Leadership News Hausa:
2025-10-18@17:34:08 GMT

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [11]

Published: 19th, March 2025 GMT

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [11]

Ibnu Juzai Allah Ya yi masa rahama, ya yi bayanin kushu’i a matsayin wani yanayi na zuciya wanda yake cike da tsoron Allah, da girmamawa, da ƙasƙantar da kai saboda girman Allah Ta’ala. Wannan yana ɗaya daga cikin manyan halayen da ake buƙata a cikin ibada, musamman salla, domin ya zamanto salla ta yi tasiri da amfani a cikin zuciyar bawa.

Ma’anar Kushu’i a Mahangar Ibnu Juzai: Ibnu Juzai ya bayyana kushu’i da wasu manyan sifofi guda uku:

Tsoro (الخوف): Wanda yake nufin jin tsoron Allah a cikin zuciya, wanda ke hana mutum ya yi sakaci ko saɓo.

Kusantar Allah (التقرب إلى الله): Wanda yake nufin yin ibada da zuciya mai tsarki da nufin neman kusanci zuwa ga Allah.

Ƙasƙantar da kai (التذلل لله): Wanda yake nufin fahimtar girman Allah da rusuna Masa da kuma ƙanƙantar da kai a bisa neman yardarsa.

Kushu’i a Cikin Gaɓoɓi: Ibnu Juzai ya ce wannan yanayin da yake cikin zuciya yana bayyana a zahiri ta hanyoyi daban-daban:

Nutsuwa a cikin salla: Wanda yake hana mutum yawan motsi ko wasa da abu a lokacin salla da zai shagaltar da shi daga sallarsa.

Mai da hankali a cikin salla: Wanda ke nufin cewa mutum ya fahimci kowace kalma da yake karantawa, kuma ya ji zurfin ma’anar abin da yake yi.

Rashin waiwaye: Ma’ana, mutum ya zamanto shagala da tunanin duniya ko kallon gefe a lokacin salla.

Kuka da rusunawa Allah: Wannan yana nuna tsananin tasirin kushu’i a zuciyar mai ibada, har ta kai yana kuka saboda tsoron Allah da soyayyarsa.

Dalilan da ke haifar da Kushu’i: Don samun kushu’i mai ƙarfi a cikin salla da sauran ibadu, dole ne mutum ya yi aiki da wasu abubuwa kamar:

Sanin Allah (معرفة الله): Wanda ke nufin mutum ya fahimci sunayen Allah da siffofinsa, hakan na haifar da tsoron Allah da girmamawa gare Shi.

Sanin lahira da azabar Allah: Wannan yana sanya zuciya ta kasance cikin jin tsoron Allah da ƙasƙantar da kai a gabansa.

Guje wa zunubi: Domin aikata zunubi na rage tasirin imanin ɗan’adam, wanda hakan ke hana zuciya samun kushu’i.

Fahimtar ma’anar Alkur’ani da addu’o’in salla: Idan mutum ya fahimci abin da yake karantawa a cikin salla, hakan yana ƙarfafa kushu’insa.

Amfanin Kushu’i: Kushu’i yana da matuƙar muhimmanci ga mai ibada, domin ya na ƙarfafa soyayya da tsoron Allah a zuciya, sannan ya na hana mutum yin sakaci a cikin ibada.

Kushu’i Yana kare mutum daga wasi-wasin Shaiɗan a cikin salla, sannan ya na haifar da ɗaukakar mutum a wurin Allah, saboda Allah ya na son bayinsa masu tawali’u.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Abu Razina Nuhu Ubale Paki Ramadan

এছাড়াও পড়ুন:

Hukumar Gidan Yarin Kano Ta Tabbatar Da Dauke Abduljabbar Zuwa Abuja

Sanarwar ta ce: “Sauya wurin da aka yi wa fursuna Malam Abduljabbar Nasiru Kabara zuwa daya daga cikin cibiyoyin tsarewa da ke karkashin ikon tarayya hanya ce ta gudanar da aiki ta yau da kullum wacce aka yi bisa ga dokokin aiki da ka’idojin hukumar.”

 

Ta kara da bayanin cewa motsa fursunoni daga cibiyar tsarewa zuwa wata musamman wadanda ke da matakan tsaro daban-daban na daga cikin ayyukan da kundin tsarin mulki ya dora wa hukumar domin tabbatar da ingantaccen tafiyar da fursunoni, gyarawa da kuma dawo da su kan turba.

 

Sanarwar ta kara da cewa: “Canjawa ko sauya wurin fursuna zuwa wata cibiyar gyaran hali mai matakin tsaro daban da wacce ake tsare da shi a baya na daga cikin ayyukan da kundin tsarin mulki ya ba Hukumar Kula da Gidajen Yari, kamar yadda Dokar Hukumar ta 2019 ta tanada.”

 

Sanarwar ta ce: “Ana yanke irin wadannan shawara ne bisa la’akari da abubuwa da dama, ciki har da tsaro, tsarin rarraba fursunoni, samun wurin da ya dace a cibiyoyi, da kuma bukatun gyarawa da farfado da fursuna.”

 

CSC Musbahu ya tabbatar wa jama’a cewa duk da wannan sauya wuri, ana ci gaba da kiyaye dukkan hakkokin Malam Abduljabbar.

 

Ya ce: “An tabbatar wa jama’a cewa walwala da dukkan hakkokin shari’a na Malam Abduljabbar suna nan daram karkashin kariyar doka.”

 

Sanarwar ta kara da cewa: “Wannan sauya wuri ba ya shafar matsayinsa na shari’a, hakkinsa na daukaka kara ko samun damar tuntubar lauyansa.”

 

Jami’in hulda da jama’a ya sake jaddada kudirin hukumar na tabbatar da tsare fursunoni cikin aminci, gyarawa da farfado da su, domin tabbatar da tsaron jiha da kare rayukan jama’a.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Rahotonni Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya October 17, 2025 Manyan Labarai Gwamnatin Kano Ta Kai Ƙarar Ganduje Da Wasu Kotu Kan Zargin Almundahanar N4.4bn October 17, 2025 Manyan Labarai Dantawaye Ya Karɓi Ragamar Aiki A Matsayin Sabon Kwamishinan Ƴansandan Abuja October 17, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hukumar Gidan Yarin Kano Ta Tabbatar Da Dauke Abduljabbar Zuwa Abuja
  • An Kara Habaka Sabon Karfin Samar Da Kayayyaki Da Hidimomi Mai Dorewa a Cikin Watannin Tara Na Farkon Bana
  • Wani mutum ya ƙona tsohuwar budurwarsa a Oyo
  • ‘Yan Nijeriya Na Dab Da Fita Daga Halin Kuncin Talauci – Shettima 
  • Manzon Allah (SAW) Ne Ya Kafa Tushen Wayewar Kai A Duniya
  • Shugaban Kasar Sudan Yana Ziyarar Aiki A Kasar Masar
  • Masu Bincike Na Sin Sun Kera Wani Dan Karamin Mutum Mutumin Hannu Da Zai Taimaka Wajen Gwaje-wajen Kimiyya
  • Miyetti Allah ta dakatar da shugabanninta a jihohi 3
  • Tarayyar Afirka AU, Ta Jingine Samuwar Madagaska Daga Cikin Kungiyar
  • Sashen Cinikayyar Kamfanonin Sarrafa Hajoji Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso 4.7 Bisa Dari Cikin Watanni Tara Na Farkon Shekarar Nan