Leadership News Hausa:
2025-07-04@00:15:58 GMT

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [11]

Published: 19th, March 2025 GMT

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [11]

Ibnu Juzai Allah Ya yi masa rahama, ya yi bayanin kushu’i a matsayin wani yanayi na zuciya wanda yake cike da tsoron Allah, da girmamawa, da ƙasƙantar da kai saboda girman Allah Ta’ala. Wannan yana ɗaya daga cikin manyan halayen da ake buƙata a cikin ibada, musamman salla, domin ya zamanto salla ta yi tasiri da amfani a cikin zuciyar bawa.

Ma’anar Kushu’i a Mahangar Ibnu Juzai: Ibnu Juzai ya bayyana kushu’i da wasu manyan sifofi guda uku:

Tsoro (الخوف): Wanda yake nufin jin tsoron Allah a cikin zuciya, wanda ke hana mutum ya yi sakaci ko saɓo.

Kusantar Allah (التقرب إلى الله): Wanda yake nufin yin ibada da zuciya mai tsarki da nufin neman kusanci zuwa ga Allah.

Ƙasƙantar da kai (التذلل لله): Wanda yake nufin fahimtar girman Allah da rusuna Masa da kuma ƙanƙantar da kai a bisa neman yardarsa.

Kushu’i a Cikin Gaɓoɓi: Ibnu Juzai ya ce wannan yanayin da yake cikin zuciya yana bayyana a zahiri ta hanyoyi daban-daban:

Nutsuwa a cikin salla: Wanda yake hana mutum yawan motsi ko wasa da abu a lokacin salla da zai shagaltar da shi daga sallarsa.

Mai da hankali a cikin salla: Wanda ke nufin cewa mutum ya fahimci kowace kalma da yake karantawa, kuma ya ji zurfin ma’anar abin da yake yi.

Rashin waiwaye: Ma’ana, mutum ya zamanto shagala da tunanin duniya ko kallon gefe a lokacin salla.

Kuka da rusunawa Allah: Wannan yana nuna tsananin tasirin kushu’i a zuciyar mai ibada, har ta kai yana kuka saboda tsoron Allah da soyayyarsa.

Dalilan da ke haifar da Kushu’i: Don samun kushu’i mai ƙarfi a cikin salla da sauran ibadu, dole ne mutum ya yi aiki da wasu abubuwa kamar:

Sanin Allah (معرفة الله): Wanda ke nufin mutum ya fahimci sunayen Allah da siffofinsa, hakan na haifar da tsoron Allah da girmamawa gare Shi.

Sanin lahira da azabar Allah: Wannan yana sanya zuciya ta kasance cikin jin tsoron Allah da ƙasƙantar da kai a gabansa.

Guje wa zunubi: Domin aikata zunubi na rage tasirin imanin ɗan’adam, wanda hakan ke hana zuciya samun kushu’i.

Fahimtar ma’anar Alkur’ani da addu’o’in salla: Idan mutum ya fahimci abin da yake karantawa a cikin salla, hakan yana ƙarfafa kushu’insa.

Amfanin Kushu’i: Kushu’i yana da matuƙar muhimmanci ga mai ibada, domin ya na ƙarfafa soyayya da tsoron Allah a zuciya, sannan ya na hana mutum yin sakaci a cikin ibada.

Kushu’i Yana kare mutum daga wasi-wasin Shaiɗan a cikin salla, sannan ya na haifar da ɗaukakar mutum a wurin Allah, saboda Allah ya na son bayinsa masu tawali’u.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Abu Razina Nuhu Ubale Paki Ramadan

এছাড়াও পড়ুন:

Lakurawa sun kashe mutum 15 a harin ramuwar gayya a Sakkwato

Wasu da ake zargin ’yan ta’addan Lakurawa ne, sun kai hari ƙauyen Kwalajiya da ke Ƙaramar Hukumar Tangaza a Jihar Sakkwato, inda suka kashe mutum 15.

Harin ya faru ne da misalin ƙarfe 2 na ranar Talata, lokacin da mutum ke sallar Azahar.

