa a yankin Tafkin Chadi, inda ‘yan ta’addan Boko Haram da ISWAP ke ƙara ƙaddamar da hare-haren bama-bamai da kwanton-ɓauna kan motocin fararen-hula da na sojoji.
An ba da rahoton hare-hare irin wannan a ranakun 21 ga watan Maris da 12 ga watan Afrilu. Kawo safiyar ranar Talata dai, jami’an tsaro a Borno ba su fitar da wata sanarwa a hukumance game da lamarin ba.