Leadership News Hausa:
2025-12-08@17:15:11 GMT

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [11]

Published: 19th, March 2025 GMT

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [11]

Ibnu Juzai Allah Ya yi masa rahama, ya yi bayanin kushu’i a matsayin wani yanayi na zuciya wanda yake cike da tsoron Allah, da girmamawa, da ƙasƙantar da kai saboda girman Allah Ta’ala. Wannan yana ɗaya daga cikin manyan halayen da ake buƙata a cikin ibada, musamman salla, domin ya zamanto salla ta yi tasiri da amfani a cikin zuciyar bawa.

Ma’anar Kushu’i a Mahangar Ibnu Juzai: Ibnu Juzai ya bayyana kushu’i da wasu manyan sifofi guda uku:

Tsoro (الخوف): Wanda yake nufin jin tsoron Allah a cikin zuciya, wanda ke hana mutum ya yi sakaci ko saɓo.

Kusantar Allah (التقرب إلى الله): Wanda yake nufin yin ibada da zuciya mai tsarki da nufin neman kusanci zuwa ga Allah.

Ƙasƙantar da kai (التذلل لله): Wanda yake nufin fahimtar girman Allah da rusuna Masa da kuma ƙanƙantar da kai a bisa neman yardarsa.

Kushu’i a Cikin Gaɓoɓi: Ibnu Juzai ya ce wannan yanayin da yake cikin zuciya yana bayyana a zahiri ta hanyoyi daban-daban:

Nutsuwa a cikin salla: Wanda yake hana mutum yawan motsi ko wasa da abu a lokacin salla da zai shagaltar da shi daga sallarsa.

Mai da hankali a cikin salla: Wanda ke nufin cewa mutum ya fahimci kowace kalma da yake karantawa, kuma ya ji zurfin ma’anar abin da yake yi.

Rashin waiwaye: Ma’ana, mutum ya zamanto shagala da tunanin duniya ko kallon gefe a lokacin salla.

Kuka da rusunawa Allah: Wannan yana nuna tsananin tasirin kushu’i a zuciyar mai ibada, har ta kai yana kuka saboda tsoron Allah da soyayyarsa.

Dalilan da ke haifar da Kushu’i: Don samun kushu’i mai ƙarfi a cikin salla da sauran ibadu, dole ne mutum ya yi aiki da wasu abubuwa kamar:

Sanin Allah (معرفة الله): Wanda ke nufin mutum ya fahimci sunayen Allah da siffofinsa, hakan na haifar da tsoron Allah da girmamawa gare Shi.

Sanin lahira da azabar Allah: Wannan yana sanya zuciya ta kasance cikin jin tsoron Allah da ƙasƙantar da kai a gabansa.

Guje wa zunubi: Domin aikata zunubi na rage tasirin imanin ɗan’adam, wanda hakan ke hana zuciya samun kushu’i.

Fahimtar ma’anar Alkur’ani da addu’o’in salla: Idan mutum ya fahimci abin da yake karantawa a cikin salla, hakan yana ƙarfafa kushu’insa.

Amfanin Kushu’i: Kushu’i yana da matuƙar muhimmanci ga mai ibada, domin ya na ƙarfafa soyayya da tsoron Allah a zuciya, sannan ya na hana mutum yin sakaci a cikin ibada.

Kushu’i Yana kare mutum daga wasi-wasin Shaiɗan a cikin salla, sannan ya na haifar da ɗaukakar mutum a wurin Allah, saboda Allah ya na son bayinsa masu tawali’u.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Abu Razina Nuhu Ubale Paki Ramadan

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan bindiga ya hallaka mutum 4, sun sace mata 4 a Sakkwato

’Yan bindiga sun kai sabon hari wasu yankuna na Jihar Sakkwato, inda suka kashe mutane huɗu tare da yin awon gaba da mata huɗu.

Wani mazaunin Gatawa, ya shaida wa Aminiya ce harin ya faru ne a daren ranar Asabar, lokacin da ’yan bindiga sama da goma suka shiga garin a kan babura.

Mutum 5 sun rasu sanadin gobara da faɗa wa rijiya a Kano Sojoji sun yi yunkurin juyin mulki a Jamhuriyar Benin

A cewarsa, “Sun ratsa gefen gari suka dinga shiga gida-gida. Sun harbe mutane huɗu; uku sun mutu nan take, na huɗu kuma ya rasu a asibiti.”

Ya ƙara da cewa bayan harin, sojoji sun isa garin wanda hakan ya sa maharan suka tsere, amma duk da haka sun tafi da mata huɗu.

Sai dai ya bayyana cewa akwai wani malamin makaranta, Mustafa Malam Malam, da aka taɓa yin garkuwa da shi a baya.

Duk da cewa an biya kudin fansar Naira miliyan ɗaya da rabi, ba su sake shi ba, daga baya suka kashe shi.

Shugaban Ƙaramar Hukumar Sabon Birni, Alhaji Ayuba Hashimu, ya musanta batun cewa an kai hari masallaci.

Ya ce babu masallacin da aka kai wa hari ko aka kashe limami kamar yadda ake yaɗawa a kafofin watsa labarai.

Shi ma ɗan majalisar yankin, Aminu Boza, ya ce ba su da labarin wani hari da aka kai wa masallaci a yankin.

A wani labarin kuma, ’yan bindiga sun kai hari ƙauyen Shallah da ke mazabar Turba a Ƙaramar Hukumar Isa, inda suka kashe mutum ɗaya.

Daga nan sai suka wuce garin Barkeji, inda suka ƙone rumbunan abinci a daren ranar Asabar.

Ya zuwa yanzu babu wata sanarwar daga rundunar ’yan sandan jihar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rashin Tsaro: Gwamnatin Tarayya ta gaza — Kwankwaso
  • ’Yan bindiga sun hallaka mutum 4, sun sace mata 4 a Sakkwato
  • ’Yan bindiga ya hallaka mutum 4, sun sace mata 4 a Sakkwato
  • Mutum 5 sun rasu sanadin gobara da faɗa wa rijiya a Kano
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan(a) 168
  • Kissoshin rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 167
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 166
  • Venezuela: Ba Mu Tsoron Kaudin Amurka Na Wuce Gona Da Iri
  • Mutum 3 sun mutum yayin haƙar rijiya a Kano
  • Sabuwar Dokar CBN: Nawa Za a Iya Cirewa a ATM da POS?