NAJERIYA A YAU: Ɓoyayyun Ƙalubalen Da Sabuwar Haɗakar ADC Za Ta Iya Fuskanta An sa zare tsakanin ‘yan Kannywood da Alhikima

Rahotanni daga mazauna yankin sun ce harin ramuwar gayya ne bayan da al’ummar ƙauyen suka daƙile wani hari da aka kai musu kwanakin baya, inda suka kashe ’yan ta’addan Lakurawa uku ciki har da wani jagoransu.

A wannan sabon harin, ’yan bindigar sun dawo da yawa inda suka fara harbi kan mai uwa da wabi.

“Muna cikin Masallaci muna sallah suka shigo suka fara harbinmu,” in ji wani mazaunin ƙauyen.

“Sun kashe mazajenmu, sun kuma ƙone kayayyakin abinci da shaguna da gidaje.”

’Yan bindigar sun kuma ƙone gonaki da na’urorin sadarwar ƙauyen, sun lalata turakun layin sadarwa, wanda hakan ya sa ba a iya kiran waya waya ko hanyoyin sadarwa.

Yawancin mazauna ƙauyen sun tsere zuwa garuruwan Gidan Madi da Sakkwato domin neman ɗauki.

“Ina zama yanzu da ’yan uwana a cikin gari,” in ji wata mata.

“Muna roƙon gwamnati ta kawo mana jami’an tsaro, ta kuma dawo mana da layin sadarwa domin mu riƙa bayar da rahoton ayyukan ’yan bindigar.”

Wasu mazauna yankin na zargin cewa harin yana da nasaba da yadda ƙauyen ke bijirewa yawaitar tasirin ƙungiyar.

Wani jagoran al’umma ya taɓa gargaɗin mutane da kada su yadda ’ya’yansu mata su auri ’yan ƙungiyar, wanda hakan ya fusata su.

Wani jami’in Ƙaramar Hukumar ya tabbatar da mutuwar mutum 15 tare da raunata wasu bakwai.

Rundunar ’Yan Sandan Jihar dai ta ce suna nan suna bincike, amma tuni aka tura jami’an tsaro zuwa yankin domin daƙile karin hari.

Ba wannan ne karon farko da ƙungiyar Lakurawa ke kai hari a yankin ba.

A makon da ya gabata, sun kashe mutum takwas a Sabiyo, kuma sun kai hari ƙauyen Baiji.

Haka kuma sun dasa bam a wani waje da ya kashe aƙalla mutum bakwai a garin Gwabro.

“Wannan ’yan ta’adda suna aiki ba tare da ƙaƙƙautawa ba,” in ji Ghazali Rakah, hadimin Shugaban Ƙaramar Hukumar.

“Sun kusan shiga Sanyinna amma suka janye bayan ganin zuwan sojoji.”

Ƙwarrarren masani kan sha’anin tsaro, Squadron Leader Aminu Bala Sakkwato (mai ritaya), ya buƙaci Gwamnatin Sakkwato da ta horar da matasa domin su taimaka wajen kare ƙauyuka da ke da hatsarin fuskantar hare-haren ’yan ta’adda.

“Rundunar tsaro ta ƙasa na da tarin aiki. Muna buƙatar matasa da aka horas, tare da haɗin gwiwar sojoji domin daƙile barazanar,” in ji shi.

Gwamnatin Jihar Sakkwato ta ce tana aiki kafaɗa da kafaɗa da rundunar soji da ’yan sanda domin inganta tsaro a yankin Tangaza da kewaye.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tsohon golan Super Eagles, Peter Rufai ya mutu
  • Buhari ba ya cikin mawuyacin hali — Bashir Ahmad
  • ’Yan bindiga sun kashe jami’an tsaro 6, sun raunata wasu a Kwara
  • Buhari Ba Shi Da Lafiya, Amma Yana Samun Sauƙi A Birtaniya — Garba Shehu
  • Buhari Ba Shi Da Lafiya, Yana Samun Sauƙi A Birtaniya — Garba Shehu
  • ‘Mutum 600 da suka bace a ambaliyar Mokwa sun mutu’
  • Lakurawa sun kashe mutum 15 a harin ramuwar gayya a Sakkwato
  • Najeriya ta kammala dawo da alhazan da suka yi Aikin Hajjin bana
  • Ba Zan Bar Jam’iyyar PDP Ba – Gwamna Muftwang
  • Rikicin Gonar Gado Ya Yi Ajalin Mutum Ɗaya, An Ƙone Gidaje A Filato